Sashe 34
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwance Bilal yake yana nazarin wani lissafi, saboda har an fara test tun satin daya gabata, jarabawa nata karatowa. Amman Rayyan zaune yake yana zane, wani lokacin zaka rantse da Allah hutu Rayyan yake zuwa yi Zaria ba karatu ba, saima lokacin jarabawa, idan baka gan shi yana zane ba, to zaka iya ganin shi yana kwance shiru, tunda shi dai baya hada hanya da wata kafar sada zumunta, har dan whatsapp din da akeyi ma bayayi. Asalima wayar shi da screen din ya fashe yar karamar Nokia ya siya ya saka sim din shi a ciki.
Idan wani abu na makaranta ne daya kama sai an duba yanar gizo, da kwamfuta din shi kirar laptop yakanyi amfani. Kuma yana daya daga cikin mutane hudun da suke jagorantar ajin su ta fannin karatu, inda Rayyan dinne na biyu, idan da zai maida hankali ma tsaf zai zama gwarzo a ajin.
"Wai ba test kace kuna da shi ba?"
Bilal ya bukata, kai Rayyan ya jinjina mishi
"Ba zakayi karatu ba?"
Raba idanuwan shi da takarda Rayyan yayi ya kalli Bilal din, kallon da yake fassara "Da ni kake?". Kafin ya mayar da hankalin shi kan zanen da yakeyi
"Lokutta irin haka kana sakani inajin kamar bani da kokari"
Dan numfashi Rayyan ya fitar
"Kana da kokarin ne? Tun dazun kake kallon takarda daya"
Bude baki Bilal yayi, kafin ya mike zaune
"Kasan wanne lissafine? Kake kira takarda daya kamar wani abu marar wahala"
Fensirin hannun shi Rayyan ya ajiye, ya dan juya zaman shi yana mika hannu ya fisge takardar da take hannun Bilal, duba tambayar yayi, batare daya dago ba yace
"Ina misalin? Wanda akayi?"
Tashi Bilal yayi ya dauko jakar shi yana fito da littafi ya dubo wani misalin yana mikawa Rayyan daya karba, sosai ya nutsar da hankalin shi yana ganin yanda aka fitar da abin. Kafin ya fara duba wanda Bilal yake nazari, a idanuwan shi yaga yanda komai zai kasance, juyawa yayi ya ajiye akan tebir, cikin mintina kasa da sha biyar ya gama fitar da shi yana jefawa Bilal din
"Ba zaka maida hankali sanda ake maka abu a aji ba, kana can kana wasu tunane-tunane..."
Rayyan din ya fadi a fadace, dauka Bilal yayi yana duddubawa, murmushi yayi
"Bayani zakayi mun dalla-dalla..."
Hararar shi Rayyan yayi yana sake hade fuska, dariya Bilal yayi mai sauti wannan karin yana tashi ya janyo kujera ya zauna gefen Rayyan din daya ke watsa mishi wani kallo
"Ni kyaleni"
Ya fadi saboda surutu Bilal zai sa shi yayi, watakila sai yayi mishi bayani sau biyu ko fiye da haka, amman sai ya zaqulo wata tambayar yayi mishi. Haka kuwa akayi, har saida ya kule daya fahimci Bilal din ya gane, surutun kawai yake so ya saka shi. Ganin yayi Rayyan din yayi banza ya kyale shi yasa Bilal komawa kan gado abin shi, so yake ya sake fitar da lissafin a wata takarda daban dan yaga koya fahimta, shekarar shi ta farko ya fadi jarabawa guda daya. Rayyan yaita mishi fada kamar zai mare shi, wani lokacin ko bai niyyar karatu ba yakan dauko yayi saboda masifar Rayyan da ba karewa takeyi ba.
Ranar ne karo na farko da yaji kamar yayi dissapointing din Rayyan din, yanayine da baya so ya kara faruwa. Duk da kwakwalwar su ta bambanta, yana iya kokarin shi. Rayyan zanen shi yaci gaba dayi, amman baya tafiya yanda yake so, saboda yau ya kasa rufe gabaki daya tunanin shi kamar yanda yakanyi a lokutta irin haka. Layla ce manne a ran shi, tun jiya bai ganta ba, har wayarta ya kira amman a kashe. Yanzun ma wayar da take ajiye kan tebir ya dauka ya duba ko ta turo mishi sako, amman shiru, sake gwada kiranta yayi yana jin bata shiga ba, kamar matsalar network tunda ba'a ce mishi a kashe take ba
Wajen mintina sha biyar tsakani, batare daya kalli Bilal ba yace
"Ka ga Layla?"
Kai Bilal din ya jinjina mishi, kullum sai yaga Layla, in ya fita kafin ya wuce aji saiya biya ya kirata ta sauko yaga ya ta kwana, ko tana da wata matsala sannan ya wuce, amanar ta Abbu ya bashi, babu yanda za'ayi ba zai dubata a duk rana ba.
"Ni ban ganta ba"
Cewar Rayyan da wani yanayi a muryar shi da yasa Bilal dagowa
"Ba tazo aji ba, bata jin dadine tun jiya da dare"
Mikewa tsaye Rayyan yayi zuciyar shi na wata irin dokawa
"Me yasa baka fada mun ba?"
Kallon shi Bilal yayi yanda ya hargitse lokaci daya kamar yace mishi wani babban abune ya samu Layla, shi yasan lokacin al'adarta ne, badan ta gaya mishi ba, sai dan ya kula da duk wata haka take fama. Wancen watan da ciwon da komai ta zo wajen Rayyan, yana ganin yanda har fuskarta Rayyan din ya taba ko zaiji zazzabi bayan ya tambayeta me ya sameta tace mishi bakomai. Bai fada mishi ba saboda yasan idan akan Layla ne Rayyan zai dauki abin ya saka a ran shi. Amman can kasan zuciyar shi yana jin kamar akwai wani dalili bayan nan, dalilin da bayaso yasan shi saboda yana da yakinin zai saka shi yaji kamar bai kyauta ba.
Jacket din shi da take can gefen gado Rayyan ya dauka yana sakawa akan kayan jikin shi da riga da wando ne, ya dauki wayar shi yana kama hanyar kofa
"Ina zaka je? Takwas da rabi fa"
Ko amsa bai samu ba, numfashi kawai ya iya saukewa yana bin Rayyan din da kallo harya fice daga dakin. Wani irin sauri yake ya karasa titi ya samu machine zuwa gate din makaranta, kawai so yake ya fara hango hostel din su Layla, bai daina gwada kiran lambarta ba, har lokacin bai samu ba, ya kusan mintina goma a tsaye bakin kofar hostel din kafin yayi nasarar samun wayarta
"Ki daga dan Allah"
Ya furta a hankali, ya kasa tsaida bugun zuciyar shi waje daya. Yankewa tayi, ya sake kira, sai gashi ta daga, muryata can kasa tace
"Hamma?"
Kamar tana son tabbatar da cewa shi dinne ya kirata
"Layla me ya sameki? Me yasa baki fadamun baki da lafiya ba? Ina wajen hostel dinku, ki sauko in ganki"
Ya karasa yana kokarin tuna ranar karshe da yayi magana cikin sauri kuma da yawa a lokaci daya irin haka.
"Ni ba zan iya fitowa ba"
Layla ta fadi daga dayan bangaren, tana saka zuciyar shi kara dokawa, shi fa sam bayason yaji bata da lafiya. Kuma gashi tana fada mishi ba zata iya fitowa ba, wacce irin rashin lafiya ce haka?
"Ki fito ba wasa nake ba, Allah ina jira"
Ya karasa yana kashe wayar, duk wata addu'a da tazo bakin shi ita yake karantawa, ya kafa idanuwan shi a kofar hostel din, har ya hango ta, dakyar take tafiya yana gani, yana kuma ji har cikin ran shi. Ta tsaya yafi sau biyar kafin ta iso inda yake tana tsugunnawa da alamar ciwon da take ji. Ta kwana biyu batayi ciwon mara irin na yau ba. Sunje clinic da Anisa an kuma bata magani, ta sha, sai taji kamar ya kara mata ciwon da take jine. Dakyar ta sauko yanzun ma
"Layla"
Rayyan ya kira yana tsugunnawa shima, idanuwanta da suka sauya kala zuwa wani launi da baisan ya zai fassara ba ta dago tana saukewa cikin nashi da dole ya rissina su saboda yanda ta kara ma bugun zuciyar shi gudu
"Ta shi muje asibiti..."
Ya furta a hankali, kai ta girgiza mishi
"Munje tun jiya, na sha magani"
Shima kan yake girgiza mata
"Baki da lafiya har yanzun"
Dakyar ta iya fadin
"Zai tafi nan da kwana hudu"
Da rashin fahimta yake kallon ta
"Ya akayi kika sani?"
Kwanciya kawai Layla take son yi saboda cikinta kamar ana shara a ciki. Kilan Allah ya taimaketa tayi bacci
"Hamma..."
Ta fadi a gajiye, ganin kallon da yake mata ya sata cewa
"Period ne..."
A hankali tana mayar da kanta ta saddar, ya dauki wasu dakika kafin ya fahimci ma'anar kalamanta. Tsintar kan shi yayi da mikewa yana kama hannunta ya taimaka mata ta mike, jin shi yayi da dumi fiye da kowanne lokaci, hakan ya saka shi taba fuskarta, zazzabine ruf a jikinta. Idan yace ya tafi gida hankalin shi ba zai taba kwanciya ba, bayan yasan babu wanda zai kula da ita idan yabarta nan hostel din
"Muje gida, in kinji sauki sai ki dawo"
Yanda yai maganar babu wajen gardama, kallon shi Layla takeyi, bama zata iya gardama ba a halin da take ciki, kwanciya kawai take son yi
"Zan dauko abu, kuma idan na koma ba zan iya sake saukowa ba Allah... Hamma kabarni anan, zuwa gobe ma zai fara sauki in shaa Allah"
Kai yake girgizawa tunda ta fara magana, sai yanzun ya kula duk tayi zuru-zuru. Idan dawowar ne gobe ta dawo, amman yau kam ba zai iya barinta ba, tunani zai mishi yawa
"Layla tare zamu tafi, karki mun gardama"
Yanda ya karasa maganar da wani irin sanyin murya da bata taba jiba yasa ta cewa
"Ka aramun wayarka in kira Anisa to"
Mika mata wayar yayi, sai da ta dan matsa sannan tayi kiran, kallonta yake duk da baya iya jin me take fadi harta gama ta dawo tana sake tsugunnawa, sun kai mintina goma da wani abu kafin Anisa ta sauko, da fara'a take kallon Rayyan
"Ina wuni..."
Yanayin yanda ta rage muryarta yasa Layla mikewa tsaye tana mata wani kallo
"Sannun ki"
Shine amsar da ta samu daga wajen Rayyan din, kyau yake yi mata tun ranar farko data fara ganin shi, amman tambayar duniya da tayiwa Layla akan shi sai ta hade rai
"Bana so Anisa, bana so Allah"
Takan fadi cike da kishin daya tabbatarwa da Anisa ba ciki daya Layla suka fito da Rayyan ba. Hakan dai bai hana yaci gaba da burgeta ba. Ledar da take hannun Anisa ta karba tana fadin
"Nagode..."
Idan wani abu na makaranta ne daya kama sai an duba yanar gizo, da kwamfuta din shi kirar laptop yakanyi amfani. Kuma yana daya daga cikin mutane hudun da suke jagorantar ajin su ta fannin karatu, inda Rayyan dinne na biyu, idan da zai maida hankali ma tsaf zai zama gwarzo a ajin.
"Wai ba test kace kuna da shi ba?"
Bilal ya bukata, kai Rayyan ya jinjina mishi
"Ba zakayi karatu ba?"
Raba idanuwan shi da takarda Rayyan yayi ya kalli Bilal din, kallon da yake fassara "Da ni kake?". Kafin ya mayar da hankalin shi kan zanen da yakeyi
"Lokutta irin haka kana sakani inajin kamar bani da kokari"
Dan numfashi Rayyan ya fitar
"Kana da kokarin ne? Tun dazun kake kallon takarda daya"
Bude baki Bilal yayi, kafin ya mike zaune
"Kasan wanne lissafine? Kake kira takarda daya kamar wani abu marar wahala"
Fensirin hannun shi Rayyan ya ajiye, ya dan juya zaman shi yana mika hannu ya fisge takardar da take hannun Bilal, duba tambayar yayi, batare daya dago ba yace
"Ina misalin? Wanda akayi?"
Tashi Bilal yayi ya dauko jakar shi yana fito da littafi ya dubo wani misalin yana mikawa Rayyan daya karba, sosai ya nutsar da hankalin shi yana ganin yanda aka fitar da abin. Kafin ya fara duba wanda Bilal yake nazari, a idanuwan shi yaga yanda komai zai kasance, juyawa yayi ya ajiye akan tebir, cikin mintina kasa da sha biyar ya gama fitar da shi yana jefawa Bilal din
"Ba zaka maida hankali sanda ake maka abu a aji ba, kana can kana wasu tunane-tunane..."
Rayyan din ya fadi a fadace, dauka Bilal yayi yana duddubawa, murmushi yayi
"Bayani zakayi mun dalla-dalla..."
Hararar shi Rayyan yayi yana sake hade fuska, dariya Bilal yayi mai sauti wannan karin yana tashi ya janyo kujera ya zauna gefen Rayyan din daya ke watsa mishi wani kallo
"Ni kyaleni"
Ya fadi saboda surutu Bilal zai sa shi yayi, watakila sai yayi mishi bayani sau biyu ko fiye da haka, amman sai ya zaqulo wata tambayar yayi mishi. Haka kuwa akayi, har saida ya kule daya fahimci Bilal din ya gane, surutun kawai yake so ya saka shi. Ganin yayi Rayyan din yayi banza ya kyale shi yasa Bilal komawa kan gado abin shi, so yake ya sake fitar da lissafin a wata takarda daban dan yaga koya fahimta, shekarar shi ta farko ya fadi jarabawa guda daya. Rayyan yaita mishi fada kamar zai mare shi, wani lokacin ko bai niyyar karatu ba yakan dauko yayi saboda masifar Rayyan da ba karewa takeyi ba.
Ranar ne karo na farko da yaji kamar yayi dissapointing din Rayyan din, yanayine da baya so ya kara faruwa. Duk da kwakwalwar su ta bambanta, yana iya kokarin shi. Rayyan zanen shi yaci gaba dayi, amman baya tafiya yanda yake so, saboda yau ya kasa rufe gabaki daya tunanin shi kamar yanda yakanyi a lokutta irin haka. Layla ce manne a ran shi, tun jiya bai ganta ba, har wayarta ya kira amman a kashe. Yanzun ma wayar da take ajiye kan tebir ya dauka ya duba ko ta turo mishi sako, amman shiru, sake gwada kiranta yayi yana jin bata shiga ba, kamar matsalar network tunda ba'a ce mishi a kashe take ba
Wajen mintina sha biyar tsakani, batare daya kalli Bilal ba yace
"Ka ga Layla?"
Kai Bilal din ya jinjina mishi, kullum sai yaga Layla, in ya fita kafin ya wuce aji saiya biya ya kirata ta sauko yaga ya ta kwana, ko tana da wata matsala sannan ya wuce, amanar ta Abbu ya bashi, babu yanda za'ayi ba zai dubata a duk rana ba.
"Ni ban ganta ba"
Cewar Rayyan da wani yanayi a muryar shi da yasa Bilal dagowa
"Ba tazo aji ba, bata jin dadine tun jiya da dare"
Mikewa tsaye Rayyan yayi zuciyar shi na wata irin dokawa
"Me yasa baka fada mun ba?"
Kallon shi Bilal yayi yanda ya hargitse lokaci daya kamar yace mishi wani babban abune ya samu Layla, shi yasan lokacin al'adarta ne, badan ta gaya mishi ba, sai dan ya kula da duk wata haka take fama. Wancen watan da ciwon da komai ta zo wajen Rayyan, yana ganin yanda har fuskarta Rayyan din ya taba ko zaiji zazzabi bayan ya tambayeta me ya sameta tace mishi bakomai. Bai fada mishi ba saboda yasan idan akan Layla ne Rayyan zai dauki abin ya saka a ran shi. Amman can kasan zuciyar shi yana jin kamar akwai wani dalili bayan nan, dalilin da bayaso yasan shi saboda yana da yakinin zai saka shi yaji kamar bai kyauta ba.
Jacket din shi da take can gefen gado Rayyan ya dauka yana sakawa akan kayan jikin shi da riga da wando ne, ya dauki wayar shi yana kama hanyar kofa
"Ina zaka je? Takwas da rabi fa"
Ko amsa bai samu ba, numfashi kawai ya iya saukewa yana bin Rayyan din da kallo harya fice daga dakin. Wani irin sauri yake ya karasa titi ya samu machine zuwa gate din makaranta, kawai so yake ya fara hango hostel din su Layla, bai daina gwada kiran lambarta ba, har lokacin bai samu ba, ya kusan mintina goma a tsaye bakin kofar hostel din kafin yayi nasarar samun wayarta
"Ki daga dan Allah"
Ya furta a hankali, ya kasa tsaida bugun zuciyar shi waje daya. Yankewa tayi, ya sake kira, sai gashi ta daga, muryata can kasa tace
"Hamma?"
Kamar tana son tabbatar da cewa shi dinne ya kirata
"Layla me ya sameki? Me yasa baki fadamun baki da lafiya ba? Ina wajen hostel dinku, ki sauko in ganki"
Ya karasa yana kokarin tuna ranar karshe da yayi magana cikin sauri kuma da yawa a lokaci daya irin haka.
"Ni ba zan iya fitowa ba"
Layla ta fadi daga dayan bangaren, tana saka zuciyar shi kara dokawa, shi fa sam bayason yaji bata da lafiya. Kuma gashi tana fada mishi ba zata iya fitowa ba, wacce irin rashin lafiya ce haka?
"Ki fito ba wasa nake ba, Allah ina jira"
Ya karasa yana kashe wayar, duk wata addu'a da tazo bakin shi ita yake karantawa, ya kafa idanuwan shi a kofar hostel din, har ya hango ta, dakyar take tafiya yana gani, yana kuma ji har cikin ran shi. Ta tsaya yafi sau biyar kafin ta iso inda yake tana tsugunnawa da alamar ciwon da take ji. Ta kwana biyu batayi ciwon mara irin na yau ba. Sunje clinic da Anisa an kuma bata magani, ta sha, sai taji kamar ya kara mata ciwon da take jine. Dakyar ta sauko yanzun ma
"Layla"
Rayyan ya kira yana tsugunnawa shima, idanuwanta da suka sauya kala zuwa wani launi da baisan ya zai fassara ba ta dago tana saukewa cikin nashi da dole ya rissina su saboda yanda ta kara ma bugun zuciyar shi gudu
"Ta shi muje asibiti..."
Ya furta a hankali, kai ta girgiza mishi
"Munje tun jiya, na sha magani"
Shima kan yake girgiza mata
"Baki da lafiya har yanzun"
Dakyar ta iya fadin
"Zai tafi nan da kwana hudu"
Da rashin fahimta yake kallon ta
"Ya akayi kika sani?"
Kwanciya kawai Layla take son yi saboda cikinta kamar ana shara a ciki. Kilan Allah ya taimaketa tayi bacci
"Hamma..."
Ta fadi a gajiye, ganin kallon da yake mata ya sata cewa
"Period ne..."
A hankali tana mayar da kanta ta saddar, ya dauki wasu dakika kafin ya fahimci ma'anar kalamanta. Tsintar kan shi yayi da mikewa yana kama hannunta ya taimaka mata ta mike, jin shi yayi da dumi fiye da kowanne lokaci, hakan ya saka shi taba fuskarta, zazzabine ruf a jikinta. Idan yace ya tafi gida hankalin shi ba zai taba kwanciya ba, bayan yasan babu wanda zai kula da ita idan yabarta nan hostel din
"Muje gida, in kinji sauki sai ki dawo"
Yanda yai maganar babu wajen gardama, kallon shi Layla takeyi, bama zata iya gardama ba a halin da take ciki, kwanciya kawai take son yi
"Zan dauko abu, kuma idan na koma ba zan iya sake saukowa ba Allah... Hamma kabarni anan, zuwa gobe ma zai fara sauki in shaa Allah"
Kai yake girgizawa tunda ta fara magana, sai yanzun ya kula duk tayi zuru-zuru. Idan dawowar ne gobe ta dawo, amman yau kam ba zai iya barinta ba, tunani zai mishi yawa
"Layla tare zamu tafi, karki mun gardama"
Yanda ya karasa maganar da wani irin sanyin murya da bata taba jiba yasa ta cewa
"Ka aramun wayarka in kira Anisa to"
Mika mata wayar yayi, sai da ta dan matsa sannan tayi kiran, kallonta yake duk da baya iya jin me take fadi harta gama ta dawo tana sake tsugunnawa, sun kai mintina goma da wani abu kafin Anisa ta sauko, da fara'a take kallon Rayyan
"Ina wuni..."
Yanayin yanda ta rage muryarta yasa Layla mikewa tsaye tana mata wani kallo
"Sannun ki"
Shine amsar da ta samu daga wajen Rayyan din, kyau yake yi mata tun ranar farko data fara ganin shi, amman tambayar duniya da tayiwa Layla akan shi sai ta hade rai
"Bana so Anisa, bana so Allah"
Takan fadi cike da kishin daya tabbatarwa da Anisa ba ciki daya Layla suka fito da Rayyan ba. Hakan dai bai hana yaci gaba da burgeta ba. Ledar da take hannun Anisa ta karba tana fadin
"Nagode..."