Sashe 53
Magajin Izzah Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Amma kaddara ta riga fata, tunda shi har da cikin shi a jikinta, *Khatoon* sunan da zuciyar shi ta ambata kenan, ya mike da sauri, ya nufi sama, yau sati Daya kenan, baya ganin wuccewarta. Bude kofar ta yayi ya shiga yaga yadda kome na ciki yayi kura, sannan kamar ance ya kalli dakin yaga alamar an shigo an fita.
Share batun yayi ya koma dakin shi ya zauna, yana nazarin wasu abubuwa, kamar wanda aka tuna mishi ya mike da sauri ya koma d'akinta Littattafan shi ya gani a kasar matashin ta, Janyowa yayi yaga wata farar takarda..ajiyar zuciya yayi sannan ya shiga karantawa.
---
_A yanzun na san nayi nisa da kai! Amma zan tuna maka wani abu da baka sani ba, Jay Ina sonka! Amma zan tafi na Barka! Masarautan ku cike yake da abubuwan damuwa, koda yake bashi bane damuwar rubuta maka wannan sakon tun ranar da ka kawo min Littafan nan nake ta yawan nazarin yadda zan buÉ—e nayi nayi amma na kasa, abin mamaki juya na zauna na gwada sa'ata kayi hakuri zan kira sunan Ammih! Jannart+ Jamal! Ka gajerce sunayen mu gani, idan aka Cire Janjamal_
Jikin shi na rawa ya gwada yaki, shiru yayi, tare da sake duba wasikar! Dariya tayi mishi da
_Hahaha! Nima haka na gwada, akwai wani sunan da su Mamah suke kiran Ammih dashi, wato Janny, muma haka muke kiran Autan Ummi, idan aka gajarce Jan! Aka kawo harafin i aka saka zai bada Jani! Kaga kenan sunan Ammih yafito saura sunan Abba wanda su kuma zasu kasance harafin uku ka na karshen sunan shi Jay Ina matuƙar sanka da wannan nayi lissafin bude Littafin labarin Amminka, amma ban karanta ba. Nagode daga Sakakkiyar matar ka Wacce kayiwa gorin aure._
Wani irin kunya ce ta kama shi, a hankali ya tuna abin da wata tsohuwa ta tab'a gaya mishi a lokacin da zai bar Nijar....
*karike kalmar Janimal zata amfane ka wata rana*
Bude Littafin yayi na farko, ya bude shafin hoton Abban shi lokacin yana matashin sa, hoton baki da fari, a kasar hoton ta rubuta.
*Kawu kenan! Mutumin farko da naso shi a rayuwata ya kuma ce baya sona!*
Bude shafi na biyu yayi hotonta, ya gani, sanye da kayan makarantar ta Rubutu..
*Jannart Jamal Jalaludeen J³ wasu suna kirana da Janny amma nafi son Firdausih dan Kalmar daga bakin Kawuna, Kawun JANNART*
Shafi na gaba ya bude sai ga hoton Sarah, *Aminiyata ce ita Kawata ce ita Dole abin da na haifa yayi biyayya da da'a a gareta. Dan yar uwata ce*
Shafi na hudu hoton Aaryaan ne, ta rubuta a kasar tace. *Yaso ni! Ya kuma kaunace ni, ina umartan abinda na haifa ya girmama al'amarin Aryaan, dan mutum ne da bazan manta dashi ba..
Ita al'amarin kaddarar a cunkushe take da soyayya sadaukarwa, farin ciki bakin ciki, kuka dariya, mugunta hassada kyashi. Rikid'ewa zuwa wata siffa ta cutuwa. Laifina da Kawu babba ne, da yau na fito na gayawa Sara ina son Kawu da bata shiga rayuwar mu ba.
Amma na boye mata bayan so shi bai iya boye kan shi, babu ruwan shi da babba ko yaro, so dangin mutuwa ce, da zaran ta zo maka babu makawa sai. Ta same ka. Daga nan zaka ji yadda kome ya kasance mana, da kuma yadda zaka kawo karshen rikicin masarautan...
A hankali yake bin shafi zuwa shafi. Har zuwa shafin karshe ajiye Littafin yayi, dan tun daga farawa har ya gama, idanun shi basu daina zubda kwalla ba, wani irin yanayi ne haka? Me yasa zuciyarsu take rufewa daga matar da suka dace dasu? Dake labarin bai kare ba, ya bude daya Littafin ya fara karantawa, a wannan ranar Jay yayi kukan da na kasa dainawa ji yaƙe mutuwar Mahaifiyarshi kamar yanzun aka mishi daga karshe inda zata tsaya tace.
_Ban sani ba ko mace ko namiji zan haifa, koma waye don Allah karki / karka wulakanta duk wanda zai ce yana sonki ko yana sonka, Ni nasan ciwon da mutum yake ji idan aka ce ba a son shi, duk wanda zai soka ya gama maka kome a duniya._ tayi nasiha sosai har da misali da rayuwarta, tayi fatan da tana raye taga me ta bari, tayiwa abin da ta bari addu'o'in, sannan ta roke shi da ya nemi ilimi Addinin domin da ita zai yake abin dake faruwa a cikin masarautan, daga haka ta rubuta zan koma mahaifata Maiduguri.
Kifa kan shi yayi a jikin Littafin ya fashe da wani irin kuka, sabida tausayin Mahaifiyarshi, da Aanih, anan ya fahimci zubda jinin da Aanih take yi da, sabida shigar ta rayuwar shine tun farko.
.mik'ewa yayi lokacin da ya fahimci, bata ga gidan. Da sauri ta sauka kasa.
"Kee ina Aanih Fatimah Khatoon take?" Cikin gangancin tace mishi.
"Taje koyar sallama,!"
"Ni zaki gayawa maganar banza!" Ya daka mata tsawa,
"Jay nifa bana son fitina, kaje ka nimo Matarka inda take karka dame ni don Allah."
Da sauri ya fita, zuwa cikin gidan su. Kamar wanda aka wurgo shi ya zuba musu ido, kafin ya wurga musu tambaya.
"Ina Aanih Fatimah Khatoon?" Shiru suka yi suna kallon shi, kafin ya kuma tambayar su.. cikin rashin damuwa Abban shi yace mishi.
"Ba ka saketa ba? Ai tayi komawar ta sokoto!"
A kidime ya zuba musu ido, yana kallon su, bakin shi na rawa yace.
"Yaushe? Ni da hankali na zan sake abin da nake s... Abba Wallahi ban saketa ba!"
"Amma kafara shaye shaye ko?" Inji Abban shi,
"Wallahi ban tab'a sha!" Ya fada musu a raunane, share shi suka yi karamin hauka ne bai yi ba a masarautan, sannan ya nufi gurin Baba Sarki, shi kuma ya mishi fata fata, tare da koran kare.
Haka ya isa cikin gidan gurin kakar shi Umma itace tayi ta rarrashin sa.
.......
Washi gari ko asibiti bai leka ba, ya jajjibi Najim, sai Sokoto. Kasa hakuri yayi ya gayawa Najim abun da aka mishi, aikuwa Najim yace.
"Yau kenan! Ba kai kace zaka sake ta ka huta ba ka tsane ta, tana maka wari ba!"
Sake baki yayi, cikin bakin ciki yace.
"Mara mutunci ashe dama kana sane da abin da aka shirya min algungunmin lauya kawai, kai baka dace da mataimakin shugaban lauyoyi na kasa ba, kafin dacewa da shugaba algunguman Daura baki daya.. mai Najim zai yi ban da dariya. Sabida Baban shi ya tab'a bashi labarin yadda Jamal yake kiran shi da Shugaban munafukai daura. Yau kuma Jay ya kira shi da shugaban algungunman daura. Haka suka isa sokoto Najim yana kara kular da Jay, dan yake bashi labarin wanda zai auri Aanih karshe yaji haushi yace mishi.
"Kai dan ubanka a wani birnin jahilan ake aurar da mace bata yi idda ba? Dan haka babu wanda zai aure..."
"Bayan da kanka ka gaya min babu abinda ya haÉ—a ku! Idan ka samu damar samun ta, baka cire kazamin kishin da ke cinka ba, har abada ba zaka iya amfanan kanka ba balle kuma wanin ka."
Jikin shi ne yayi sanyi, ya kalli Najim sannan yace.
"Hala na gaya maka wasu abubuwan ma ko?"
"A'ah aminin Arziki! Iya k'iyayyar Aanih ce baka iya boye min ba, shima ba k'iyayya bace lalura ce, amma kayi hakuri É—an ba zasu baka ita ka cigaba da mata gori ba" juyawa yayi ya zubawa Najim ido sannan ya sauke ajiyar zuciya yace mishi.
"Na gaya mata magana marasa dad'i ko?"
Domin ya kuma kambama al'amarin yace mishi.
"Ina dad'i ai ta kare maka wallahi.." gaban Jay ne ya fadi cikin tashin hankali yace.
"Kuma Wallahi ina sonta"
"Son banza dai da kaga zaka rasa ba! Ai duk me sonka bazaka wulankata shi ba, balle kuma fatima shi yasa baba sarki yace yayi mata miji!" Inji najim.
"Wallahi zanci Ubanka dan 'iska, a gidan wata uwar za a mata miji wallahi zan kafta maka rashin mutunci, matar yawa shugaban algungunman daura kawai! Idan na gama da su Fulani dan ubanka kai ma sai na maka rashin mutunci, sauke ni na tafi da kafana, mara mutunci na fasa bink"
10/23/20, 10:04 AM - Ummi Tandama: *_Kura da shan bugu! Gardi da amsar kuÉ—i_*
"Toh Yallabai! Zan sauke ka amma kasan dole sai ka biya ni kudin tuka ka da nayi, dan wallahi bani aikin banza!" Inji Najim wanda yake cike da jin daÉ—in ya kular da Jay.
"Sauke Ni nace!" Yadda yayi maganar sai ya baka dariya, haka suka yi ta faÉ—a har suka isa cikin Masarautar Sakkwato, kallon Jay yayi sannan ya kunshe dariyar shi yace mishi.
"Me zaka gayawa Ummin da Baabina?" Shafa kan shi yayi cikin nutsuwa sannan ya juya yana kallon Najim yace.
"Wallahi Malam Lauya ban sani ba! Ga baki daya kome ya tsaya min cak, ji nake kamar nayi ta fasa ihu ko zaku ji yadda nake ji. Ina sonta! Wallahi bazan iya rayuwa babu ita ba, don Allah ka taimaka min kar na rasata." D'aga mishi gira yayi sannan yace mishi.
"Tunda ka iya tafiya babu masu tsaron lafiyar ka, sannan ka tawo niman abin da zuciyarka keso ai ka shiryawa yaki akan ta."
Share batun yayi ya koma dakin shi ya zauna, yana nazarin wasu abubuwa, kamar wanda aka tuna mishi ya mike da sauri ya koma d'akinta Littattafan shi ya gani a kasar matashin ta, Janyowa yayi yaga wata farar takarda..ajiyar zuciya yayi sannan ya shiga karantawa.
---
_A yanzun na san nayi nisa da kai! Amma zan tuna maka wani abu da baka sani ba, Jay Ina sonka! Amma zan tafi na Barka! Masarautan ku cike yake da abubuwan damuwa, koda yake bashi bane damuwar rubuta maka wannan sakon tun ranar da ka kawo min Littafan nan nake ta yawan nazarin yadda zan buÉ—e nayi nayi amma na kasa, abin mamaki juya na zauna na gwada sa'ata kayi hakuri zan kira sunan Ammih! Jannart+ Jamal! Ka gajerce sunayen mu gani, idan aka Cire Janjamal_
Jikin shi na rawa ya gwada yaki, shiru yayi, tare da sake duba wasikar! Dariya tayi mishi da
_Hahaha! Nima haka na gwada, akwai wani sunan da su Mamah suke kiran Ammih dashi, wato Janny, muma haka muke kiran Autan Ummi, idan aka gajarce Jan! Aka kawo harafin i aka saka zai bada Jani! Kaga kenan sunan Ammih yafito saura sunan Abba wanda su kuma zasu kasance harafin uku ka na karshen sunan shi Jay Ina matuƙar sanka da wannan nayi lissafin bude Littafin labarin Amminka, amma ban karanta ba. Nagode daga Sakakkiyar matar ka Wacce kayiwa gorin aure._
Wani irin kunya ce ta kama shi, a hankali ya tuna abin da wata tsohuwa ta tab'a gaya mishi a lokacin da zai bar Nijar....
*karike kalmar Janimal zata amfane ka wata rana*
Bude Littafin yayi na farko, ya bude shafin hoton Abban shi lokacin yana matashin sa, hoton baki da fari, a kasar hoton ta rubuta.
*Kawu kenan! Mutumin farko da naso shi a rayuwata ya kuma ce baya sona!*
Bude shafi na biyu yayi hotonta, ya gani, sanye da kayan makarantar ta Rubutu..
*Jannart Jamal Jalaludeen J³ wasu suna kirana da Janny amma nafi son Firdausih dan Kalmar daga bakin Kawuna, Kawun JANNART*
Shafi na gaba ya bude sai ga hoton Sarah, *Aminiyata ce ita Kawata ce ita Dole abin da na haifa yayi biyayya da da'a a gareta. Dan yar uwata ce*
Shafi na hudu hoton Aaryaan ne, ta rubuta a kasar tace. *Yaso ni! Ya kuma kaunace ni, ina umartan abinda na haifa ya girmama al'amarin Aryaan, dan mutum ne da bazan manta dashi ba..
Ita al'amarin kaddarar a cunkushe take da soyayya sadaukarwa, farin ciki bakin ciki, kuka dariya, mugunta hassada kyashi. Rikid'ewa zuwa wata siffa ta cutuwa. Laifina da Kawu babba ne, da yau na fito na gayawa Sara ina son Kawu da bata shiga rayuwar mu ba.
Amma na boye mata bayan so shi bai iya boye kan shi, babu ruwan shi da babba ko yaro, so dangin mutuwa ce, da zaran ta zo maka babu makawa sai. Ta same ka. Daga nan zaka ji yadda kome ya kasance mana, da kuma yadda zaka kawo karshen rikicin masarautan...
A hankali yake bin shafi zuwa shafi. Har zuwa shafin karshe ajiye Littafin yayi, dan tun daga farawa har ya gama, idanun shi basu daina zubda kwalla ba, wani irin yanayi ne haka? Me yasa zuciyarsu take rufewa daga matar da suka dace dasu? Dake labarin bai kare ba, ya bude daya Littafin ya fara karantawa, a wannan ranar Jay yayi kukan da na kasa dainawa ji yaƙe mutuwar Mahaifiyarshi kamar yanzun aka mishi daga karshe inda zata tsaya tace.
_Ban sani ba ko mace ko namiji zan haifa, koma waye don Allah karki / karka wulakanta duk wanda zai ce yana sonki ko yana sonka, Ni nasan ciwon da mutum yake ji idan aka ce ba a son shi, duk wanda zai soka ya gama maka kome a duniya._ tayi nasiha sosai har da misali da rayuwarta, tayi fatan da tana raye taga me ta bari, tayiwa abin da ta bari addu'o'in, sannan ta roke shi da ya nemi ilimi Addinin domin da ita zai yake abin dake faruwa a cikin masarautan, daga haka ta rubuta zan koma mahaifata Maiduguri.
Kifa kan shi yayi a jikin Littafin ya fashe da wani irin kuka, sabida tausayin Mahaifiyarshi, da Aanih, anan ya fahimci zubda jinin da Aanih take yi da, sabida shigar ta rayuwar shine tun farko.
.mik'ewa yayi lokacin da ya fahimci, bata ga gidan. Da sauri ta sauka kasa.
"Kee ina Aanih Fatimah Khatoon take?" Cikin gangancin tace mishi.
"Taje koyar sallama,!"
"Ni zaki gayawa maganar banza!" Ya daka mata tsawa,
"Jay nifa bana son fitina, kaje ka nimo Matarka inda take karka dame ni don Allah."
Da sauri ya fita, zuwa cikin gidan su. Kamar wanda aka wurgo shi ya zuba musu ido, kafin ya wurga musu tambaya.
"Ina Aanih Fatimah Khatoon?" Shiru suka yi suna kallon shi, kafin ya kuma tambayar su.. cikin rashin damuwa Abban shi yace mishi.
"Ba ka saketa ba? Ai tayi komawar ta sokoto!"
A kidime ya zuba musu ido, yana kallon su, bakin shi na rawa yace.
"Yaushe? Ni da hankali na zan sake abin da nake s... Abba Wallahi ban saketa ba!"
"Amma kafara shaye shaye ko?" Inji Abban shi,
"Wallahi ban tab'a sha!" Ya fada musu a raunane, share shi suka yi karamin hauka ne bai yi ba a masarautan, sannan ya nufi gurin Baba Sarki, shi kuma ya mishi fata fata, tare da koran kare.
Haka ya isa cikin gidan gurin kakar shi Umma itace tayi ta rarrashin sa.
.......
Washi gari ko asibiti bai leka ba, ya jajjibi Najim, sai Sokoto. Kasa hakuri yayi ya gayawa Najim abun da aka mishi, aikuwa Najim yace.
"Yau kenan! Ba kai kace zaka sake ta ka huta ba ka tsane ta, tana maka wari ba!"
Sake baki yayi, cikin bakin ciki yace.
"Mara mutunci ashe dama kana sane da abin da aka shirya min algungunmin lauya kawai, kai baka dace da mataimakin shugaban lauyoyi na kasa ba, kafin dacewa da shugaba algunguman Daura baki daya.. mai Najim zai yi ban da dariya. Sabida Baban shi ya tab'a bashi labarin yadda Jamal yake kiran shi da Shugaban munafukai daura. Yau kuma Jay ya kira shi da shugaban algungunman daura. Haka suka isa sokoto Najim yana kara kular da Jay, dan yake bashi labarin wanda zai auri Aanih karshe yaji haushi yace mishi.
"Kai dan ubanka a wani birnin jahilan ake aurar da mace bata yi idda ba? Dan haka babu wanda zai aure..."
"Bayan da kanka ka gaya min babu abinda ya haÉ—a ku! Idan ka samu damar samun ta, baka cire kazamin kishin da ke cinka ba, har abada ba zaka iya amfanan kanka ba balle kuma wanin ka."
Jikin shi ne yayi sanyi, ya kalli Najim sannan yace.
"Hala na gaya maka wasu abubuwan ma ko?"
"A'ah aminin Arziki! Iya k'iyayyar Aanih ce baka iya boye min ba, shima ba k'iyayya bace lalura ce, amma kayi hakuri É—an ba zasu baka ita ka cigaba da mata gori ba" juyawa yayi ya zubawa Najim ido sannan ya sauke ajiyar zuciya yace mishi.
"Na gaya mata magana marasa dad'i ko?"
Domin ya kuma kambama al'amarin yace mishi.
"Ina dad'i ai ta kare maka wallahi.." gaban Jay ne ya fadi cikin tashin hankali yace.
"Kuma Wallahi ina sonta"
"Son banza dai da kaga zaka rasa ba! Ai duk me sonka bazaka wulankata shi ba, balle kuma fatima shi yasa baba sarki yace yayi mata miji!" Inji najim.
"Wallahi zanci Ubanka dan 'iska, a gidan wata uwar za a mata miji wallahi zan kafta maka rashin mutunci, matar yawa shugaban algungunman daura kawai! Idan na gama da su Fulani dan ubanka kai ma sai na maka rashin mutunci, sauke ni na tafi da kafana, mara mutunci na fasa bink"
10/23/20, 10:04 AM - Ummi Tandama: *_Kura da shan bugu! Gardi da amsar kuÉ—i_*
"Toh Yallabai! Zan sauke ka amma kasan dole sai ka biya ni kudin tuka ka da nayi, dan wallahi bani aikin banza!" Inji Najim wanda yake cike da jin daÉ—in ya kular da Jay.
"Sauke Ni nace!" Yadda yayi maganar sai ya baka dariya, haka suka yi ta faÉ—a har suka isa cikin Masarautar Sakkwato, kallon Jay yayi sannan ya kunshe dariyar shi yace mishi.
"Me zaka gayawa Ummin da Baabina?" Shafa kan shi yayi cikin nutsuwa sannan ya juya yana kallon Najim yace.
"Wallahi Malam Lauya ban sani ba! Ga baki daya kome ya tsaya min cak, ji nake kamar nayi ta fasa ihu ko zaku ji yadda nake ji. Ina sonta! Wallahi bazan iya rayuwa babu ita ba, don Allah ka taimaka min kar na rasata." D'aga mishi gira yayi sannan yace mishi.
"Tunda ka iya tafiya babu masu tsaron lafiyar ka, sannan ka tawo niman abin da zuciyarka keso ai ka shiryawa yaki akan ta."