Sashe 12
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwata-kwata tun ranar daya sauke idanuwan shi kan yarinyar batayi mishi ba, bayason mage, basu da ita a gidan su, akwai a gidan Yaya Ayuba, kuma in dai zai shiga gidan zasu dauke dan ansan tsoron ta yake, a cewar Hajja Mama, matar Baffa kamar yanda suke kiran Yaya Ayuba din, tun yana yaro bayason mage, da ya gani kamar zai shide, shisa bayason Layla, idanuwanta na mishi kama dana jaririn magen gidan Baffa daya gani. Gashi duk inda yayi cikin gidan sai yaga kamar tana bin shine, lokutta da dama Haris ke zuwa yayi sauri yaja hannunta dan kamar shi kadai ya kula da bayason yarinyar na zuwa kusa da shi.
Kuma akan kunnen shi rannan yaji Ayya tace mayya ce, baiyi mamaki ba. Tunda itace mutum ta farko daya taba gani da kalar wannan idanuwan, da gaske mayyar ce, shisa duk inda yabi cikin gidan sai ya ganta. Yar kular abincin ya ajiye a gefe yana karasawa cikin dakin, fensirin ya fara fisgewa daga hannun ta, kafin ya fara kokarin karbar takardar da take rike da ita, bayason yasa karfi ya karba, kamar yanda da dukkan zuciyar shi bayason ko yaya ne jikin shi ya hadu da nata, dan a tsorace yake, kokari yakeyi na ganin bai kalli fuskarta ba
"Saki mana..."
Ya furta, amman sai ta maqale kafada, ran shi bashida wuyar baci
"Mtswww, ki saki nace, ta ina ma kika shigo mana"
Rayyan yake fadi yana sake jan takardar, itama ja tayi ta kuwa rabata gida biyu, cikin tashin hankali Rayyan yake kallon takardar da take hannun shi, kafin ya kalli ta hannun Layla din, wani malolon bakin ciki na mishi tsaye a makoshi, baisan lokacin da ya dauketa da wani irin mari ba, dai-dai shigowar Bilal daya karasa da gudu yana tare hannun Rayyan daya daga zai sake mata wani marin, dayan hannun shi kuma yana ture Layla da ta gigice ko kuka ta kasa saki saboda azaba
"Hamma... Me tayi maka? Baka ga yarinya bace?"
Bilal yake tambaya cikin tashin hankali yana juyawa ya kalli Layla da sai lokacin ta samu ta fashe da wani irin kuka
"Ban sani ba, daka shigo baka ga abinda yake hannunta bane ba? Me yasa zata shigo mana daki?"
Hannunta Bilal ya rike yana rasa ta inda zai fara lallashinta
"Amman ai karama ce, me yasa zaka mareta?"
Bilal ya sake tambaya, dan shi sam baiga dalilin da zaisa duk girman Rayyan ya mari 'yar yarinya kamar Layla ba. Duk da saurin hannun shi akan kowa yake sauka. Ko jiya yayi mishi magana daya mari Shamsu saboda bai gani ba ya diga mishi ruwa. Yan kananan yaran gidan babu mai zuwa kusa dashi, wani lokacin ko wasa sukayi yayi sallama da gudu zakaga kowa na neman wajen boyewa. Wanda suka girmi Rayyan ma shakkar shi sukeyi, ko Khalifa yakan rabe gefe yaba Rayyan hanya, bamai so wani abu ya hadasu sam
"Ka fita da ita, wallahi zan kara dukan ta idan taci gaba da kuka"
Bilal hannun Layla ya kama yana janta suka fice daga dakin. Rayyan din nabin su da wani irin tsaki. Yanajin yanda bai daki wahalar kwanan shi biyu da yayi yana wahala ba sam, da Bilal bai shigo ba ya samu ya jibgeta da ya samu saukin tafasar da ran shi yakeyi yanzun
"Mayya kawai"
Ya furta yana jin wata tsanarta a ran shi, a gefe daya kuma Bilal ne yake ta kokarin lallashin Layla daya samu tayi shiru, sai yatsun Rayyan kwance akan fuskarta. Baisan menene maraici ba, duk da yaji idan Ayya tayi baki wata rana suna maganar yanda shi din maraya ne. Itama kuma yaji ance marainiya ce, haka kawai yake jin tausayin yarinyar. Ko ido suka hada saiya tsinci kan shi dayi mata murmushi. Ko kadan basu da masaniya akan yanda kaddara ta bude musu sabon shafi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 6, 2020
05
*
Kwanakin shi a lissafe suke, yana son makaranta, har kasan ran shi yana son makaranta. Yana kuma son karatu, musamman yanda Allah ya bashi baiwar kwakwalwa, da wahalar gaske ayi abu sau daya a gaban shi bai dauke ba. Kawai abu dayane ya kasa fahimta a shekarun shi goma sha bakwai yanzun a duniya. Duk lokacin da Abbu ko Ayya zasu nuna suna son abu, lokacin zaiji har ranshi babu abinda ya tsana sama da abin, yana so ya bari, yana so yaso abinda suke so ko dan yanda yake ganin halayen shi sun kasa raba zukatan su da tarin kaunar da sukeyi mishi.
Ya wuce Bilal da aji daya, amman zai iya tuna lokuttan da Bilal din yake daukar nashi litattafan ya duba ko an basu wani aiki da baiyi ba dan ya taya shi. Da gangan zai bar takardun shi babu rubutun komai, kawai dan yanda Abbu ya nuna yana bala'in kaunar su da karatu, bawai dan tambayoyin sun gagare shi amsawa ba. Ba a makaranta kawai hakan ya tsaya mishi ba, duk wani lamari na rayuwa da zamantakewar yau da kullum, kar dai Abbu ko Ayya su nuna ga yanda suke so, dan zaiyi abu daban da wannan din ne. Bai fara kawo sakamako mai kyau ba sai da yazo aji hudu a makaranta, ranar da kalaman Abbu suka tunzura shi
"Nasan asarar kudina kawai nakeyi Rayyan, da ka daina zuwa makarantar nan zaifi mun, amman dai zanci gaba da biya dan in nunawa Yaya Ayuba cewa zancena gaskiya ne, babu abinda zaka iya ganewa indai bangaren makaranta ne"
Daga ranar hatta Malaman shi mamaki sukeyi, irin yanda lokaci daya ya canza haka. Har kaguwa yayi lokacin jarabawa yayi dan ya kawowa Abbu, aikam na biyu yazo a ajin nasu lokacin. Da kan shi yazo ya nunawa Abbu, karba yayi batare daya nuna wani jin dadi a fuskar shi ba
"Dan kayi wannan baya nufin za'a dore"
Shine kalaman Abbu, sune kuma kalaman shi a duk lokacin da zai kawo mishi wani abu daya danganci kokarin da yayi a makaranta. Tunda ko hira baya zama suyi, idan hirar shi tayi tsayi da wani to Bilal ne. Yanzun ma makaranta zasu tafi, harya gama shiryawa tsaf, amman Bilal ko wanka bai fito ba. Takalman shi ya dauko yana fitowa bakin kofa ya ajiye, silipas din da yake ajiye ya zira ma kafafuwan shi da nufin ya shiga bangaren Ayya ya dauko musu ruwa. Shi kayan sanyi ba damun shi sukayi ba, bama yaso sam, da an kawo pure water yake zuwa ya sungomo leda daya yazo dakin su ya ajiye. Ya duba ya kare shisa ya fito.
Yana karyo kwana suna cin karo da Layla da tsayin shi bai hana idanuwanta sauka cikin nashi ba
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..."
Ya furta da karfi, zuciyar shi na wani irin dokawa, bayason ganin yarinyar sam, sai yaga kamar mage ce ta gitta mishi, yanzun ma ko ina na jikin shi bari yakeyi, har zuciyar shi.
"Ina kwana"
Ta furta a hankali, duk da tasan ba amsawa zaiyi ba, zuwa yanzun da zata iya hana kanta gaishe da Rayyan ko shiga sabgar shi da ta daina. Amman duk abinda zata shirya ma kanta da ta sauke idanuwanta kan Rayyan din komai yake kwance mata. Kallonta yayi ran shi a bala'in bace
"Dan ubanki ban hanaki zuwa inda nake ba? Mayya ce ke? Sau nawa zan gaya miki idan ina waje ki daina zuwa?"
Rayyan ya furta har lokacin zuciyar shi bata daina dokawa ba. Wasu irin hawayen bakin ciki Layla taji sun taru a cikin idanuwan ta, bashi bane mutum na farko daya kirata da "Mayya" ba, ba kuma shi bane zai zama na karshe, ko Ayya takan fada wasu lokuttan, su kadai ne suke fada a cikin gidan gabaki daya. A waje kuwa da wahalar gaske ka furta kalmar bata fasa maka baki ba, ta karfi da yaji ta zama mafadaciya ta gaske. Kullum saiya mata kashedin zuwa inda yake, amman a haka yake aikenta, a haka yakan sakata aiki, tana iya dawowa daga aiken shi ya hauta da masifar ta daina zuwa inda yake kamar bashi ya kirata ba. Har mamakin shi takeyi, sai kace mai jinnu.
Bata zabi zuwa duniya da kalar idanuwanta ba, asalima idan da an bata zabi zata dauki irin na kowa, bata kuma zabi fitowa daga jikin mahafiyar ta ba, balle a dinga alakanta su da Maita, kalma mafi ciwo a duniyarta gabaki daya.
"Hanya ce, kuma kowa wucewa yakeyi Hamma..."
Layla ta fadi itama nata ran a bace
"Rashin kunya zakiyi mun?"
Rayyan ya bukata yana sata kallon shi da idanuwanta da bayaso, tana kara hautsina mishi lissafi, ita kadai ce ta raina shi haka duk gidan, ita kadai ce take kallon shi kamar bata tsoron shi, take kallon shi kamar shi din bai isa ba
"Idan nace ba rashin kunya nai maka ba zaka yarda ne?"
Tayi tambayar tana sake tsare shi da manyan idanuwanta, kamar da take mishi da mage na kara bayyana, baisan lokacin daya dauketa da wani irin mari ba. Kafin ta wartsake ya kara dora mata wani duk a kunci daya. Ba marin shi bane ba ta saba sha ba, kawai a lokutta irin haka sai ta rantse da Allah a duniya babu wanda ya tsaneta sama da Rayyan, kullum kuma neman dalilin tsanar takeyi ta rasa.
"Matsa daga nan kafin in tattakaki, wawiya kawai"
Rayyan ya karasa maganar da wani irin tsaki, yana saka hannu ya tunkudeta harta kusan faduwa tukunna ya wuce. Gabaki daya ta hargitsa mishi lissafi, da yasan zai ganta, sam ba zai fito ba, ruwan daya hakura saiya dawo makaranta sai ya dauka. Abbu yagani, ran shi a bace yake ko magana bai mishi ba ya raba zai wuce
"Rayyan gaisuwar ma ba zan samu ba kenan yau ko?"
Kuma akan kunnen shi rannan yaji Ayya tace mayya ce, baiyi mamaki ba. Tunda itace mutum ta farko daya taba gani da kalar wannan idanuwan, da gaske mayyar ce, shisa duk inda yabi cikin gidan sai ya ganta. Yar kular abincin ya ajiye a gefe yana karasawa cikin dakin, fensirin ya fara fisgewa daga hannun ta, kafin ya fara kokarin karbar takardar da take rike da ita, bayason yasa karfi ya karba, kamar yanda da dukkan zuciyar shi bayason ko yaya ne jikin shi ya hadu da nata, dan a tsorace yake, kokari yakeyi na ganin bai kalli fuskarta ba
"Saki mana..."
Ya furta, amman sai ta maqale kafada, ran shi bashida wuyar baci
"Mtswww, ki saki nace, ta ina ma kika shigo mana"
Rayyan yake fadi yana sake jan takardar, itama ja tayi ta kuwa rabata gida biyu, cikin tashin hankali Rayyan yake kallon takardar da take hannun shi, kafin ya kalli ta hannun Layla din, wani malolon bakin ciki na mishi tsaye a makoshi, baisan lokacin da ya dauketa da wani irin mari ba, dai-dai shigowar Bilal daya karasa da gudu yana tare hannun Rayyan daya daga zai sake mata wani marin, dayan hannun shi kuma yana ture Layla da ta gigice ko kuka ta kasa saki saboda azaba
"Hamma... Me tayi maka? Baka ga yarinya bace?"
Bilal yake tambaya cikin tashin hankali yana juyawa ya kalli Layla da sai lokacin ta samu ta fashe da wani irin kuka
"Ban sani ba, daka shigo baka ga abinda yake hannunta bane ba? Me yasa zata shigo mana daki?"
Hannunta Bilal ya rike yana rasa ta inda zai fara lallashinta
"Amman ai karama ce, me yasa zaka mareta?"
Bilal ya sake tambaya, dan shi sam baiga dalilin da zaisa duk girman Rayyan ya mari 'yar yarinya kamar Layla ba. Duk da saurin hannun shi akan kowa yake sauka. Ko jiya yayi mishi magana daya mari Shamsu saboda bai gani ba ya diga mishi ruwa. Yan kananan yaran gidan babu mai zuwa kusa dashi, wani lokacin ko wasa sukayi yayi sallama da gudu zakaga kowa na neman wajen boyewa. Wanda suka girmi Rayyan ma shakkar shi sukeyi, ko Khalifa yakan rabe gefe yaba Rayyan hanya, bamai so wani abu ya hadasu sam
"Ka fita da ita, wallahi zan kara dukan ta idan taci gaba da kuka"
Bilal hannun Layla ya kama yana janta suka fice daga dakin. Rayyan din nabin su da wani irin tsaki. Yanajin yanda bai daki wahalar kwanan shi biyu da yayi yana wahala ba sam, da Bilal bai shigo ba ya samu ya jibgeta da ya samu saukin tafasar da ran shi yakeyi yanzun
"Mayya kawai"
Ya furta yana jin wata tsanarta a ran shi, a gefe daya kuma Bilal ne yake ta kokarin lallashin Layla daya samu tayi shiru, sai yatsun Rayyan kwance akan fuskarta. Baisan menene maraici ba, duk da yaji idan Ayya tayi baki wata rana suna maganar yanda shi din maraya ne. Itama kuma yaji ance marainiya ce, haka kawai yake jin tausayin yarinyar. Ko ido suka hada saiya tsinci kan shi dayi mata murmushi. Ko kadan basu da masaniya akan yanda kaddara ta bude musu sabon shafi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 6, 2020
05
*
Kwanakin shi a lissafe suke, yana son makaranta, har kasan ran shi yana son makaranta. Yana kuma son karatu, musamman yanda Allah ya bashi baiwar kwakwalwa, da wahalar gaske ayi abu sau daya a gaban shi bai dauke ba. Kawai abu dayane ya kasa fahimta a shekarun shi goma sha bakwai yanzun a duniya. Duk lokacin da Abbu ko Ayya zasu nuna suna son abu, lokacin zaiji har ranshi babu abinda ya tsana sama da abin, yana so ya bari, yana so yaso abinda suke so ko dan yanda yake ganin halayen shi sun kasa raba zukatan su da tarin kaunar da sukeyi mishi.
Ya wuce Bilal da aji daya, amman zai iya tuna lokuttan da Bilal din yake daukar nashi litattafan ya duba ko an basu wani aiki da baiyi ba dan ya taya shi. Da gangan zai bar takardun shi babu rubutun komai, kawai dan yanda Abbu ya nuna yana bala'in kaunar su da karatu, bawai dan tambayoyin sun gagare shi amsawa ba. Ba a makaranta kawai hakan ya tsaya mishi ba, duk wani lamari na rayuwa da zamantakewar yau da kullum, kar dai Abbu ko Ayya su nuna ga yanda suke so, dan zaiyi abu daban da wannan din ne. Bai fara kawo sakamako mai kyau ba sai da yazo aji hudu a makaranta, ranar da kalaman Abbu suka tunzura shi
"Nasan asarar kudina kawai nakeyi Rayyan, da ka daina zuwa makarantar nan zaifi mun, amman dai zanci gaba da biya dan in nunawa Yaya Ayuba cewa zancena gaskiya ne, babu abinda zaka iya ganewa indai bangaren makaranta ne"
Daga ranar hatta Malaman shi mamaki sukeyi, irin yanda lokaci daya ya canza haka. Har kaguwa yayi lokacin jarabawa yayi dan ya kawowa Abbu, aikam na biyu yazo a ajin nasu lokacin. Da kan shi yazo ya nunawa Abbu, karba yayi batare daya nuna wani jin dadi a fuskar shi ba
"Dan kayi wannan baya nufin za'a dore"
Shine kalaman Abbu, sune kuma kalaman shi a duk lokacin da zai kawo mishi wani abu daya danganci kokarin da yayi a makaranta. Tunda ko hira baya zama suyi, idan hirar shi tayi tsayi da wani to Bilal ne. Yanzun ma makaranta zasu tafi, harya gama shiryawa tsaf, amman Bilal ko wanka bai fito ba. Takalman shi ya dauko yana fitowa bakin kofa ya ajiye, silipas din da yake ajiye ya zira ma kafafuwan shi da nufin ya shiga bangaren Ayya ya dauko musu ruwa. Shi kayan sanyi ba damun shi sukayi ba, bama yaso sam, da an kawo pure water yake zuwa ya sungomo leda daya yazo dakin su ya ajiye. Ya duba ya kare shisa ya fito.
Yana karyo kwana suna cin karo da Layla da tsayin shi bai hana idanuwanta sauka cikin nashi ba
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un..."
Ya furta da karfi, zuciyar shi na wani irin dokawa, bayason ganin yarinyar sam, sai yaga kamar mage ce ta gitta mishi, yanzun ma ko ina na jikin shi bari yakeyi, har zuciyar shi.
"Ina kwana"
Ta furta a hankali, duk da tasan ba amsawa zaiyi ba, zuwa yanzun da zata iya hana kanta gaishe da Rayyan ko shiga sabgar shi da ta daina. Amman duk abinda zata shirya ma kanta da ta sauke idanuwanta kan Rayyan din komai yake kwance mata. Kallonta yayi ran shi a bala'in bace
"Dan ubanki ban hanaki zuwa inda nake ba? Mayya ce ke? Sau nawa zan gaya miki idan ina waje ki daina zuwa?"
Rayyan ya furta har lokacin zuciyar shi bata daina dokawa ba. Wasu irin hawayen bakin ciki Layla taji sun taru a cikin idanuwan ta, bashi bane mutum na farko daya kirata da "Mayya" ba, ba kuma shi bane zai zama na karshe, ko Ayya takan fada wasu lokuttan, su kadai ne suke fada a cikin gidan gabaki daya. A waje kuwa da wahalar gaske ka furta kalmar bata fasa maka baki ba, ta karfi da yaji ta zama mafadaciya ta gaske. Kullum saiya mata kashedin zuwa inda yake, amman a haka yake aikenta, a haka yakan sakata aiki, tana iya dawowa daga aiken shi ya hauta da masifar ta daina zuwa inda yake kamar bashi ya kirata ba. Har mamakin shi takeyi, sai kace mai jinnu.
Bata zabi zuwa duniya da kalar idanuwanta ba, asalima idan da an bata zabi zata dauki irin na kowa, bata kuma zabi fitowa daga jikin mahafiyar ta ba, balle a dinga alakanta su da Maita, kalma mafi ciwo a duniyarta gabaki daya.
"Hanya ce, kuma kowa wucewa yakeyi Hamma..."
Layla ta fadi itama nata ran a bace
"Rashin kunya zakiyi mun?"
Rayyan ya bukata yana sata kallon shi da idanuwanta da bayaso, tana kara hautsina mishi lissafi, ita kadai ce ta raina shi haka duk gidan, ita kadai ce take kallon shi kamar bata tsoron shi, take kallon shi kamar shi din bai isa ba
"Idan nace ba rashin kunya nai maka ba zaka yarda ne?"
Tayi tambayar tana sake tsare shi da manyan idanuwanta, kamar da take mishi da mage na kara bayyana, baisan lokacin daya dauketa da wani irin mari ba. Kafin ta wartsake ya kara dora mata wani duk a kunci daya. Ba marin shi bane ba ta saba sha ba, kawai a lokutta irin haka sai ta rantse da Allah a duniya babu wanda ya tsaneta sama da Rayyan, kullum kuma neman dalilin tsanar takeyi ta rasa.
"Matsa daga nan kafin in tattakaki, wawiya kawai"
Rayyan ya karasa maganar da wani irin tsaki, yana saka hannu ya tunkudeta harta kusan faduwa tukunna ya wuce. Gabaki daya ta hargitsa mishi lissafi, da yasan zai ganta, sam ba zai fito ba, ruwan daya hakura saiya dawo makaranta sai ya dauka. Abbu yagani, ran shi a bace yake ko magana bai mishi ba ya raba zai wuce
"Rayyan gaisuwar ma ba zan samu ba kenan yau ko?"