Sashe 77
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Baku sani ba, Bilal bai sani ba amman ina shan kwayoyi, sune na zuba a ruwa har ya samu ya sha, har suka sha da Layla... Laifina ne Ayya... Ina jin laifina ne. Amman idan da gaske sihiri akayi mun, ni wa zan daurawa laifi? Wa zance ya kawo mu inda muke yanzun ko zan samu sauki. Ayya ina zan kai laifin nan?"
Rayyan ya tambaya yana kallon cikin idanuwanta
"Ya zan fara rayuwa a duk rana da sanin nayi sanadin mutuwar Bilal?"
Ya karasa maganar wasu hawaye na cika misji idanuwa. Numfashi me nauyi ya sauke yana sake kallon Ayya da ta sadda kanta kasa, bata son ganin shi, ya kashe mata yaro dole taqi son ganin shi, shima baya son ganin kan shi yanzun nan. Juyawa yayi yana ficewa daga dakin, sai dai baisan inda ya kamata ya nufa ba, bakin kofar dakin su ya tsaya yana tsintar kan shi da kasa shiga. Abu daya zai gani na Bilal abinda yake ji yana gab da ballewa a tare da shi zai balle, tsaye yake yana maida numfashi yana kuma son ganin hawayen da suke cikin idanuwan shi basu zuba ba. Kirjin shi ya dan dafe yana murza inda yake ciwo kamar zai rabe biyu.
"Hamma..."
Yaji muryar Layla da ta saka shi juyawa, kamar tsayuwar wahala take mata shisa ta dafa bango. Ta dade bakin kofa ko zata ga giccin Mami kafin ta samu ta fito, tana jin numfashin da Rayyan din yake fitarwa ta cikin wayar cikin yanayin daya daga mata hankali, gashi tanata magana shiru kafin kiran ya yanke. Zuciyarta ta kasa hakuri, wata irin soyayyar shi ce take dawainiya da ita, tunanin halin da yake ciki, tsantsar ciwon zuciyar da taji a cikin muryar shi ya hade yana sakata kasa hakuri sai ta gan shi, ko na dakika biyune ta leqa taga yana nan dai zata samu sauki. Sai da ta fara takowa taji kamar tana yawo saman iska.
Shikuma kallonta yakeyi, idanuwanta na saka shi jin wani iri, amman ya kasa daina kallon su, saboda a cikin su yake ganin tarin rudani a shimfide, kafin ya samu ya kalli duka fuskarta da har zanen kashin kuncinta ya fito kamar wadda ta dade tana jinya, tayi zuru zuru ta fita hayyacinta. Tana cikin firgicin da yake jin duka shine silar shi
"Layla"
Ya kira da wani yanayi mai wahala
Idanuwanta cike taf da hawaye tana jan numfashin da ta fitar da shi tare da hawayen ta da suka zuba, dayan hannunta ta saka ta share su, tana kallon yanda fuskar shi take cike da gashi, kayan jikin shi sunyi daudar da bata taba ganin shi da ita ba, shi kan shi ya mata wani irin cuku-cuku. Ko takalma babu a kafafuwan shi, Rayyan da ko a daki baya yawo babu takalmi ko safa, Rayyan da ta san zai iya wanka hudu a rana, shine yau a firgice haka. Hannunta ta kai tana dafe cikinta da taji kamar ya kulle, yanayin da ya saka Rayyan bin cikin nata da kallo.
Akwai yaron Bilal a cikin nata, a jikinta yana rayuwa, kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da zaizo ta hanyar da kowa yake gudu saboda shi
"Ki yafe mun Layla"
Yayi maganar yana sadda kan shi kasa, wasu hawayen ne masu zafi suka zubo mata, bata san me yasa yake rokon ta yafe mishi ba. Bayan ita din ya kamata ta roki ya yafe mata. Jin tayi shiru ya saka shi sauke idanuwan shi cikin nata, yana jin yanda bata kyauta mishi ba
"Ban hana ki zama a gidan mu idan bana nan ba? Me yasa kika zauna?"
Kafadu ta dan daga mishi, bata da bakin magana bata da wani bayanin da zatayi mishi
"Baki kyauta mun ba, kin sani ko?"
Da ta taimaka mishi bata zauna ba, da ya gujema abubuwa da yawa. Duk da kukanta na kara mishi zafin da zuciyar shi takeyi. Amman yana bukatar raba laifin da wani. Numfashi ya sauke ya juya da nufin shiga daki
"Hamma..."
Ta kira shi, juyowa Rayyan yayi, kuka yake so yayi har sai inda hawayen shi suka tsaya. Amman bayason yi a gabanta. Baya son kowa ya lallashe shi. Idan ya gama duk zai roke su da su yafe mishi, sai ya kara yawaita addu'o'in shi akan Bilal ko zasu isa wanke girman abinda yayi mishi idan suka tsaya a gaban Allah.
"Idan na kira ka daga, dan Allah kayi mun kowanne hukunci karka rabani da kai, abubuwan da suka rage mun basu da yawa"
Kai kawai ya iya daga mata yana shigewa daki. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyin gaske tana samu ta koma bangaren su tana wucewa daki. Wannan karin waje ta samu ta zauna, kafafuwanta taja ta hade su da kirjinta, sai taji bata iya fitar da numfashi sosai, kamar ta matse cikin nata da yawa, babu shiri ta sauke kafafuwan nata, kafin wani irin tashin hankali ya dirar mata, cikine a jikinta da gaske, da duk ranar da zata wuce da yanda cikin zai cigaba da fitowa. A hankali take jin yanda ba rabuwa da Rayyan bane matsalarta ta farko, yanda zata fara rayuwa da cikin da in ya tako duniya bata da amsar bashi, cikin da Bilal baya nan ballantana ya tayata yi mishi bayani
"Na shiga uku"
Ta furta a hankali tana fashewa da kuka, komai nata ya canza, rayuwarta, makaranta, watakila tabarta kenan har abada, idan haihuwa tayi ta ina zata fara yawo da yaro cikin mutane, me zata ce musu idan sun tambayeta? Ya Mami zata fara shiga dangi, wacce tambaya kowa zai jefe ta da ita? Watakila kowa ya fara tunanin Mami bata riketa da kyau ba, su Abbu basu riketa da kyau ba saboda ita din ba yarsu bace ba. Duk yanzun ne ta samu damar yin wannan tunanin da yake kara daga hankalinta, kasa ta kwanta kan tayal din dakin da sanyin shi ke kara mata zazzabin da ya sake saukar mata, kuka takeyi marar sauti, kukan da bata hango ranar da zata daina shi ba.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 7, 2020
29
Tayi kuka fiye da wanda tayi na rasuwar Bilal, kukan da bata tabayin kalar shi a tsayin zaman duniyarta ba. Saboda akwai banbanci a kuka na rashi, akwai kuma banbanci a kukan sanin cewa kaine da laifi a wannan rashin, kuka ne tayi na dana sani kan abubuwa da dama. Yanda duk zata so raba nata laifin da Dije da kuma Gwaggo da suka dorata akan bin Malamai ta kasa, sosai take so ta boye bayan ko da kuruciya ce dan samun sauki. Amman da hankalin ta lokacin, ko da kuwa da shekaru za ayi amfani wajen auna hakan, balle kuma zaman gidan miji da kuma yawan yara.
Ba abokai nagari da zatayi shawara da su bane ta rasa a lokacin, da ta dora kacokan laifin akan su Hajiya Dije. Tana zagaye da yan uwanta da suke matukar kaunarta. Yan uwan da ta gujewa saboda suna gaya mata gaskiyar da bataji. Sai ta dinga ganin kamar babu kaunar nan da tayi tunanin akwaita a tsakanin su. Da sun fada mata abinda take son ji kamar yanda su Gwaggo suka dingayi. Yanzun ne da hankalinta ya dawo jikinta take tunani kala-kala. Ko da asiri Mami tayi ta aure Abbu ba zai zama dalilin da itama zata ce ta fara shiga Malamai ba, wannan ba uzuri bane ba sam.
Balle da idanuwanta bata shaida hakan ba, Gwaggo ta fara kawo mata wannan tunanin. Kuma ta hau ta zauna saboda yayi dai-dai da abinda take son ji. Akwai tarin son zuciya a abinda tayi. Yanzun tunanin cutar da Haris ko da yaya ne sai da ya sa kanta sarawa saboda tarin kaunar da takeyi mishi. A baya idanuwanta ya rufe da soyayyar da taga Abbu yana nuna mishi, tana manta lokacin tata kuruciyar da girma, da kuma yanda kaf kowa yake maganar kusancin da take da shi da nata baban. Bata kuma duba kalar kusancin da take da shi da Bilal ba, da yanda duka yaranta sukan ce tafi son Bilal akan su.
Tunani ne kala-kala yake mata yawo yanzun. Son zuciya ya kaita ya barota, abinda taso da dan wani sai Allah ya juya shi kan nata yaron, ko ma tace nata yaran. Tana ta takamar tana kula da abinda yake faruwa da su, sai ta kasa fahimtar a baudadden halayya irin na Rayyan akwai tarin abubuwan da yake fuskanta. Balle kuma ta kalli Bilal da kullum take dorawa nauyin kula da Rayyan din. Sai ta maida hankalinta wajen raba abinda kaddara ta rigada ta gama rubutawa, a karo na babu adadi tayi kokarin cutar da Layla. Da yake kaddara na biye da su sai gata da cikin Bilal ta hanyar da Ayya zatayi komai da zata iya dan kaucema faruwar hakan.
Yanzun da take wannan tunanin sai abin ya kara tsoratata, saboda tana jin yanda cikin jikin Layla ne kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da bata damu da hanyar da ya samun ba in dai zai taka duniya ta rike shi a cikin hannuwanta. Har cikin zuciyarta take jin son abinda yake cikin Layla din. A gefe daya kuma tana tunanin da idanuwan da zata kalli Rayyan yanzun. Zata so ta fada mishi da ita ya kamata ya raba laifin da yake jin ya mishi nauyi. Amman hakan ma ba mafita bane a hargitsin da yake ciki. Idan ta gaya mishi zata kara rikita shi, amman tana bukatar yafiyar shi, duk da take mahaifiyar shi wannan hakkine mai girman gaske.
Rayyan ya tambaya yana kallon cikin idanuwanta
"Ya zan fara rayuwa a duk rana da sanin nayi sanadin mutuwar Bilal?"
Ya karasa maganar wasu hawaye na cika misji idanuwa. Numfashi me nauyi ya sauke yana sake kallon Ayya da ta sadda kanta kasa, bata son ganin shi, ya kashe mata yaro dole taqi son ganin shi, shima baya son ganin kan shi yanzun nan. Juyawa yayi yana ficewa daga dakin, sai dai baisan inda ya kamata ya nufa ba, bakin kofar dakin su ya tsaya yana tsintar kan shi da kasa shiga. Abu daya zai gani na Bilal abinda yake ji yana gab da ballewa a tare da shi zai balle, tsaye yake yana maida numfashi yana kuma son ganin hawayen da suke cikin idanuwan shi basu zuba ba. Kirjin shi ya dan dafe yana murza inda yake ciwo kamar zai rabe biyu.
"Hamma..."
Yaji muryar Layla da ta saka shi juyawa, kamar tsayuwar wahala take mata shisa ta dafa bango. Ta dade bakin kofa ko zata ga giccin Mami kafin ta samu ta fito, tana jin numfashin da Rayyan din yake fitarwa ta cikin wayar cikin yanayin daya daga mata hankali, gashi tanata magana shiru kafin kiran ya yanke. Zuciyarta ta kasa hakuri, wata irin soyayyar shi ce take dawainiya da ita, tunanin halin da yake ciki, tsantsar ciwon zuciyar da taji a cikin muryar shi ya hade yana sakata kasa hakuri sai ta gan shi, ko na dakika biyune ta leqa taga yana nan dai zata samu sauki. Sai da ta fara takowa taji kamar tana yawo saman iska.
Shikuma kallonta yakeyi, idanuwanta na saka shi jin wani iri, amman ya kasa daina kallon su, saboda a cikin su yake ganin tarin rudani a shimfide, kafin ya samu ya kalli duka fuskarta da har zanen kashin kuncinta ya fito kamar wadda ta dade tana jinya, tayi zuru zuru ta fita hayyacinta. Tana cikin firgicin da yake jin duka shine silar shi
"Layla"
Ya kira da wani yanayi mai wahala
Idanuwanta cike taf da hawaye tana jan numfashin da ta fitar da shi tare da hawayen ta da suka zuba, dayan hannunta ta saka ta share su, tana kallon yanda fuskar shi take cike da gashi, kayan jikin shi sunyi daudar da bata taba ganin shi da ita ba, shi kan shi ya mata wani irin cuku-cuku. Ko takalma babu a kafafuwan shi, Rayyan da ko a daki baya yawo babu takalmi ko safa, Rayyan da ta san zai iya wanka hudu a rana, shine yau a firgice haka. Hannunta ta kai tana dafe cikinta da taji kamar ya kulle, yanayin da ya saka Rayyan bin cikin nata da kallo.
Akwai yaron Bilal a cikin nata, a jikinta yana rayuwa, kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da zaizo ta hanyar da kowa yake gudu saboda shi
"Ki yafe mun Layla"
Yayi maganar yana sadda kan shi kasa, wasu hawayen ne masu zafi suka zubo mata, bata san me yasa yake rokon ta yafe mishi ba. Bayan ita din ya kamata ta roki ya yafe mata. Jin tayi shiru ya saka shi sauke idanuwan shi cikin nata, yana jin yanda bata kyauta mishi ba
"Ban hana ki zama a gidan mu idan bana nan ba? Me yasa kika zauna?"
Kafadu ta dan daga mishi, bata da bakin magana bata da wani bayanin da zatayi mishi
"Baki kyauta mun ba, kin sani ko?"
Da ta taimaka mishi bata zauna ba, da ya gujema abubuwa da yawa. Duk da kukanta na kara mishi zafin da zuciyar shi takeyi. Amman yana bukatar raba laifin da wani. Numfashi ya sauke ya juya da nufin shiga daki
"Hamma..."
Ta kira shi, juyowa Rayyan yayi, kuka yake so yayi har sai inda hawayen shi suka tsaya. Amman bayason yi a gabanta. Baya son kowa ya lallashe shi. Idan ya gama duk zai roke su da su yafe mishi, sai ya kara yawaita addu'o'in shi akan Bilal ko zasu isa wanke girman abinda yayi mishi idan suka tsaya a gaban Allah.
"Idan na kira ka daga, dan Allah kayi mun kowanne hukunci karka rabani da kai, abubuwan da suka rage mun basu da yawa"
Kai kawai ya iya daga mata yana shigewa daki. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyin gaske tana samu ta koma bangaren su tana wucewa daki. Wannan karin waje ta samu ta zauna, kafafuwanta taja ta hade su da kirjinta, sai taji bata iya fitar da numfashi sosai, kamar ta matse cikin nata da yawa, babu shiri ta sauke kafafuwan nata, kafin wani irin tashin hankali ya dirar mata, cikine a jikinta da gaske, da duk ranar da zata wuce da yanda cikin zai cigaba da fitowa. A hankali take jin yanda ba rabuwa da Rayyan bane matsalarta ta farko, yanda zata fara rayuwa da cikin da in ya tako duniya bata da amsar bashi, cikin da Bilal baya nan ballantana ya tayata yi mishi bayani
"Na shiga uku"
Ta furta a hankali tana fashewa da kuka, komai nata ya canza, rayuwarta, makaranta, watakila tabarta kenan har abada, idan haihuwa tayi ta ina zata fara yawo da yaro cikin mutane, me zata ce musu idan sun tambayeta? Ya Mami zata fara shiga dangi, wacce tambaya kowa zai jefe ta da ita? Watakila kowa ya fara tunanin Mami bata riketa da kyau ba, su Abbu basu riketa da kyau ba saboda ita din ba yarsu bace ba. Duk yanzun ne ta samu damar yin wannan tunanin da yake kara daga hankalinta, kasa ta kwanta kan tayal din dakin da sanyin shi ke kara mata zazzabin da ya sake saukar mata, kuka takeyi marar sauti, kukan da bata hango ranar da zata daina shi ba.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:09 PM - 111: Jan 7, 2020
29
Tayi kuka fiye da wanda tayi na rasuwar Bilal, kukan da bata tabayin kalar shi a tsayin zaman duniyarta ba. Saboda akwai banbanci a kuka na rashi, akwai kuma banbanci a kukan sanin cewa kaine da laifi a wannan rashin, kuka ne tayi na dana sani kan abubuwa da dama. Yanda duk zata so raba nata laifin da Dije da kuma Gwaggo da suka dorata akan bin Malamai ta kasa, sosai take so ta boye bayan ko da kuruciya ce dan samun sauki. Amman da hankalin ta lokacin, ko da kuwa da shekaru za ayi amfani wajen auna hakan, balle kuma zaman gidan miji da kuma yawan yara.
Ba abokai nagari da zatayi shawara da su bane ta rasa a lokacin, da ta dora kacokan laifin akan su Hajiya Dije. Tana zagaye da yan uwanta da suke matukar kaunarta. Yan uwan da ta gujewa saboda suna gaya mata gaskiyar da bataji. Sai ta dinga ganin kamar babu kaunar nan da tayi tunanin akwaita a tsakanin su. Da sun fada mata abinda take son ji kamar yanda su Gwaggo suka dingayi. Yanzun ne da hankalinta ya dawo jikinta take tunani kala-kala. Ko da asiri Mami tayi ta aure Abbu ba zai zama dalilin da itama zata ce ta fara shiga Malamai ba, wannan ba uzuri bane ba sam.
Balle da idanuwanta bata shaida hakan ba, Gwaggo ta fara kawo mata wannan tunanin. Kuma ta hau ta zauna saboda yayi dai-dai da abinda take son ji. Akwai tarin son zuciya a abinda tayi. Yanzun tunanin cutar da Haris ko da yaya ne sai da ya sa kanta sarawa saboda tarin kaunar da takeyi mishi. A baya idanuwanta ya rufe da soyayyar da taga Abbu yana nuna mishi, tana manta lokacin tata kuruciyar da girma, da kuma yanda kaf kowa yake maganar kusancin da take da shi da nata baban. Bata kuma duba kalar kusancin da take da shi da Bilal ba, da yanda duka yaranta sukan ce tafi son Bilal akan su.
Tunani ne kala-kala yake mata yawo yanzun. Son zuciya ya kaita ya barota, abinda taso da dan wani sai Allah ya juya shi kan nata yaron, ko ma tace nata yaran. Tana ta takamar tana kula da abinda yake faruwa da su, sai ta kasa fahimtar a baudadden halayya irin na Rayyan akwai tarin abubuwan da yake fuskanta. Balle kuma ta kalli Bilal da kullum take dorawa nauyin kula da Rayyan din. Sai ta maida hankalinta wajen raba abinda kaddara ta rigada ta gama rubutawa, a karo na babu adadi tayi kokarin cutar da Layla. Da yake kaddara na biye da su sai gata da cikin Bilal ta hanyar da Ayya zatayi komai da zata iya dan kaucema faruwar hakan.
Yanzun da take wannan tunanin sai abin ya kara tsoratata, saboda tana jin yanda cikin jikin Layla ne kwai daya da Bilal yake da rabon samu a duniya. Kwan da bata damu da hanyar da ya samun ba in dai zai taka duniya ta rike shi a cikin hannuwanta. Har cikin zuciyarta take jin son abinda yake cikin Layla din. A gefe daya kuma tana tunanin da idanuwan da zata kalli Rayyan yanzun. Zata so ta fada mishi da ita ya kamata ya raba laifin da yake jin ya mishi nauyi. Amman hakan ma ba mafita bane a hargitsin da yake ciki. Idan ta gaya mishi zata kara rikita shi, amman tana bukatar yafiyar shi, duk da take mahaifiyar shi wannan hakkine mai girman gaske.