Sashe 20
Magajin Izzah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
     "Yallabai da abinda za a taimaka maka ne?!" A hankali ya bude shanyayyun idanun shi akan matar ya girgiza mata kai! Tare da juya kan shi yana kallon tagar jirgin.
        A iya sanin shi bai tab'a kusantar matsala irin ta kwanakin nan, Aanih ta haifa masa da damuwa, gani yake jirgin ma bata sauri.
     A hankali barci yayi gaba dashi. Cikin abibds bai fi minti biyar ba, sai gashi yana jin shashekar kukanta, a hankali take kusanto shi, har ya iso dab dashi.
"Ina sonka Jay!" Bude idanu yayi cikin sauri. Tare da dafe goshin sa.
    Suna tafiya har dare yayi, a lokacin ya mike tare da nufar wasu musulmai suka gabatar da sallah. Bayan sun idar ya dawo mazaunin shi. Jikin shi na kuma sanyi.
    ----
"Mamahna! Amshi abincin mana!"
    A sannu na bude bakina ya saka min! Ina taunawa hawaye na zuba min, kallon shi nayi ina hango juriya da jarumta mahaifina, karb'an kwanon nayi tare da gyara gashina na fara ci, hannu baka hannu kwarya.
        Rike hannuna yayi tare da ce min.
"Ki nutsu! Don Allah kin ji."
  Kallon shi nayi tare da kai abincin bakina, a nutse?
"Yace baya sona! Baya kaunata! Kuma Baabina, ina son shi. Baabina me yasa kaddarata tazo a hade da nashi bayan bazan iya jurewa ba, me yasa halayyar shi suka bambanta da sauran Mazan?
.... Baabi kirjina kamar ta fashe! Baabina! Me yasa ka ajiye sarautar ka?!"
   Murmushi yayi, sannan ya shiga bani abincin kauda kai nayi tare da mik'ewa. Na nufi tagar dakin ina kallon yadda garin yake.
"Ban san Mahaifiyata ba? Kamar yadda shima bai san Mahaifiyar shi ba!
    Mun rayu a mabanbanta duniyoyi! Sai dai nasan bazai tab'a kaunata ba."
  "Inji waye? Ai tuni ya kaunace ki? Tuni yaso ki? Ki bani aron lokaci idan bai dawo ba, ni da kaina zan dawo kawo.."
     "Rahil! Ki bar maganar Jalal, Ni na miki miji!" Juyowa nai a firgice tare da rike kirjina, na fashe da wata irin kuka, ina me durkusawa a gurin, da gwiwata dukka biyu. Jan hannun ta yayi suka fita basu kuma bin ta kaina ba. Anan nayi kuma har na godewa Allah da ya halicce ni.
        Kamar wacce aka yiwa fada na had'iye kukan tare da yin alqawarin idan Son Jay itace ajalina gwara na mutu na huta da bakin cikin rayuwa.
    ---
Daura...
Tunda suka isa Mamah Sarah take kuka, kamar ranta zai fito. Janny ta shiga a hankali, tana me kallonta tare da Raihah sai Rumah.
    Tsayawa suka yi daga bakin kofar, suna share kwalla, ganin yadda mahaifiyar su take zubda kwalla, haka ya kashe musu jiki musamman Rumah da taki komawa gidan Mijinta! Khalid dan gidan Mamah Raihanah, shekara daya kenan da auren tazo daga Kaduna.
 Dake anan suke da zama, a hankali Janny ta karasa kusa da ita, ta fara zare mata takalmin kafarta, tare da matsa mata kafar.
     "Ita rayuwa tana bamu damar fuskantar matsalolin mu, bawai mu kasance cikin damuwa da rashin nutsuwa bane! Da matukar wahala, a fahimci banbancin Ra'ayin tare da juyewar wata dab'ia, amma a yadda tsarin zanen kaddarar take.
  Dole sai anyi rashi kuma anyi samu, haka ce zata damawa zukatar wasu mutanen adalci, Mama karki tilas zuciyar ki! D'anki zai dawo gare ki!"
     Shi yasa take masifar kaunar Yarinyar domin gani take kamar Jannynta ce ta kuma dawo mata, hakuri kawaici zurfin ciki. Duk ta gado me sunanta.
      ---
"Abba! Ba zai tab'a yarda ya biyo mu ba! Sannan kuma bazai tab'a amincewa da bukatar mu ba, A wannan lokaci nake bukatar shi, amma bazai tab'a zama damu ba,
    Asalima abinda muke kokarin yi kamar tursasawa ce, shi da kan shi, zai biyo sawun mu."
   Murmushi Abban Jaamal yayi tare da kallon shi wato hali a jikin rai tace.
"Hmm! Mahaukaciyar Kasuwa! Sa gabanki inda kike dosa, itama Kuma Faɗimah fa? Ko ba zaka bata wata tukwaicin kaunar da ta nuna maka bane? Ko da yake! A tambayi kalwa zaƙin miya, a tambayi barkono a sha labari. Ba wani sabon abu bane, domin kuwa idan muka duba."
  Sunkuyar da kai Kawu yayi cikin nutsuwa ya shafa kan shi sannan yace.
"Abba kenan! Karka min. An yi min sagegeduwa, halin Jalal ya sha kaina, ni ban tab'a."
  "Amma wa. Dodo ɗaya ake yiwa tsafi. Idan shi bai tab'a kawowa kai ne ka haife shi ba, amma shi ya nunawa duniya abinda kayiwa Jannart! Ya nuna halin. Kaje ka sami Magaji duk yadda kuka yi ka same ni, amma bazan iya barin jini na a wata duniya domin yace bai samun ba."
       Ajiyar zuciya Kawu ya sauke tare da cewa.
"Toh Abba!"
  Tashi yayi tare da mishi sai da an jima.
      ----
Karfe shida na safe!
Ya sauka a garin Calgary! Cike da son sanin abubuwan da suka boya daga ganin shi.
. Kallon Asood da Hikmi yayi, tare da mika musu hannu suka gaisa.
"Ya kome ya tafi yadda ya dace? Ka same ta?!"
Shiga yayi Bayan motar su ya kwantar da kan shi a jikin kujerar, tare da lumshe idanun shi.
Ya kasa fahimtar kome akan kan shi, amma yana jinjina qarfin shigar da shi da Fatimah tayi.
"Jay! Kayi mana shiru? Jay ko baka same ta bane?!" Inji Asood,
Ajiyar zuciya ya shiga saukewa sabida yadda.yake jin ya barta kenan, ba ita ba hatta mutanen da suka gabatar da kan su a gare shi!! Yana jin kowacce motsin da zai yi da mutane biyun nan yake motsawa.
Sarkin Daura! Sai Ummin Fatimah! Yana jinta a ran shi sosai, sama da yadda yake jin mai martaba sarkin Daura!
"Amma kai wallahi anyi d'an iska! Ka mana bayani kayi shiru sai share mu kake!" Bude idanu yayi shanye da toka, kamar bazai magana ba yace.
"Ka dame Ni!"
Kura mishi ido Asood yayi tare da gyara zaman shi bai kuma ce mishi kala ba, asalima tsoron kuma mishi magana yayi.
Har suka iso Unguwar su Jay! Ya fita a hankali daga cikin motar, ya kura musu ido.
"Don Allah ku kyale Ni!"
Daga haka ya shige gidan su, bayan tafiyar Jay! Asood ya kalle Hikmi.
"Hiky me kake ganin ya faru? Jay Ya sauya daga yadda yake a baya, ko dai ya fara soyayya da Aanih ce?!"
."toh laifi ne? Dan ya fara soyayya da ita? Ni ban ga kome ba, sai tashin hankali da dimauta da take cikin ƙwayar idanu shi! Sai tsantsar damuwa da take cikin ƙwayar idanun shi! Yana cikin matsala sosai! Dan haka mu barshi na wasu lokuta kafin ya samu nutsuwa."
"Toh ko yayi mata fyade ne?!" Juyawa Hiky yayi cikin mamaki!
"Me yasa kake danganta shi da aikata hakan? Abokin mu ne! Sannan dan kai kana ganin kana aikata laifuka bai zama dole ni dashi mu aikata abin da kake zargi ba."
Cizon bakin shi yayi tare da rintsa idanun shi, tun ranar da Aanih ta mare shi, yake niman mafita da zai rama, amma bai samu ba, shi yasa ya d'aura Jay akan yaje ya mata fyade.
Idan kuma bai mata ba, tabbatacciya ce shi zai mata hakan koda kuwa akan mutuwar shi ce.
....
"Assalamu alaikum warahmatullah!" Kallon shi suka yi cike da mamaki.
"Jayyyyy! Zo nan."
A hankali yake cire kafar shi, har ya isa gaban su.
"Ya mutanen gidan?!"
"Ya Jay! Zauna mana!" Inji Munih.
"Yarona zauna mana!" Kura musu ido yayi kawai ya nufi sama abin shi, yana shiga ya rufe dakin shi, tare da sulalewa ya zauna.
Abinda ya dawo kan shi, shine kamar shi da Sarkin Daura, babu kamar da yake da Baban shi na nan Canada, amma me yasa suka mishi haka?
Waye shi? Me yasa suka raba shi da dangin shi! Me yasa suka sami damar nisanta shi da ahalin shi.
Shi yasa yake jin cewa, akwai abinda ake boye mishi, musamman idan Kaka tana mishi kallon bai cika ba? Ashe itama bata amshe shi a matsayin jikarta bane.
Shi yasa Munih take son sakar mishi jiki dan tasan babu wata alaƙa a tsakanin su! Lumshe idanunshi yayi tare da kwanciya a kasar dakin shi.
Me yasa shi kaddarar shi tazo mishi a kaikace!? Me yasa kome ya lalace mishi lokaci guda? Taya Haka ta faru ba tare da ya fahimci cewa shi din d'an wasu ne?....
#Mai_Dambu
10/23/20, 9:53 AM - Ummi Tandama: MAGAJIN IZZAH!!!
  {CIGABA KWARKWARAH}
  *HAZAKA WRITER'S ASSO*
(HWA)
*Ban yarda wani ko wata ta juya min koda Harafi daya ne na Labarin! Ko kuma a samun wani kafar Sadarwa! Yin haka zai sanya wani ya fuskanci b'acin rai!*
Mallakin
 Mai_Dambu
Sadaukarwa ta gare ki bazata kare ba! Mab'allin zuciyata! Zahran Addah Ramla☺ï¸
SHA SHIDA.
Dafe goshin sa yayi tare da fadin.
"Nayi hauka!" Ya kuma mik'ewa daga kwancen ya shiga ban daki, cika ruwa yayi a cikin abin wankar ya shiga ciki.
  Ya kwanta ruwa na ratsa shi, kamar yadda yake takura Ƙwaƙwalwar shi da zurfaffa tunanin halin da yake ciki. Ya jima a cikin ruwan kafin ya cud'e jikin shi ya fito. Yana shiga dakin shi yayi arba da Munih.
 Kauda kan shi yayi kamar baya Dakin, takowa tayi har gaban shi ta mika mishi madara mai zafi tayi tana kallon hadaddiyar surar jikin shi, wanda yake cike dam da gashi, sun kwanta luf luf.
        A iya sanin shi bai tab'a kusantar matsala irin ta kwanakin nan, Aanih ta haifa masa da damuwa, gani yake jirgin ma bata sauri.
     A hankali barci yayi gaba dashi. Cikin abibds bai fi minti biyar ba, sai gashi yana jin shashekar kukanta, a hankali take kusanto shi, har ya iso dab dashi.
"Ina sonka Jay!" Bude idanu yayi cikin sauri. Tare da dafe goshin sa.
    Suna tafiya har dare yayi, a lokacin ya mike tare da nufar wasu musulmai suka gabatar da sallah. Bayan sun idar ya dawo mazaunin shi. Jikin shi na kuma sanyi.
    ----
"Mamahna! Amshi abincin mana!"
    A sannu na bude bakina ya saka min! Ina taunawa hawaye na zuba min, kallon shi nayi ina hango juriya da jarumta mahaifina, karb'an kwanon nayi tare da gyara gashina na fara ci, hannu baka hannu kwarya.
        Rike hannuna yayi tare da ce min.
"Ki nutsu! Don Allah kin ji."
  Kallon shi nayi tare da kai abincin bakina, a nutse?
"Yace baya sona! Baya kaunata! Kuma Baabina, ina son shi. Baabina me yasa kaddarata tazo a hade da nashi bayan bazan iya jurewa ba, me yasa halayyar shi suka bambanta da sauran Mazan?
.... Baabi kirjina kamar ta fashe! Baabina! Me yasa ka ajiye sarautar ka?!"
   Murmushi yayi, sannan ya shiga bani abincin kauda kai nayi tare da mik'ewa. Na nufi tagar dakin ina kallon yadda garin yake.
"Ban san Mahaifiyata ba? Kamar yadda shima bai san Mahaifiyar shi ba!
    Mun rayu a mabanbanta duniyoyi! Sai dai nasan bazai tab'a kaunata ba."
  "Inji waye? Ai tuni ya kaunace ki? Tuni yaso ki? Ki bani aron lokaci idan bai dawo ba, ni da kaina zan dawo kawo.."
     "Rahil! Ki bar maganar Jalal, Ni na miki miji!" Juyowa nai a firgice tare da rike kirjina, na fashe da wata irin kuka, ina me durkusawa a gurin, da gwiwata dukka biyu. Jan hannun ta yayi suka fita basu kuma bin ta kaina ba. Anan nayi kuma har na godewa Allah da ya halicce ni.
        Kamar wacce aka yiwa fada na had'iye kukan tare da yin alqawarin idan Son Jay itace ajalina gwara na mutu na huta da bakin cikin rayuwa.
    ---
Daura...
Tunda suka isa Mamah Sarah take kuka, kamar ranta zai fito. Janny ta shiga a hankali, tana me kallonta tare da Raihah sai Rumah.
    Tsayawa suka yi daga bakin kofar, suna share kwalla, ganin yadda mahaifiyar su take zubda kwalla, haka ya kashe musu jiki musamman Rumah da taki komawa gidan Mijinta! Khalid dan gidan Mamah Raihanah, shekara daya kenan da auren tazo daga Kaduna.
 Dake anan suke da zama, a hankali Janny ta karasa kusa da ita, ta fara zare mata takalmin kafarta, tare da matsa mata kafar.
     "Ita rayuwa tana bamu damar fuskantar matsalolin mu, bawai mu kasance cikin damuwa da rashin nutsuwa bane! Da matukar wahala, a fahimci banbancin Ra'ayin tare da juyewar wata dab'ia, amma a yadda tsarin zanen kaddarar take.
  Dole sai anyi rashi kuma anyi samu, haka ce zata damawa zukatar wasu mutanen adalci, Mama karki tilas zuciyar ki! D'anki zai dawo gare ki!"
     Shi yasa take masifar kaunar Yarinyar domin gani take kamar Jannynta ce ta kuma dawo mata, hakuri kawaici zurfin ciki. Duk ta gado me sunanta.
      ---
"Abba! Ba zai tab'a yarda ya biyo mu ba! Sannan kuma bazai tab'a amincewa da bukatar mu ba, A wannan lokaci nake bukatar shi, amma bazai tab'a zama damu ba,
    Asalima abinda muke kokarin yi kamar tursasawa ce, shi da kan shi, zai biyo sawun mu."
   Murmushi Abban Jaamal yayi tare da kallon shi wato hali a jikin rai tace.
"Hmm! Mahaukaciyar Kasuwa! Sa gabanki inda kike dosa, itama Kuma Faɗimah fa? Ko ba zaka bata wata tukwaicin kaunar da ta nuna maka bane? Ko da yake! A tambayi kalwa zaƙin miya, a tambayi barkono a sha labari. Ba wani sabon abu bane, domin kuwa idan muka duba."
  Sunkuyar da kai Kawu yayi cikin nutsuwa ya shafa kan shi sannan yace.
"Abba kenan! Karka min. An yi min sagegeduwa, halin Jalal ya sha kaina, ni ban tab'a."
  "Amma wa. Dodo ɗaya ake yiwa tsafi. Idan shi bai tab'a kawowa kai ne ka haife shi ba, amma shi ya nunawa duniya abinda kayiwa Jannart! Ya nuna halin. Kaje ka sami Magaji duk yadda kuka yi ka same ni, amma bazan iya barin jini na a wata duniya domin yace bai samun ba."
       Ajiyar zuciya Kawu ya sauke tare da cewa.
"Toh Abba!"
  Tashi yayi tare da mishi sai da an jima.
      ----
Karfe shida na safe!
Ya sauka a garin Calgary! Cike da son sanin abubuwan da suka boya daga ganin shi.
. Kallon Asood da Hikmi yayi, tare da mika musu hannu suka gaisa.
"Ya kome ya tafi yadda ya dace? Ka same ta?!"
Shiga yayi Bayan motar su ya kwantar da kan shi a jikin kujerar, tare da lumshe idanun shi.
Ya kasa fahimtar kome akan kan shi, amma yana jinjina qarfin shigar da shi da Fatimah tayi.
"Jay! Kayi mana shiru? Jay ko baka same ta bane?!" Inji Asood,
Ajiyar zuciya ya shiga saukewa sabida yadda.yake jin ya barta kenan, ba ita ba hatta mutanen da suka gabatar da kan su a gare shi!! Yana jin kowacce motsin da zai yi da mutane biyun nan yake motsawa.
Sarkin Daura! Sai Ummin Fatimah! Yana jinta a ran shi sosai, sama da yadda yake jin mai martaba sarkin Daura!
"Amma kai wallahi anyi d'an iska! Ka mana bayani kayi shiru sai share mu kake!" Bude idanu yayi shanye da toka, kamar bazai magana ba yace.
"Ka dame Ni!"
Kura mishi ido Asood yayi tare da gyara zaman shi bai kuma ce mishi kala ba, asalima tsoron kuma mishi magana yayi.
Har suka iso Unguwar su Jay! Ya fita a hankali daga cikin motar, ya kura musu ido.
"Don Allah ku kyale Ni!"
Daga haka ya shige gidan su, bayan tafiyar Jay! Asood ya kalle Hikmi.
"Hiky me kake ganin ya faru? Jay Ya sauya daga yadda yake a baya, ko dai ya fara soyayya da Aanih ce?!"
."toh laifi ne? Dan ya fara soyayya da ita? Ni ban ga kome ba, sai tashin hankali da dimauta da take cikin ƙwayar idanu shi! Sai tsantsar damuwa da take cikin ƙwayar idanun shi! Yana cikin matsala sosai! Dan haka mu barshi na wasu lokuta kafin ya samu nutsuwa."
"Toh ko yayi mata fyade ne?!" Juyawa Hiky yayi cikin mamaki!
"Me yasa kake danganta shi da aikata hakan? Abokin mu ne! Sannan dan kai kana ganin kana aikata laifuka bai zama dole ni dashi mu aikata abin da kake zargi ba."
Cizon bakin shi yayi tare da rintsa idanun shi, tun ranar da Aanih ta mare shi, yake niman mafita da zai rama, amma bai samu ba, shi yasa ya d'aura Jay akan yaje ya mata fyade.
Idan kuma bai mata ba, tabbatacciya ce shi zai mata hakan koda kuwa akan mutuwar shi ce.
....
"Assalamu alaikum warahmatullah!" Kallon shi suka yi cike da mamaki.
"Jayyyyy! Zo nan."
A hankali yake cire kafar shi, har ya isa gaban su.
"Ya mutanen gidan?!"
"Ya Jay! Zauna mana!" Inji Munih.
"Yarona zauna mana!" Kura musu ido yayi kawai ya nufi sama abin shi, yana shiga ya rufe dakin shi, tare da sulalewa ya zauna.
Abinda ya dawo kan shi, shine kamar shi da Sarkin Daura, babu kamar da yake da Baban shi na nan Canada, amma me yasa suka mishi haka?
Waye shi? Me yasa suka raba shi da dangin shi! Me yasa suka sami damar nisanta shi da ahalin shi.
Shi yasa yake jin cewa, akwai abinda ake boye mishi, musamman idan Kaka tana mishi kallon bai cika ba? Ashe itama bata amshe shi a matsayin jikarta bane.
Shi yasa Munih take son sakar mishi jiki dan tasan babu wata alaƙa a tsakanin su! Lumshe idanunshi yayi tare da kwanciya a kasar dakin shi.
Me yasa shi kaddarar shi tazo mishi a kaikace!? Me yasa kome ya lalace mishi lokaci guda? Taya Haka ta faru ba tare da ya fahimci cewa shi din d'an wasu ne?....
#Mai_Dambu
10/23/20, 9:53 AM - Ummi Tandama: MAGAJIN IZZAH!!!
  {CIGABA KWARKWARAH}
  *HAZAKA WRITER'S ASSO*
(HWA)
*Ban yarda wani ko wata ta juya min koda Harafi daya ne na Labarin! Ko kuma a samun wani kafar Sadarwa! Yin haka zai sanya wani ya fuskanci b'acin rai!*
Mallakin
 Mai_Dambu
Sadaukarwa ta gare ki bazata kare ba! Mab'allin zuciyata! Zahran Addah Ramla☺ï¸
SHA SHIDA.
Dafe goshin sa yayi tare da fadin.
"Nayi hauka!" Ya kuma mik'ewa daga kwancen ya shiga ban daki, cika ruwa yayi a cikin abin wankar ya shiga ciki.
  Ya kwanta ruwa na ratsa shi, kamar yadda yake takura Ƙwaƙwalwar shi da zurfaffa tunanin halin da yake ciki. Ya jima a cikin ruwan kafin ya cud'e jikin shi ya fito. Yana shiga dakin shi yayi arba da Munih.
 Kauda kan shi yayi kamar baya Dakin, takowa tayi har gaban shi ta mika mishi madara mai zafi tayi tana kallon hadaddiyar surar jikin shi, wanda yake cike dam da gashi, sun kwanta luf luf.