Sashe 11
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Labarin soyayya kala biyu zai bayar da kan shi a dage, muryar shi dauke da alfahari, shine soyayyar mahaifiyar shi, sai kuma soyayyar da Maimuna take yi mishi, shisa ya fahimci kishinta, tana mishi son da yake da yakinin yanzun a fadin duniyar shi baida na biyun sa. Amman a lokaci irin wannan yana rasa me yake lullube kwakwalwarta haka, me yasa soyayyar shi bata sakata zaben kalaman da zata furta mishi, kishin shi yasa ta daina gudun bacin ran shi sam.
"Ina manta cewa Bilal ba daga jikin mu ya fito ba wallahi, ki daina maganar nan dan Allah..."
Ahmadi ya fara cikin taushin murya, amman kai Maimuna take girgiza mishi, tun jiya da safe da ta fita tsakar gida taga Layla sai da gabanta yai wata irin mummunar faduwa, babu shiri ta koma daki tana karanta duk wata addu'a da zata zo bakinta, gashi yarinyar bata da haske can da zatayi zaton ko daga kasar turawa ta fado musu cikin gida. Babu kalar tunanin da batayi ba a ranta kan yarinyar, ko da Ahmadi ya dawo ta tambaye shi saiya fada mata ko wacece Laylar.
Bata manta lokacin da akaita surutun auren Deeni da Mannira a dangi ba, har Gwaggo bare na fadin
"Mugun abinsu ne ya fara koma musu, shisa yaje ya kwaso mayya... Watakila ta lashe mana kurwar Karime duk mu huta"
A lokacin abin dariya yayita bata, sanda labarin mutuwar Mannira ta riske su zatai karya idan bataji wani iri a ranta ba, duk surutun da ta dinga sha, ashe ma bata da rabon zama mai nisa a gidan auren, fatan samun Rahma tayi mata. Ta dauka tunda tayiwa Maryama gaisuwa a wancen lokacin ba zata sake jin ko da labarin Mannira bane ba. Sai ga yarta a cikin gidan ta, yar Mannira mai idanuwan aljanu, yarinyar da tun jiya ta kasa samun sukuni a cikin nata gidan saboda su Haris sun shigo mata da ita bangarenta.
Har ranta ta dauka ko Maryama tazo da itane ta kwana biyu ta mayar da ita, sai yanzun da Ahmadi yazo mata da wani bayani da babu abinda ta fahimta a cikin shi sai cewar Layla din zata zauna ne a cikin gidan.
"Ni dai ba zan zauna a gida daya da ita ba, sai kasan yanda zakayi da mu... Haka kawai muna zaman lafiya zata zo ta lashe mun yara"
Rai a bace Ahmadi yake kallon ta
"Wani lokaci sai ki dinga magana kamar baki da ilimi. Kina manta babu wani abu maita a addini ne, sai kambun baka... Kuma ita kadai kika fara gani da kalar idanuwa haka? Ko bakiga wanda aka haifa babu idanuwan bane gabaki daya? Kinsan karki fara mun fitinar da bata da karshe, na fada miki Layla zata zauna ne saboda girmamawa, ba wai shawararki nake nema akan hakan ba"
Wannan karon itace take kallon shi, yanda ya rufe ido yana datsa mata maganganu har yana kiranta da jahila a fakaice saboda wannan dangin mayun
"Ni kake kira da jahila? Ahmadi ni kake cewa jahila akan nace ba zan zauna gida daya da mayya ba?"
Numfashi ya sauke
"Kinga irin abin ko? Ni ban kiraki jahila ba, ki daina ce ma yarinyar mutane mayya tunda idan wani ya kira naki yaran da wannan kalmar ba zakiji dadi ba..."
Ido cikin ido take kallon shi
"Akan me za'a kira nawa yaran da mayu tunda basu hada hanya da maita ba? Ni dai na fada maka ba zan zauna gida daya da ita ba, ko ka kwashe ta da Maryaman kasan inda zaka kaisu, ko kuma ni kasan inda zaka kaini"
Murmushin takaici Ahmadi yayi yana binta da ido
"Kiyi duk abinda kike so, Layla kam zataci gaba da zama a gidan nan, in ba aure ko mutuwa ya rabata da shi ba..."
Idanuwan Maimuna cike taf da hawaye take kallon shi, tana son tabbatar da cewa da gaske yakeyi wannan yarinyar da tun jiya take firgitata zai bar mata cikin gida
"Ahmadi da gaske nakeyi ba zan zauna da ita ba. Dan Allah to ka raba mana gida"
Ta karasa hawaye na zubo mata
"Ke kinsan ko ina da hali ba zan raba muku gida ba saboda banason zumuncin yarana ya samu tangarda, balle kuma bani da wannan halin..."
Mikewa Maimuna tayi, hawaye takeyi sosai, ta kowacce fuska Maryama ta zame mata bala'i.
"Ni kam zan bar muku gidan, sai ku zauna. A banza ba za'a zo a lashe mun kurwa ba wallahi"
Gyara zaman shi Ahmadi yayi baice mata komai ba, rigima take nema sosai. Ya rigada ya gama magana, ba zai biye mata ba. Kamar yanda yace Layla kama zama daram a cikin gidan. In tayi rikicin ta gama taga da gaske yakeyi zata hakura. Yana nan zaune yaga ta fito da jaka ta saka mayafi
"Ina zakije?"
Sai da ta share kwallar da ta zubo mata sannan tace mishi
"Gidan mu"
Yasan ba lokacin da ya kamata yayi dariya bane, amman dariyar ce ta kubce mishi, da kuruciyar su ma, duk fadan da takeyi dashi batace zatayi yaji ba sai yanzun da girma yazo musu, dariya yakeyi sosai da ta kara sosa ranta, wato bai damu ba, bai kuma dauki abinda takeyi din da wani girma ba
"Tunda kaga mahaukaciya dole kayi dariya Ahmadi..."
Ta karasa maganar cikin kuka tana daukar yar jakar da ita kanta batasan me da me ta zuba a ciki ba. Tasan idan akace ta bar gidan Ahmadi da sunan yaji ba zata iya ba, tunda ta aure shi, rasuwar Audu ne tayi kwanaki har bakwai batare da shi ba, kuma ko a cikin jimami na rashi, kewar shi na nukurkusarta. Yanzun ma tayi ne kawai dan ta razana shi, ganin kukan da takeyi yasa Ahmadi tashi, amman har lokacin murmushine a fuskar shi, jakar yake kokarin kwacewa ta janye, ya kama hannunta duk kokarin kwacewa da takeyi ya karbi jakar, da kanshi ya kama mayafinta yana cirewa
"Ke yanzun da girman ki sai kiyi yaji? Kuma ina zakije ki barni? Ko bakisan Maimuna ce jigon rayuwar Ahmadi bane?"
Wasu hawayen ne suka kara zubo mata, tana tsinewa ranar da Maryama ta dora idanuwanta akan Ahmadi har taji ya kwanta mata, tasata raba wannan soyayyar tashi da ita, shisa bata ga ranar da zata wayi gari da son matar nan ko kankani a zuciyarta ba.
"Ni ba zan zauna da yarinyar nan a gida daya ba, ba zan zauna ba. Kabarni in tafi tunda su ka zaba a kaina. Ka nuna mun yanda banda wani muhimmanci a wajen ka"
Kamata yayi suka zauna, kalaman da yasan da wahala taki yin laushi yake amfani dasu wajen tausarta, tasan yasan cewa shi dinne rauninta, soyayyar shi ita ce rauninta
"Idan ta lashe mun yara fa?"
Tayi maganar da wani irin sanyi murya dan gabaki daya ya gama kashe mata jiki
"Ba zatayi ba, ki yarda dani mana...alfarma nake roko a wajenki Maimuna, ko saina tsugunna..."
Ahmadi ya karasa maganar yana kokarin sauka daga kujerar, da sauri ta riko hannun shi tana girgiza mishi kai, murmushi yayi mata
"Nagode... Dan Allah karki takali Maryama da maganar nan, alfarma dana roka ta hada da wannan, wallahi badan Bilal ta kawo Layla ba, itama da nata dalilin kamar yanda kike da shi"
Taji shi, amman ita tasan gasa Maeyama takeyi da ita, tunda ta kawo Bilal gidan take bakin ciki, shine sai da itama ta nemo wannan mayyar ta kawo, kowa na da yara da kuma dan riko kenan a cikin gidan.
"Kinga daman bata da mace ko..."
Ahmadi ya fara, wani irin kallo da Maimuna ta watsa mishi yana saka shi yin dariya yana daga hannuwan shi ya hadesu waje daya cikin sigar ban hakuri
"Ka tashi ka tafi wajenta idan kewarta ce tasa kake son yimun hirarta a daki..."
Maimuna ta fadi wani irin kishi na taso mata, tashin yayi niyya tunda daman ya jimane haka saboda yana so ya fada mata zancen Layla. Amman maganar da tayi tasa shi yanke hukunci kara zama, yasan ana gab da kiran isha'i, sai yayi amfani da wannan damar ya fice gabaki daya. Maimunar tashi ta zama a lallaba, rikicinta sai shi.
*
Ba ko yaushe yake zama gidan Yaya Ayuba ba, ko da kuwa duka yaran gidan suna can. Lokutta da dama dawowa yake yai kwanciyar shi a daki, yasan ko Ayya tana tunanin yana can wani lokacin. Haka yakan haramtawa Bilal zaman ko da yana so, shi dai da bakin shi baya ce mishi ya taso su taho tare, idan ya taso din kuma baya hana shi biyo shi. Yau baima kula da ya dawo gida ba, zane yake sonyi, haka kawai tunda ya fara rike fensiri, tun ma kafin Abbu ya saka su makaranta zaiyi zane akan duk wani abu da zai samu. Ganin ko gawayi ya tsinto yana musu zane a jikin bango yasa Abbu din kwaso mishi litattafan da zai dingayi a kai.
Yanzun ma gara yayi zanen shi, ko fada sukeyi idan aka rabasu akan takardun zanen shi yake huce haushin shi har sai yaji zuciyar shi tayi sanyi. Ba kasafai yake ganin kyawun abinda yake zanawa din da baya wuce mutane, dabbobi, kwari, ko duk wani abu da yake so ya zana din, amman sai ayita cewa yayi kyau
"Allah yayi riko da hannayenka Rayyan, watakila kai kuma abincin ka a zane yake"
Abbu ya fadi kwanakin baya, baigane asalin ma'anar kalaman ba, ya dai amsa da Amin ne kawai. Ya fara zanen yaji yunwa na naniqar shi, sai ya tuna fada yayi a makaranta bayan sun tashi, daya dawo baibi takan abinci ba. Tashi yayi ya fita daga dakin yana nufar kitchen, yasan inda Ayya take ajiye musu abincin su shida Bilal, nashi ya dauko da cokali, yana dawowa dakin ya samu Layla a ciki, hannunta rike da fensirin zanen shi, dayan rike da takardar da yai kwana biyu yana aiki a kanta, a karo na farko da yaso gwada zana wani a cikin gidan, ya kuma zabi daya fara da Bilal, ta dakuna takardar, tana kuma kokarin kara bi da fensirin a kai.
"Ina manta cewa Bilal ba daga jikin mu ya fito ba wallahi, ki daina maganar nan dan Allah..."
Ahmadi ya fara cikin taushin murya, amman kai Maimuna take girgiza mishi, tun jiya da safe da ta fita tsakar gida taga Layla sai da gabanta yai wata irin mummunar faduwa, babu shiri ta koma daki tana karanta duk wata addu'a da zata zo bakinta, gashi yarinyar bata da haske can da zatayi zaton ko daga kasar turawa ta fado musu cikin gida. Babu kalar tunanin da batayi ba a ranta kan yarinyar, ko da Ahmadi ya dawo ta tambaye shi saiya fada mata ko wacece Laylar.
Bata manta lokacin da akaita surutun auren Deeni da Mannira a dangi ba, har Gwaggo bare na fadin
"Mugun abinsu ne ya fara koma musu, shisa yaje ya kwaso mayya... Watakila ta lashe mana kurwar Karime duk mu huta"
A lokacin abin dariya yayita bata, sanda labarin mutuwar Mannira ta riske su zatai karya idan bataji wani iri a ranta ba, duk surutun da ta dinga sha, ashe ma bata da rabon zama mai nisa a gidan auren, fatan samun Rahma tayi mata. Ta dauka tunda tayiwa Maryama gaisuwa a wancen lokacin ba zata sake jin ko da labarin Mannira bane ba. Sai ga yarta a cikin gidan ta, yar Mannira mai idanuwan aljanu, yarinyar da tun jiya ta kasa samun sukuni a cikin nata gidan saboda su Haris sun shigo mata da ita bangarenta.
Har ranta ta dauka ko Maryama tazo da itane ta kwana biyu ta mayar da ita, sai yanzun da Ahmadi yazo mata da wani bayani da babu abinda ta fahimta a cikin shi sai cewar Layla din zata zauna ne a cikin gidan.
"Ni dai ba zan zauna a gida daya da ita ba, sai kasan yanda zakayi da mu... Haka kawai muna zaman lafiya zata zo ta lashe mun yara"
Rai a bace Ahmadi yake kallon ta
"Wani lokaci sai ki dinga magana kamar baki da ilimi. Kina manta babu wani abu maita a addini ne, sai kambun baka... Kuma ita kadai kika fara gani da kalar idanuwa haka? Ko bakiga wanda aka haifa babu idanuwan bane gabaki daya? Kinsan karki fara mun fitinar da bata da karshe, na fada miki Layla zata zauna ne saboda girmamawa, ba wai shawararki nake nema akan hakan ba"
Wannan karon itace take kallon shi, yanda ya rufe ido yana datsa mata maganganu har yana kiranta da jahila a fakaice saboda wannan dangin mayun
"Ni kake kira da jahila? Ahmadi ni kake cewa jahila akan nace ba zan zauna gida daya da mayya ba?"
Numfashi ya sauke
"Kinga irin abin ko? Ni ban kiraki jahila ba, ki daina ce ma yarinyar mutane mayya tunda idan wani ya kira naki yaran da wannan kalmar ba zakiji dadi ba..."
Ido cikin ido take kallon shi
"Akan me za'a kira nawa yaran da mayu tunda basu hada hanya da maita ba? Ni dai na fada maka ba zan zauna gida daya da ita ba, ko ka kwashe ta da Maryaman kasan inda zaka kaisu, ko kuma ni kasan inda zaka kaini"
Murmushin takaici Ahmadi yayi yana binta da ido
"Kiyi duk abinda kike so, Layla kam zataci gaba da zama a gidan nan, in ba aure ko mutuwa ya rabata da shi ba..."
Idanuwan Maimuna cike taf da hawaye take kallon shi, tana son tabbatar da cewa da gaske yakeyi wannan yarinyar da tun jiya take firgitata zai bar mata cikin gida
"Ahmadi da gaske nakeyi ba zan zauna da ita ba. Dan Allah to ka raba mana gida"
Ta karasa hawaye na zubo mata
"Ke kinsan ko ina da hali ba zan raba muku gida ba saboda banason zumuncin yarana ya samu tangarda, balle kuma bani da wannan halin..."
Mikewa Maimuna tayi, hawaye takeyi sosai, ta kowacce fuska Maryama ta zame mata bala'i.
"Ni kam zan bar muku gidan, sai ku zauna. A banza ba za'a zo a lashe mun kurwa ba wallahi"
Gyara zaman shi Ahmadi yayi baice mata komai ba, rigima take nema sosai. Ya rigada ya gama magana, ba zai biye mata ba. Kamar yanda yace Layla kama zama daram a cikin gidan. In tayi rikicin ta gama taga da gaske yakeyi zata hakura. Yana nan zaune yaga ta fito da jaka ta saka mayafi
"Ina zakije?"
Sai da ta share kwallar da ta zubo mata sannan tace mishi
"Gidan mu"
Yasan ba lokacin da ya kamata yayi dariya bane, amman dariyar ce ta kubce mishi, da kuruciyar su ma, duk fadan da takeyi dashi batace zatayi yaji ba sai yanzun da girma yazo musu, dariya yakeyi sosai da ta kara sosa ranta, wato bai damu ba, bai kuma dauki abinda takeyi din da wani girma ba
"Tunda kaga mahaukaciya dole kayi dariya Ahmadi..."
Ta karasa maganar cikin kuka tana daukar yar jakar da ita kanta batasan me da me ta zuba a ciki ba. Tasan idan akace ta bar gidan Ahmadi da sunan yaji ba zata iya ba, tunda ta aure shi, rasuwar Audu ne tayi kwanaki har bakwai batare da shi ba, kuma ko a cikin jimami na rashi, kewar shi na nukurkusarta. Yanzun ma tayi ne kawai dan ta razana shi, ganin kukan da takeyi yasa Ahmadi tashi, amman har lokacin murmushine a fuskar shi, jakar yake kokarin kwacewa ta janye, ya kama hannunta duk kokarin kwacewa da takeyi ya karbi jakar, da kanshi ya kama mayafinta yana cirewa
"Ke yanzun da girman ki sai kiyi yaji? Kuma ina zakije ki barni? Ko bakisan Maimuna ce jigon rayuwar Ahmadi bane?"
Wasu hawayen ne suka kara zubo mata, tana tsinewa ranar da Maryama ta dora idanuwanta akan Ahmadi har taji ya kwanta mata, tasata raba wannan soyayyar tashi da ita, shisa bata ga ranar da zata wayi gari da son matar nan ko kankani a zuciyarta ba.
"Ni ba zan zauna da yarinyar nan a gida daya ba, ba zan zauna ba. Kabarni in tafi tunda su ka zaba a kaina. Ka nuna mun yanda banda wani muhimmanci a wajen ka"
Kamata yayi suka zauna, kalaman da yasan da wahala taki yin laushi yake amfani dasu wajen tausarta, tasan yasan cewa shi dinne rauninta, soyayyar shi ita ce rauninta
"Idan ta lashe mun yara fa?"
Tayi maganar da wani irin sanyi murya dan gabaki daya ya gama kashe mata jiki
"Ba zatayi ba, ki yarda dani mana...alfarma nake roko a wajenki Maimuna, ko saina tsugunna..."
Ahmadi ya karasa maganar yana kokarin sauka daga kujerar, da sauri ta riko hannun shi tana girgiza mishi kai, murmushi yayi mata
"Nagode... Dan Allah karki takali Maryama da maganar nan, alfarma dana roka ta hada da wannan, wallahi badan Bilal ta kawo Layla ba, itama da nata dalilin kamar yanda kike da shi"
Taji shi, amman ita tasan gasa Maeyama takeyi da ita, tunda ta kawo Bilal gidan take bakin ciki, shine sai da itama ta nemo wannan mayyar ta kawo, kowa na da yara da kuma dan riko kenan a cikin gidan.
"Kinga daman bata da mace ko..."
Ahmadi ya fara, wani irin kallo da Maimuna ta watsa mishi yana saka shi yin dariya yana daga hannuwan shi ya hadesu waje daya cikin sigar ban hakuri
"Ka tashi ka tafi wajenta idan kewarta ce tasa kake son yimun hirarta a daki..."
Maimuna ta fadi wani irin kishi na taso mata, tashin yayi niyya tunda daman ya jimane haka saboda yana so ya fada mata zancen Layla. Amman maganar da tayi tasa shi yanke hukunci kara zama, yasan ana gab da kiran isha'i, sai yayi amfani da wannan damar ya fice gabaki daya. Maimunar tashi ta zama a lallaba, rikicinta sai shi.
*
Ba ko yaushe yake zama gidan Yaya Ayuba ba, ko da kuwa duka yaran gidan suna can. Lokutta da dama dawowa yake yai kwanciyar shi a daki, yasan ko Ayya tana tunanin yana can wani lokacin. Haka yakan haramtawa Bilal zaman ko da yana so, shi dai da bakin shi baya ce mishi ya taso su taho tare, idan ya taso din kuma baya hana shi biyo shi. Yau baima kula da ya dawo gida ba, zane yake sonyi, haka kawai tunda ya fara rike fensiri, tun ma kafin Abbu ya saka su makaranta zaiyi zane akan duk wani abu da zai samu. Ganin ko gawayi ya tsinto yana musu zane a jikin bango yasa Abbu din kwaso mishi litattafan da zai dingayi a kai.
Yanzun ma gara yayi zanen shi, ko fada sukeyi idan aka rabasu akan takardun zanen shi yake huce haushin shi har sai yaji zuciyar shi tayi sanyi. Ba kasafai yake ganin kyawun abinda yake zanawa din da baya wuce mutane, dabbobi, kwari, ko duk wani abu da yake so ya zana din, amman sai ayita cewa yayi kyau
"Allah yayi riko da hannayenka Rayyan, watakila kai kuma abincin ka a zane yake"
Abbu ya fadi kwanakin baya, baigane asalin ma'anar kalaman ba, ya dai amsa da Amin ne kawai. Ya fara zanen yaji yunwa na naniqar shi, sai ya tuna fada yayi a makaranta bayan sun tashi, daya dawo baibi takan abinci ba. Tashi yayi ya fita daga dakin yana nufar kitchen, yasan inda Ayya take ajiye musu abincin su shida Bilal, nashi ya dauko da cokali, yana dawowa dakin ya samu Layla a ciki, hannunta rike da fensirin zanen shi, dayan rike da takardar da yai kwana biyu yana aiki a kanta, a karo na farko da yaso gwada zana wani a cikin gidan, ya kuma zabi daya fara da Bilal, ta dakuna takardar, tana kuma kokarin kara bi da fensirin a kai.