Sashe 68
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kan shi Rayyan ya durkusar kasa sosai yana wani irin maida numfashi, watakila haka ake ji yayin fitar rai, saboda wani abu ke fisgar shi da kalaman Bilal. Dakyar bakin shi ya iya furta
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Yana dagowa ya dafe fuskar shi da hannuwan shi ko inya bude zai farka daga wannan mummunan mafarkin. Bilal ma kasa yayi
"Hamma idan nace kuskure ne zaka yarda?"
Bude fuskar shi Rayyan yayi
"Kuskure? Cikin ne zaka dauka ka dora akan kuskure? Layla fa... Bilal ba wata bace Layla"
Rayyan ya fadi yana kallon Bilal, har lokacin yana son ya san me ma yake ji gabaki daya
"Kuskure n..."
Mikewar da Rayyan yayi na katse ma Bilal maganar daya fara. Hannu ya mike mishi
"Bani mukullin mota..."
Da wani yanayi Bilal yake kallon shi
"Baka iya tuqi ba Hamma, me zakayi da shi?"
Yanda Rayyan din yake kallon shi ya saka shi mikewa
"Ni ya kamata in bar maka dakin"
Ya karasa yana ficewa, ko takalmi babu a kafar shi, komawa Rayyan yayi ya zauna, kan shi ya dora jikin gadon dakin yana jin kamar zai mutu. Kwanan shi biyar yau rabon da ya busa hayaki, saboda yana son ya bari, baima yi tunanin akwai wahala sosai a barin shan tababa sai da yake son bari. Jakar shi da sai lokacin ya sauketa daga kafadar shi ya bude, jikin shi har rawa yake lokacin daya dauko kwalin tabar, a yanda yake jin shi zabi biyu yake da shi, ko tabar ko kwayoyin da yayi ma Bappa alkawarin zai sha su kan ka'ida a kowanne yanayi
"Abu daya zai iya sa ka koma Rayyan, dan Allah ka kula, kaga su da taba ne kawai matsalar ka yanzun"
Ya kan ga Bappa din ya dauki robar maganin na shi yana lekawa, kamar yana son kirga su batare daya fito da su gabaki daya ba, ba zai iya surutun maimaita magana daya ba saiya kyale shi. Shisa yanzun ya zabi tabar, kunnawa yayi kuwa, sai da yaja kara goma amman a banza, banda zafin da kirjin shi ya kara har tari yake kamar sabon shiga a shan sigarin. Ko dan yana kokawa da numfashin shine bai sani ba. Amman ya kasa samun sauki ko yaya. Yanda duk yaso ya hango Layla da Bilal ya kasa, idan wani ne daban zai iya lakaba mishi kowanne sigar laifi.
Zai iya cewa tursasa Layla yayi, zai iya cewa ya bata wani abune ta sha. Zai iya cewa komai, amman Bilal ba zaiyi abu daya daga cikin duka tunanin shi ba, gabaki daya Bilal bashi da wani dalili da zai iya tunawa nayin abinda yayi. Shisa baiga dalilin da zai saurari komai ba, iya abinda yaji ya ishe shi har karshen rayuwar shi. Kirjin shi zafi yake kamar ana hura wuta a ciki. Shisa ya sulale ya kwanta, babu abinda yake mishi yawo sai Bilal da Layla da ya kasa haskowa saboda tabbas zuciyar shi tarwatsewa zatayi. Mutum biyun da yafi yarda dasu akan kowa, mutum biyu da suka fi kowa kusanci a rayuwar shi.
Bilal yana fita a bakin kofa ya zauna, hawaye yake nema ko zai samu sauki amman ya rasa su yau
"Kaina kamar zai bude nake ji"
Muryar Jabir ta daki kunnuwan Bilal din, gefen shi ya samu shima ya zauna. Kowa da abinda yake ji, kowa da abinda yake tunani. Yanayi ne da babu wanda zai iya lallashin wani
"Na kasa yarda Hamma Rayyan zai mana haka, zuciyata ta kasa yarda..."
Numfashi Bilal yaja yana saukewa
"Bashi bane ba, ni ne"
Murmushi mai kunar rai Jabir yayi
"Idan kace kaine sai kake tunanin abin zai mana saukin dauka? Ka daina dan Allah Hamma, kabari muji da abu daya"
Jabir ya karasa yana mikewa, gara ko ruwa yaje ya dauka ya sha, koya watsama jikin shi. Koma me da zai dan saukaka mishi abinda yake ji, bin shi da kallo Bilal yayi, wato babu wanda yake son sauraren shi, haka girman yardar da sukayi mishi yake daman? Haka suke ganin ba zai taba cin amanar su ba. Kamar an dora dutse a kirjin shi haka yaji. Kafafuwan shi ya kara ja yana hade su da kirjin nashi ko zai ji dama-dama. Kan shi ya dora a jikin gwiwar shi yana sauke numfashi a hankali.
*
Zaune Ayya take akan kafet, sai yanzun komai yake tabata, yanzun girman abin yake yawo a kwanyarta. Layla da Rayyan, kaddarar su mai girma ce haka ashe? Duk yanda taso ta shiga tsakanin su alkalami ya gama rubutun shi akan su, sai kawai tunanin farraqun da tayi musu ya fado mata. Zuciyarta na wani irin tsalle ta koma cikin makoshinta, daman ance wani rabon har kisa yakeyi. Ko nasu ne yazo a haka? Raba sun da tayine da rabo a tsakanin su shisa ya kullu ta wannan gurbatanciyyar hanyar da take jin gara mata auren, komin yanda zuciyarta bata so zata koyi jure ganin su a tare kamar yanda take ganin Mami da Abbu.
Batason laifin ya zagayo ya dawo kanta, bataso saboda hakan na sakata jin kamar an tsomata a ruwan kankara. Zuciyarta ta tsinke daga inda take a kulle lokacin da taga Abbu a kasa, dan tana jin yanda zuciyar ke mata barazanar daina bugawa a mintunan da Abbu yayi bai tashi ba, yaran da take karewa da kominta, yaran da take jin zata iya komai dan nisanta su da juna, sune hanya irin wannan ta hada har suna neman kashe mata mijin da take so fiye da su, mijin da take kauna fiye da yanda take son kanta.
Yanzun ma kallon shi takeyi, yanda yake durkushe kan gwiwoyin shi yana sharar kwalla, zuciyarta kamar zata fito waje
"Dan Allah Ahmadi kayi hakuri, kar wani ciwon ya shigeka lokaci daya, bansan ya zanyi ba... Kayi hakuri dan Allah, komai zai zo da sauki"
Take fadi tana kokarin tarbe nata hawayen, tasan mijinta, ta san shi din mai rauni ne akan lamurran duniya. Sau nawa ita take nakuda amman take samun karfin halin bashi hakuri duk idan ciwo ya kwanta mata, kuka riris haka Ahmadi yakeyi duk idan ta fara nakuda, balle takan yi mai dogon zangon da sai an fara fidda rai da ita. Yana da raunin da batasan ya zata misalta a fahimta ba, shisa tasan da wahala ya iya daukar wannan kaddarar salin alin. Bata su Rayyan ko Layla takeyi ba yanzun, ta mijinta takeyi, ta tunanin halin da yake ciki da wanda zai shiga anan gaba.
Watakila da batayi katsalandan a cikin al'amarin ba da haka bata faru. Akwai abinda ya girmi tsanar da tayiwa Mami, akwai abinda zai iya tabata fiye da kaddarar da ta hada Mami da Abbu waje daya. Yanzun take gani, abubuwa ne masu tarin yawa suke mata yawo, lokuttan da tayi kokarin shiga hurumin da ba nata ba, canza lamurran da bata da iko a kan su. Zuciyarta da tsoro take bugawa, da kokwanto mai girman gaske kan makomar ayyukanta, kan inda kaddarar da tayi komai dan ta canza take son ta kai ta
"Idan mutuwa ta daukeni yanzun fa Maimuna? Ni ya zanyi? Me zan fadi akan amanar da ban rike da kyau ba? Ke da kanki kin gano mun matsala a rikon da nayiwa Layla, Allah da yake ganin komai fa?"
Sai Ayya taji kamar da ita yake, kamar ya watsa mata ruwan gishiri a ciwukan ta haka taji. Idan ita tata mutuwar ta dauketa kafin ta mike fa? Ya zatayi ita? Me zata fada akan katsalandan da tayi ma kaddara? Wanne hujjoji zata labe a bayan su? Hawayen da suka zubo mata masu zafi ne na gaske.
"Ba kai bane baka da abin fadi, nice. Wallahi nice ban da abinda zance, ya zan kalli yan uwana? Me zance musu ya faru?"
Mami da ta samu bakin magana tayi jero tambayoyin wani sabon tashin hankalin yana dirar mata, tunda suka shigo dakin ta jujjuya maganganun da Ayya ta fada mata. Idan tace ga dalili daya da ya saka ta barin Layla komawa Zaria zatayi karya. Bata san ya akayi ta yarda ta koma ba, a wannan halin ma ba zata iya dorawa kaddara ba, ba kuma ta son yin amfani da kalmar sakaci da take ta mata yawo. Gani tayi kamar akan tarbiyar duka yaran tana iya yinta. Yaune take gane baka taba yin iya yinka a tarbiya, saboda ba abu bane na lokaci daya, ba kuma abu bane iri daya.
Tarbiyar jiya takan banbanta da ta yau, saboda a duk rana halaye kan canza, yanayi mai girma ko karami, bakon yanayi kan samu wajen zama da dan adam. Shisa tarbiya zata zamana yau da kullum. In kayi jiya, yau ma ka kara, saika hada da addu'ar samun karfin yin fiye da ta yau a goben da zaka samu aronta.
"Nayi iya yi na"
Da iyaye da yawa kan fadi ba uzuri bane ba, ba kuma lallai ya zama hujja ba a gaban Allah, su yaran amana ne. Mutum ma ya baka amana kaci ya kake karewa, balle Allah da kan shi da ya zabeka a cikin mutane da dama ya baka amanar yara, ya baka aron lokaci, lafiya, da wadatar kula da su. Soyayyar Layla ta rufe mata ido
"Rikon maraya da wahala"
Shine kalaman da mutane kan furta a duk lokacin da tarbiyar marayun da suka dauki amanar kula dasu ta sami matsala. Kusan shine hujjar da suke kafawa, har wanda basa rike da maraya ma suna hasaso wahalar da take cikin rikon maraya. Yau ta canza mata tunani gabaki daya, babu wani riko na yaro da yake da sauki, babu kuma wani kalar yaro da baya bukatar tarbiya. Maraya ko mai iyaye, musamman maraya da tausayin rashin iyaye kan saka iyayen rikon sakaci kan tarbiyar shi. Bata san me yasa duk wannan tunanin yazo mata a kurarren lokaci ba, babu wanda zai mata uzuri kamar yanda ta kasa yiwa kanta yanzun
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Yana dagowa ya dafe fuskar shi da hannuwan shi ko inya bude zai farka daga wannan mummunan mafarkin. Bilal ma kasa yayi
"Hamma idan nace kuskure ne zaka yarda?"
Bude fuskar shi Rayyan yayi
"Kuskure? Cikin ne zaka dauka ka dora akan kuskure? Layla fa... Bilal ba wata bace Layla"
Rayyan ya fadi yana kallon Bilal, har lokacin yana son ya san me ma yake ji gabaki daya
"Kuskure n..."
Mikewar da Rayyan yayi na katse ma Bilal maganar daya fara. Hannu ya mike mishi
"Bani mukullin mota..."
Da wani yanayi Bilal yake kallon shi
"Baka iya tuqi ba Hamma, me zakayi da shi?"
Yanda Rayyan din yake kallon shi ya saka shi mikewa
"Ni ya kamata in bar maka dakin"
Ya karasa yana ficewa, ko takalmi babu a kafar shi, komawa Rayyan yayi ya zauna, kan shi ya dora jikin gadon dakin yana jin kamar zai mutu. Kwanan shi biyar yau rabon da ya busa hayaki, saboda yana son ya bari, baima yi tunanin akwai wahala sosai a barin shan tababa sai da yake son bari. Jakar shi da sai lokacin ya sauketa daga kafadar shi ya bude, jikin shi har rawa yake lokacin daya dauko kwalin tabar, a yanda yake jin shi zabi biyu yake da shi, ko tabar ko kwayoyin da yayi ma Bappa alkawarin zai sha su kan ka'ida a kowanne yanayi
"Abu daya zai iya sa ka koma Rayyan, dan Allah ka kula, kaga su da taba ne kawai matsalar ka yanzun"
Ya kan ga Bappa din ya dauki robar maganin na shi yana lekawa, kamar yana son kirga su batare daya fito da su gabaki daya ba, ba zai iya surutun maimaita magana daya ba saiya kyale shi. Shisa yanzun ya zabi tabar, kunnawa yayi kuwa, sai da yaja kara goma amman a banza, banda zafin da kirjin shi ya kara har tari yake kamar sabon shiga a shan sigarin. Ko dan yana kokawa da numfashin shine bai sani ba. Amman ya kasa samun sauki ko yaya. Yanda duk yaso ya hango Layla da Bilal ya kasa, idan wani ne daban zai iya lakaba mishi kowanne sigar laifi.
Zai iya cewa tursasa Layla yayi, zai iya cewa ya bata wani abune ta sha. Zai iya cewa komai, amman Bilal ba zaiyi abu daya daga cikin duka tunanin shi ba, gabaki daya Bilal bashi da wani dalili da zai iya tunawa nayin abinda yayi. Shisa baiga dalilin da zai saurari komai ba, iya abinda yaji ya ishe shi har karshen rayuwar shi. Kirjin shi zafi yake kamar ana hura wuta a ciki. Shisa ya sulale ya kwanta, babu abinda yake mishi yawo sai Bilal da Layla da ya kasa haskowa saboda tabbas zuciyar shi tarwatsewa zatayi. Mutum biyun da yafi yarda dasu akan kowa, mutum biyu da suka fi kowa kusanci a rayuwar shi.
Bilal yana fita a bakin kofa ya zauna, hawaye yake nema ko zai samu sauki amman ya rasa su yau
"Kaina kamar zai bude nake ji"
Muryar Jabir ta daki kunnuwan Bilal din, gefen shi ya samu shima ya zauna. Kowa da abinda yake ji, kowa da abinda yake tunani. Yanayi ne da babu wanda zai iya lallashin wani
"Na kasa yarda Hamma Rayyan zai mana haka, zuciyata ta kasa yarda..."
Numfashi Bilal yaja yana saukewa
"Bashi bane ba, ni ne"
Murmushi mai kunar rai Jabir yayi
"Idan kace kaine sai kake tunanin abin zai mana saukin dauka? Ka daina dan Allah Hamma, kabari muji da abu daya"
Jabir ya karasa yana mikewa, gara ko ruwa yaje ya dauka ya sha, koya watsama jikin shi. Koma me da zai dan saukaka mishi abinda yake ji, bin shi da kallo Bilal yayi, wato babu wanda yake son sauraren shi, haka girman yardar da sukayi mishi yake daman? Haka suke ganin ba zai taba cin amanar su ba. Kamar an dora dutse a kirjin shi haka yaji. Kafafuwan shi ya kara ja yana hade su da kirjin nashi ko zai ji dama-dama. Kan shi ya dora a jikin gwiwar shi yana sauke numfashi a hankali.
*
Zaune Ayya take akan kafet, sai yanzun komai yake tabata, yanzun girman abin yake yawo a kwanyarta. Layla da Rayyan, kaddarar su mai girma ce haka ashe? Duk yanda taso ta shiga tsakanin su alkalami ya gama rubutun shi akan su, sai kawai tunanin farraqun da tayi musu ya fado mata. Zuciyarta na wani irin tsalle ta koma cikin makoshinta, daman ance wani rabon har kisa yakeyi. Ko nasu ne yazo a haka? Raba sun da tayine da rabo a tsakanin su shisa ya kullu ta wannan gurbatanciyyar hanyar da take jin gara mata auren, komin yanda zuciyarta bata so zata koyi jure ganin su a tare kamar yanda take ganin Mami da Abbu.
Batason laifin ya zagayo ya dawo kanta, bataso saboda hakan na sakata jin kamar an tsomata a ruwan kankara. Zuciyarta ta tsinke daga inda take a kulle lokacin da taga Abbu a kasa, dan tana jin yanda zuciyar ke mata barazanar daina bugawa a mintunan da Abbu yayi bai tashi ba, yaran da take karewa da kominta, yaran da take jin zata iya komai dan nisanta su da juna, sune hanya irin wannan ta hada har suna neman kashe mata mijin da take so fiye da su, mijin da take kauna fiye da yanda take son kanta.
Yanzun ma kallon shi takeyi, yanda yake durkushe kan gwiwoyin shi yana sharar kwalla, zuciyarta kamar zata fito waje
"Dan Allah Ahmadi kayi hakuri, kar wani ciwon ya shigeka lokaci daya, bansan ya zanyi ba... Kayi hakuri dan Allah, komai zai zo da sauki"
Take fadi tana kokarin tarbe nata hawayen, tasan mijinta, ta san shi din mai rauni ne akan lamurran duniya. Sau nawa ita take nakuda amman take samun karfin halin bashi hakuri duk idan ciwo ya kwanta mata, kuka riris haka Ahmadi yakeyi duk idan ta fara nakuda, balle takan yi mai dogon zangon da sai an fara fidda rai da ita. Yana da raunin da batasan ya zata misalta a fahimta ba, shisa tasan da wahala ya iya daukar wannan kaddarar salin alin. Bata su Rayyan ko Layla takeyi ba yanzun, ta mijinta takeyi, ta tunanin halin da yake ciki da wanda zai shiga anan gaba.
Watakila da batayi katsalandan a cikin al'amarin ba da haka bata faru. Akwai abinda ya girmi tsanar da tayiwa Mami, akwai abinda zai iya tabata fiye da kaddarar da ta hada Mami da Abbu waje daya. Yanzun take gani, abubuwa ne masu tarin yawa suke mata yawo, lokuttan da tayi kokarin shiga hurumin da ba nata ba, canza lamurran da bata da iko a kan su. Zuciyarta da tsoro take bugawa, da kokwanto mai girman gaske kan makomar ayyukanta, kan inda kaddarar da tayi komai dan ta canza take son ta kai ta
"Idan mutuwa ta daukeni yanzun fa Maimuna? Ni ya zanyi? Me zan fadi akan amanar da ban rike da kyau ba? Ke da kanki kin gano mun matsala a rikon da nayiwa Layla, Allah da yake ganin komai fa?"
Sai Ayya taji kamar da ita yake, kamar ya watsa mata ruwan gishiri a ciwukan ta haka taji. Idan ita tata mutuwar ta dauketa kafin ta mike fa? Ya zatayi ita? Me zata fada akan katsalandan da tayi ma kaddara? Wanne hujjoji zata labe a bayan su? Hawayen da suka zubo mata masu zafi ne na gaske.
"Ba kai bane baka da abin fadi, nice. Wallahi nice ban da abinda zance, ya zan kalli yan uwana? Me zance musu ya faru?"
Mami da ta samu bakin magana tayi jero tambayoyin wani sabon tashin hankalin yana dirar mata, tunda suka shigo dakin ta jujjuya maganganun da Ayya ta fada mata. Idan tace ga dalili daya da ya saka ta barin Layla komawa Zaria zatayi karya. Bata san ya akayi ta yarda ta koma ba, a wannan halin ma ba zata iya dorawa kaddara ba, ba kuma ta son yin amfani da kalmar sakaci da take ta mata yawo. Gani tayi kamar akan tarbiyar duka yaran tana iya yinta. Yaune take gane baka taba yin iya yinka a tarbiya, saboda ba abu bane na lokaci daya, ba kuma abu bane iri daya.
Tarbiyar jiya takan banbanta da ta yau, saboda a duk rana halaye kan canza, yanayi mai girma ko karami, bakon yanayi kan samu wajen zama da dan adam. Shisa tarbiya zata zamana yau da kullum. In kayi jiya, yau ma ka kara, saika hada da addu'ar samun karfin yin fiye da ta yau a goben da zaka samu aronta.
"Nayi iya yi na"
Da iyaye da yawa kan fadi ba uzuri bane ba, ba kuma lallai ya zama hujja ba a gaban Allah, su yaran amana ne. Mutum ma ya baka amana kaci ya kake karewa, balle Allah da kan shi da ya zabeka a cikin mutane da dama ya baka amanar yara, ya baka aron lokaci, lafiya, da wadatar kula da su. Soyayyar Layla ta rufe mata ido
"Rikon maraya da wahala"
Shine kalaman da mutane kan furta a duk lokacin da tarbiyar marayun da suka dauki amanar kula dasu ta sami matsala. Kusan shine hujjar da suke kafawa, har wanda basa rike da maraya ma suna hasaso wahalar da take cikin rikon maraya. Yau ta canza mata tunani gabaki daya, babu wani riko na yaro da yake da sauki, babu kuma wani kalar yaro da baya bukatar tarbiya. Maraya ko mai iyaye, musamman maraya da tausayin rashin iyaye kan saka iyayen rikon sakaci kan tarbiyar shi. Bata san me yasa duk wannan tunanin yazo mata a kurarren lokaci ba, babu wanda zai mata uzuri kamar yanda ta kasa yiwa kanta yanzun
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"