Sashe 33
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta karasa muryarta na rawa, tun azahar yau ta gama darasinta, tana komawa hostel ta fara aikin yi mishi girkin nan saboda ta siyo kifine sai tayi mishi sauce ta dafa wake da shinkafa. Anisa da suke daki daya taso tayata, tunda wani lokaci har girki sukan hada, tace karta damu zatayi in yaso sai Anisa din tayi wanke-wanke. Ba tsafta bace bata da ita, kawai halin jujun Rayyan ta sani, zai iya tambaya idan ita kadai tayi girkin, kuma ba zata iya kallon shi tayi karya ba, yana ganeta, ta sha gwadawa bakinta yanayin jini
"Karya ne"
Yake fadi a duk lokuttan yana kara kai mata wani dukan, sakar mata hannu yayi yana komawa wajen shi ya zauna. Tsaye tayi a wajen tana murza hannunta, shikuma ita yake jira ta zuba mishi, hakan ta kula da shi, bata dauko faranti ba, a dakin ta samu da cokali, sai da ta dauki ruwan leda tana fita wajen dakin ta daurayo su sannan ta dawo
"Kazama, a bakin kofa kika zubar mun da ruwa ko?"
Bata kula shi ba, turo labbanta tayi kawai, sai lokacin ta cire hijabin da yake jikinta tana ajiyewa kan teburin da yake cikin dakin. Bai taba mata maganar kayan da take sakawa ba, amman tasan bayaso, har wata zuciyar na fada mata kishi yake shisa, ba karamin dadi take ji ba kuma. Jacket din shi guda hudune a wajenta yanzun, kuma duk idan ta saka kayan da baisone yake bata. Kamar yana yawo da jacket dinne yanzun ko zai ganta da kayan da bayaso, dan kwanaki a jakar shi ya fito da jacket din. Kuma Rayyan sam bai damu da yawan mutanen da suke waje ba idan ya tashi yi mata abu, kamar ma baya ganin su haka yakeyi.
Abincin ta zuba mishi tana neman waje ta zauna, ya fara ci yaga yanda take bin duk cokalin da zai kai a bakin shi da kallo, kai ya girgiza yana ajiye farantin da ya daga, ya gyara zaman shi sosai
"Me yasa zakiyi girki ba zakici ba?"
Tasan baya tambayeta dan ta bashi amsa bane, shisa tayi shiru, ita batama san tanajin yunwa haka ba sai yanzun da taga yana cin abincin. Cokali ya dauka yana mika mata, zata saka cikin abincin ya dakatar da ita da fadin
"An taba marin ki cikin ido? Ba zaki tashi ki wanko shi ba, kazama kawai"
Mikewa tayi tana daukar sauran ruwan da ta ajiye a gefe ta daurayo cokalin ta dawo. Tare suka cinye abincin tana kara zuba musu wani. Abin bai mata wani iri ba, zuwanta makarantar wannan ne karo na wajen biyar da suke cin abinci tare, na farkon ta kusan raba dare data juya yanayin su tare take hangowa sai wani murmushi ya kwace mata da ba zata ce ga dalilin shi ba. Da yake yana cin abinci da sauri, kafin taci guda daya yaci uku, baisan dalilin da zaisa ka tsaya yanga in zakaci abinci ba. Da kanshi ya dauki kular yana kara mata ya zuba mata miya a kai, abincin da yawa tayi.
Yasan Bilal in dai ba wani abu yaci a wajen Aysha ba, zaici, in baici ba da safe sai su dumama suci abinsu. Layla na karasawa, ruwa kawai ta sha, batama gama ba Rayyan ya mike
"Tashi muje"
Kallon shi tayi da tashin hankali a fuskata
"Ina zamu je? Hamma kabari abinci ya tsarga mun, yanzun fa nagama ci"
Kallon da yayi matane yasata mikewa ta dauki hijabinta tana buga kafarta, duka Rayyan ya kaimata tana kaucewa dan ta gan shi
"Zaki wuce ko saina kwada miki mari?"
Ya bukata, fita tayi daga dakin, shima takalmi ya zira a kafafuwan shi yana fita, baisan ko Bilal ya dauki mukulli ba, shisa ya janyo kofar kawai, gidan su ba'a taba yin sata ba. Kusan ko yaushe Bilal kan yabi halayyar yan gidan. Ko baka rufe daki ba, wani zai janyo maka. Haka sukeyi, in shanya kayi hadari ya hado ma za'a kwashe maka, inka dawo a kawo maka. Suna da kirki matuqa. Shisa bayajin dadin yanda Rayyan yake hade musu girar sama da ta kasa. Shiya fara yin gaba Layla na biye da shi, cikinta take ji har wuya, inda tasan ba zai bari abinci ya natsa mata ba, da bata cika cikinta haka ba.
Ganin har sun kai titi suna tsallakawa yasa ta fadin
"In mukai nisa fa ba zamu sama abin hawa ba"
Dan juyawa Rayyan yayi ya kalleta, hannunta yake shirin kamawa ta kauce
"A kafa? Hamma a kafa? Tafdin... In dai rakani zakayi nagode...amman ni wal..."
Da sauri yace
"Karma ki rantse, zakiyi azumi yarinya... Ki zo mu tafi"
A kafa yake jin tafiya, saboda yana son dan takawa tunda ya cika cikin shi, kuma ko ba haka ba, a ranshi yana jin yin tafiyar tare da ita, ko tana so ko bata so ba matsalar shi bane ba, duk yau ganinta ne yadan nutsar da shi, amman da wani kunci ya wuni, wasu ranakun idan yana azumin yakan ji shi wasai, har Qur'ani yakan dauka ya karanta. Amman wasu ranakun bawai bayaso ya dauka bane, kawai wata irin kasala kan rufe shi duk idan ya yunkura sai ya kasa, haka zai hakura yaita juyi, inya gaji ya kunna sigari ya bukama cikin shi.
"Ni dan Allah kabarni, wallahi nagaji, kuma na saka dogon takalmi"
Layla ta furta tana shirin yin kuka, tun kafin ta fito take murnar zuwa ta gan shi, amman yanzun harya isheta, ta ina zata fara shafawa a kafa ana zaune lafiya. Zagaye suka fara
"Layla..."
Ya furta cike da kashedin da yasata tsayawa waje daya, yasan ko bata zagin shi a ranta, tana tunanin hanyoyin da zata jibge shi idan ta samu dama ne saboda kallon da takeyi mishi, hasken wutar lantarki ya sake ma idanuwanta launi, sai da gabanshi ya fadi daya kalle su, musamman da irin kallon da take watsa mishi, hannunta ya damqa yana janta tana tirjewa kamar karamar yarinya. Bai damu ba, cigaba yayi da janta har suka karasa wani shago, yana rike da hannunta har lokacin ya siya silipas, babu karamar lamba, dan koshi sun mishi yawa, sakinta yayi ya fito dasu daga leda yana ajiye mata
"Ni ce zan saka wannan?"
Ta bukata tana ware mishi ido, kamar duk ranar bataga wani abu daya daga mata hankali irin shi ba, takalman kafafuwan shi dana fata ne yan zire ya cire yana saka silipas din
"Hamma..."
Cikin ido ya kalleta
"Kina gwada hakurina Layla, kin sani ko? Wallahi ba zan sake magana dake ba"
Dogayen takalman kafarta ta cire, ta saka nashin, da kanshi ya kwashe nata ya saka a ledar daya zaro silipas din yana bata, karba tayi ta rike baqar ledar. Hannunta ya sake kamawa suna tafiya. A hankali har suka fara hango makaranta, ba hira sukeyi ba sam balle tace tafiyar tana mata dadi, amman yanayin Rayyan din ya nuna yana cikin nishadi. Musamman yanda ya kalleta yaga tana ta turo baki
"Ki maida hankali, kilan bakin ki ya rigaki zuwa hostel"
Ya furta yana kara sauri, yana kallon yanda take kokarin kamo shi tana kara turo baki, sai da tasa murmushi ya kusan kwace mishi, tunda dai babu yanda zatayi da shi. Har kusan kofar hostel din ya karasa da ita, inda sukaci karo da su Bilal su kuma, Aysha zata rako shi, sunyi tsaye suna hira
"Hamma!"
Ta kwala mishi kira tana murmushi, kallon su Bilal yakeyi da mamaki suna karasowa inda suke, hannun Layla da yake cikin na Rayyan ya kalla, bai amsa Layla ba saboda wani sanannen abu da yaji ya mishi tsaye a makoshi. Kirjin shi harya fara zafin da yakan mishi duk idan ya gansu tare haka
"Ayshan Hamma"
Layla ta fadi tana mata murmushi
"Layla..."
Aisha tace cikin gaisuwa, tana kallon Rayyan
"Ina wuni"
So yakeyi yayi mata murmushi koya ne, amman sam bayajin yi
"Lafiya kalau. Sannu da kokari, mungode"
Ya fadi, yana saka Bilal kallon shi cike da mamaki, Layla ma mamakin takeyi, shi kuma tun rannan yake so yayi mata godiya saboda tana ma Bilal kirki. Tun satin daya wuce yake hada kalaman da zai fada mata in sun hadu, sai yaune ya samu ya fada, baisan me yasa su Bilal suke kallon shi kamar sunga wani abu a fuskar shi
"Bakomai"
Aisha ta furta a kunyace, Layla zatayi magana Rayyan yaja hannunta sunayin gaba, ta cika surutu, baiga abinda zata fada ba kuma, bayan an gaisa. Tsayawa yayi yana sakinta hadi da fadin
"Tam sai da safe"
Kafin ta amsa ya juya, inda su Bilal suke tsaye ya karasa yana dan matsawa gefe hadi da jiran Bilal din, shima hakan yagani yayi sallama da Aisha din yana samun Rayyan. A hanya suka tsaya sunayin sallar isha'i sannan suka nufi gida. Sai da Rayyan ya tsaya wani shago ya siyi sigari.
"Ba zaka daina sha ba ko Hamma?"
Bilal yai tambayar da wani yanayi a muryar shi, sai da Rayyan ya zari kara daya ya kunna yana zuqa ya fitar da hayakin tukunna yace
"Me yasa kake magana a kai?"
Tunda yasan ba dainawa zaiyi ba, shima ya kamata yabar asarar bakin shi. Ba so ya daina bane bayayi, ko yanzun kamar dole ake mishi haka yake zuqar sigarin, kafin su karasa gida yasha kara hudu, yana shirin daukar ta biyar ne Bilal ya fisge kwalin daga hannun shi yana sakawa a aljihu, Rayyan baice mishi komai ba, haka da suka shiga daki ma baice mishi komai ba. Asalima kan tebir ya zauna ya fara rage tarin assignment din da yake gaban shi, yana kallon Bilal ma yayi nashi kafin ya fara danne-dannen waya da bazai wuce hira yake da Aisha ba.
Nan Bilal yayi bacci yabar shi, kwayoyin shi ya sha ganin Bilal din yayi bacci, amman har karfe uku da rabi ko gyangyadi, sai wajen hudu yadan kwanta, yasan ko da babu sallar asuba, da wahala baccin ya wuce awa daya. Rufe idanuwan shi yayi, baya ganin komai sai hotunan Layla kala-kala a cikin kan shi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 28, 2020
13
"Karya ne"
Yake fadi a duk lokuttan yana kara kai mata wani dukan, sakar mata hannu yayi yana komawa wajen shi ya zauna. Tsaye tayi a wajen tana murza hannunta, shikuma ita yake jira ta zuba mishi, hakan ta kula da shi, bata dauko faranti ba, a dakin ta samu da cokali, sai da ta dauki ruwan leda tana fita wajen dakin ta daurayo su sannan ta dawo
"Kazama, a bakin kofa kika zubar mun da ruwa ko?"
Bata kula shi ba, turo labbanta tayi kawai, sai lokacin ta cire hijabin da yake jikinta tana ajiyewa kan teburin da yake cikin dakin. Bai taba mata maganar kayan da take sakawa ba, amman tasan bayaso, har wata zuciyar na fada mata kishi yake shisa, ba karamin dadi take ji ba kuma. Jacket din shi guda hudune a wajenta yanzun, kuma duk idan ta saka kayan da baisone yake bata. Kamar yana yawo da jacket dinne yanzun ko zai ganta da kayan da bayaso, dan kwanaki a jakar shi ya fito da jacket din. Kuma Rayyan sam bai damu da yawan mutanen da suke waje ba idan ya tashi yi mata abu, kamar ma baya ganin su haka yakeyi.
Abincin ta zuba mishi tana neman waje ta zauna, ya fara ci yaga yanda take bin duk cokalin da zai kai a bakin shi da kallo, kai ya girgiza yana ajiye farantin da ya daga, ya gyara zaman shi sosai
"Me yasa zakiyi girki ba zakici ba?"
Tasan baya tambayeta dan ta bashi amsa bane, shisa tayi shiru, ita batama san tanajin yunwa haka ba sai yanzun da taga yana cin abincin. Cokali ya dauka yana mika mata, zata saka cikin abincin ya dakatar da ita da fadin
"An taba marin ki cikin ido? Ba zaki tashi ki wanko shi ba, kazama kawai"
Mikewa tayi tana daukar sauran ruwan da ta ajiye a gefe ta daurayo cokalin ta dawo. Tare suka cinye abincin tana kara zuba musu wani. Abin bai mata wani iri ba, zuwanta makarantar wannan ne karo na wajen biyar da suke cin abinci tare, na farkon ta kusan raba dare data juya yanayin su tare take hangowa sai wani murmushi ya kwace mata da ba zata ce ga dalilin shi ba. Da yake yana cin abinci da sauri, kafin taci guda daya yaci uku, baisan dalilin da zaisa ka tsaya yanga in zakaci abinci ba. Da kanshi ya dauki kular yana kara mata ya zuba mata miya a kai, abincin da yawa tayi.
Yasan Bilal in dai ba wani abu yaci a wajen Aysha ba, zaici, in baici ba da safe sai su dumama suci abinsu. Layla na karasawa, ruwa kawai ta sha, batama gama ba Rayyan ya mike
"Tashi muje"
Kallon shi tayi da tashin hankali a fuskata
"Ina zamu je? Hamma kabari abinci ya tsarga mun, yanzun fa nagama ci"
Kallon da yayi matane yasata mikewa ta dauki hijabinta tana buga kafarta, duka Rayyan ya kaimata tana kaucewa dan ta gan shi
"Zaki wuce ko saina kwada miki mari?"
Ya bukata, fita tayi daga dakin, shima takalmi ya zira a kafafuwan shi yana fita, baisan ko Bilal ya dauki mukulli ba, shisa ya janyo kofar kawai, gidan su ba'a taba yin sata ba. Kusan ko yaushe Bilal kan yabi halayyar yan gidan. Ko baka rufe daki ba, wani zai janyo maka. Haka sukeyi, in shanya kayi hadari ya hado ma za'a kwashe maka, inka dawo a kawo maka. Suna da kirki matuqa. Shisa bayajin dadin yanda Rayyan yake hade musu girar sama da ta kasa. Shiya fara yin gaba Layla na biye da shi, cikinta take ji har wuya, inda tasan ba zai bari abinci ya natsa mata ba, da bata cika cikinta haka ba.
Ganin har sun kai titi suna tsallakawa yasa ta fadin
"In mukai nisa fa ba zamu sama abin hawa ba"
Dan juyawa Rayyan yayi ya kalleta, hannunta yake shirin kamawa ta kauce
"A kafa? Hamma a kafa? Tafdin... In dai rakani zakayi nagode...amman ni wal..."
Da sauri yace
"Karma ki rantse, zakiyi azumi yarinya... Ki zo mu tafi"
A kafa yake jin tafiya, saboda yana son dan takawa tunda ya cika cikin shi, kuma ko ba haka ba, a ranshi yana jin yin tafiyar tare da ita, ko tana so ko bata so ba matsalar shi bane ba, duk yau ganinta ne yadan nutsar da shi, amman da wani kunci ya wuni, wasu ranakun idan yana azumin yakan ji shi wasai, har Qur'ani yakan dauka ya karanta. Amman wasu ranakun bawai bayaso ya dauka bane, kawai wata irin kasala kan rufe shi duk idan ya yunkura sai ya kasa, haka zai hakura yaita juyi, inya gaji ya kunna sigari ya bukama cikin shi.
"Ni dan Allah kabarni, wallahi nagaji, kuma na saka dogon takalmi"
Layla ta furta tana shirin yin kuka, tun kafin ta fito take murnar zuwa ta gan shi, amman yanzun harya isheta, ta ina zata fara shafawa a kafa ana zaune lafiya. Zagaye suka fara
"Layla..."
Ya furta cike da kashedin da yasata tsayawa waje daya, yasan ko bata zagin shi a ranta, tana tunanin hanyoyin da zata jibge shi idan ta samu dama ne saboda kallon da takeyi mishi, hasken wutar lantarki ya sake ma idanuwanta launi, sai da gabanshi ya fadi daya kalle su, musamman da irin kallon da take watsa mishi, hannunta ya damqa yana janta tana tirjewa kamar karamar yarinya. Bai damu ba, cigaba yayi da janta har suka karasa wani shago, yana rike da hannunta har lokacin ya siya silipas, babu karamar lamba, dan koshi sun mishi yawa, sakinta yayi ya fito dasu daga leda yana ajiye mata
"Ni ce zan saka wannan?"
Ta bukata tana ware mishi ido, kamar duk ranar bataga wani abu daya daga mata hankali irin shi ba, takalman kafafuwan shi dana fata ne yan zire ya cire yana saka silipas din
"Hamma..."
Cikin ido ya kalleta
"Kina gwada hakurina Layla, kin sani ko? Wallahi ba zan sake magana dake ba"
Dogayen takalman kafarta ta cire, ta saka nashin, da kanshi ya kwashe nata ya saka a ledar daya zaro silipas din yana bata, karba tayi ta rike baqar ledar. Hannunta ya sake kamawa suna tafiya. A hankali har suka fara hango makaranta, ba hira sukeyi ba sam balle tace tafiyar tana mata dadi, amman yanayin Rayyan din ya nuna yana cikin nishadi. Musamman yanda ya kalleta yaga tana ta turo baki
"Ki maida hankali, kilan bakin ki ya rigaki zuwa hostel"
Ya furta yana kara sauri, yana kallon yanda take kokarin kamo shi tana kara turo baki, sai da tasa murmushi ya kusan kwace mishi, tunda dai babu yanda zatayi da shi. Har kusan kofar hostel din ya karasa da ita, inda sukaci karo da su Bilal su kuma, Aysha zata rako shi, sunyi tsaye suna hira
"Hamma!"
Ta kwala mishi kira tana murmushi, kallon su Bilal yakeyi da mamaki suna karasowa inda suke, hannun Layla da yake cikin na Rayyan ya kalla, bai amsa Layla ba saboda wani sanannen abu da yaji ya mishi tsaye a makoshi. Kirjin shi harya fara zafin da yakan mishi duk idan ya gansu tare haka
"Ayshan Hamma"
Layla ta fadi tana mata murmushi
"Layla..."
Aisha tace cikin gaisuwa, tana kallon Rayyan
"Ina wuni"
So yakeyi yayi mata murmushi koya ne, amman sam bayajin yi
"Lafiya kalau. Sannu da kokari, mungode"
Ya fadi, yana saka Bilal kallon shi cike da mamaki, Layla ma mamakin takeyi, shi kuma tun rannan yake so yayi mata godiya saboda tana ma Bilal kirki. Tun satin daya wuce yake hada kalaman da zai fada mata in sun hadu, sai yaune ya samu ya fada, baisan me yasa su Bilal suke kallon shi kamar sunga wani abu a fuskar shi
"Bakomai"
Aisha ta furta a kunyace, Layla zatayi magana Rayyan yaja hannunta sunayin gaba, ta cika surutu, baiga abinda zata fada ba kuma, bayan an gaisa. Tsayawa yayi yana sakinta hadi da fadin
"Tam sai da safe"
Kafin ta amsa ya juya, inda su Bilal suke tsaye ya karasa yana dan matsawa gefe hadi da jiran Bilal din, shima hakan yagani yayi sallama da Aisha din yana samun Rayyan. A hanya suka tsaya sunayin sallar isha'i sannan suka nufi gida. Sai da Rayyan ya tsaya wani shago ya siyi sigari.
"Ba zaka daina sha ba ko Hamma?"
Bilal yai tambayar da wani yanayi a muryar shi, sai da Rayyan ya zari kara daya ya kunna yana zuqa ya fitar da hayakin tukunna yace
"Me yasa kake magana a kai?"
Tunda yasan ba dainawa zaiyi ba, shima ya kamata yabar asarar bakin shi. Ba so ya daina bane bayayi, ko yanzun kamar dole ake mishi haka yake zuqar sigarin, kafin su karasa gida yasha kara hudu, yana shirin daukar ta biyar ne Bilal ya fisge kwalin daga hannun shi yana sakawa a aljihu, Rayyan baice mishi komai ba, haka da suka shiga daki ma baice mishi komai ba. Asalima kan tebir ya zauna ya fara rage tarin assignment din da yake gaban shi, yana kallon Bilal ma yayi nashi kafin ya fara danne-dannen waya da bazai wuce hira yake da Aisha ba.
Nan Bilal yayi bacci yabar shi, kwayoyin shi ya sha ganin Bilal din yayi bacci, amman har karfe uku da rabi ko gyangyadi, sai wajen hudu yadan kwanta, yasan ko da babu sallar asuba, da wahala baccin ya wuce awa daya. Rufe idanuwan shi yayi, baya ganin komai sai hotunan Layla kala-kala a cikin kan shi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 28, 2020
13