Sashe 33
Magajin Izzah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai bayan da Sidi AbdulKadir ya zama sarkin Zazzau, an yi ta samun kwamacala da rigingimu, tun da abin ya zama gado kowa ma dan gida yana ganin ya cancanci rike sarautar. Daga nan aka fara samun rashin yarda da juna, har aka kai kara Sakkwato, aka dakatar da Sarkin Zazzau Sidi AbdulKadir daga sarauta. Shi kuma ya ce, duk zargin da ake masa na sarautar ba shi kadai yake sarautar ba. Tare da shawarar dukkan ’yan majalisarsa ake yi, wato su masu son a ba su sarautar nan. Saboda haka, ba wanda ya cancanta a cikinsu, kamar yadda shi ma bai cancanta ba.
Saboda haka, sai sarkin musulmi na wancan lokaci ya ga ya fi dacewa a dauko wani malami cikin daliban Shehu Danfodiyo a ba shi jagoranci, duk da ya manyanta a wannan lokaci. Kuma lokacin ya yi tsawo, Malam Musa ya yi shekaru goma sha, Yamusa ya yi shekaru goma sha, AbdulKarim ya yi shekaru goma sha, Hammada ya yi ’yan kwanaki, Mamman Sani ya yi shekaru, Sidi AbdulKadir ya yi wata takwas zuwa goma a gadon sarauta. To, idan ka tara wadannan shekaru, ka ga an dumfari shekaru arba’in.
To, shi Malam AbdulSalam idan ka dora shekara arba’in a kan shekarunsa, ka ga ya manyanta. Amma sai sarkin musulmi na wancan lokaci ya ce a ba AbdulSalami sarautar Zazzau ya rike. Da haka ya zama raba-gardama. Ba a ba kowa ba daga cikin ‘ya’yan wadancan sarakuna. Wannan kuma shi ne dalilin zuwan gida na hudu a sarautar Zazzau kenan, wato don a sami natsuwa.                                                                                                      Â
Ta haka ne aka sami wadannan khalifofi guda hudu, kuma kowannensu an ba shi sarauta ne a matsayin kansa na masanin addinin musulunci, na mai biyayya da gaskata abin da jihadin Shehu Usman Danfodiyo ya kawo bisa koyarwa Alkur’ani da Sunnar Manzon Allah (SAW).
Tarihin Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Dokta Shehu Idris
Haihuwa da Tsatson Sarki
Mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Dokta Shehu Idris, an haife shi ne a watan Maris na shekarar 1936. Wanda ya haife shi ne Mai Unguwa Auta. Sunan na Auta aka fi sani, amma sunansa na Littafi shi ne Idrisu. Shi da ne, dan autan Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Sambo.
Shi kuma Sarki Muhamadu Sambo da ne, kuma na biyu a cikin ‘ya’yan Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim. Shi kuma Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim shi ne na farko a daular Fulani karkashin jaddada addinin musulunci da Shehu Usumanu Danfodiyo ya yi a kasar Zazzau, kuma shi ne ya assasa gidan Katsinawa a sarautar Zazzau.
Ina Sarki ya taso?
Shi Mai martaba Sarki lokacin mahaifinsu yana Mai Unguwa a unguwar Iya a nan aka haife shi. Unguwar Iya wata unguwa ce da ke tsakanin unguwar Durumi da Kuyanbana. A nan ya girma, ya shekara akalla bakwai, inda har ya shiga makarantar allo, ya fara karatun addini.
A nan dai unguwar Iya ya yi makarantar farko da Bature ya gina a cikin birnin Zariya, wadda ake kira ‘Town School one�, ita ce kuma makaranatar ‘Kofar Kuyanbana Local Government Education Primary School�. Yanzu ana ce mata ‘Waziri Lawal Local Government Education Primary School�, a nan ya fara karatu.
Bayan ya gama sai ya tafi Alhudahuda College, lokacin ana kiran makarantar da sunan ‘Middle School�. Daga nan aka yi masa sauyi, ya koma makarantar koyar da malunta a Katsina lokacin ana kiran ta ‘Katsina Teachers� College�.To, a nan ya koyi aikin koyarwa, wanda shi ne babbar sana’arsa ta farko da ya iya.
Daga baya mai martaba ya sauya daga malamin makaranta ya shiga aikin mulki, wanda har ya je kasar Ostireliya (Australia). Yana cikin daliban farko da ofishin jakadancin Ostireliya suka dauki dawainiyarsu suka je suka yi karatu na koyon ilimin mulki a kasar ta Osireliya
Wuraren da ya yi aiki
Daga shekarar 1956 ya koyar a wurare daban-daban a cikin garin Zariya da kauyuka. Ya koyar a Zangon Aya, ya koyar a Paki, har ya yi hedimasta a Pakin. Ya kuma yi hedimasta a Hancin Kare a makarantar ‘Town School No.3’�.
A shekarar 1962 ya koma aikin mulki, lokacin da ya koma karkashin hukumar ‘NA� (Native Authority) ta Zariya a zamanin Sarkin Zazzau Aminu. Inda ya gwama aiki biyu, wato yana aiki a hukumar ‘NA�, kuma yana aiki a matsayin jami’in sadarwa na hukumar kula da kananan hukumomi da masarautu na jihar Arewa.
Daga baya Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu ya ba shi mukamin Babban sarakatare na musamman na sarki. Daga nan ne sai aka nada shi sarauta, ya zama wakilin ofis, wato mai daukar nauyin duk abin da ya shafi aikin masarauta a karkashin ‘Native Authorityâ€? a wannan lokacin.                              Â
Ya rike wannan mukami na tsawon kamar shekara biyu zuwa uku, sai Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu ya nada shi hakimin birni da kewaye, mukamin da ya rike na tsawon shekara biyu zuwa uku, yana hakimi. Kuma Dan Madamin Zazzau.
A shekarar 1975 likafarsa ta yi gaba, aka ba shi a sarautar Sarkin Zazzau.
Sauyin da ya kawo a sarautar Zazzau cikin shekaru arba’in da biyar yana mulki
Makusantan Sarkin suna ganin ba wani al’amari da ya shafi rayuwar Zage-zagi a birnin Zariya ko a masarautar Zazzau ne da ba a sami ci gaba ba. Ta fuskar ilimi, tun daga kananan makarantun firamare zuwa sakandire, zuwa na gaba da sakandire, zuwa jami’o’i, makarantun sojoji da sauransu da aka yi a masarautarsa, akalla ba za a rasa makarantu ashirin ba.
Iyalin Sarki
Allah Ya albarkaci mai martaba Sarkin Zazzau Alhaji Dokta Shehu Idris da iyali masu yawa. Yana da mata hudu, da ‘ya’ya maza da mata da yawansu ba zai gaza arba’in da biyu ko da biyar ba.
Dabi’u da halayen Sarki
Daya daga cikin hakiman masarautar Zazzau, Salanken Zazzau, Dokta Muhammadu Bello AbdulKadir, ya ce, babbar baiwar da Allah Ya yi wa mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Shehu Idris, shi ne hakuri, yana da hakuri matuka.
Ga shi kuma yana da kawaici, wanda a sakamakon haka ne ya kai kusan shekara ashirin yana sarauta, amma bai nada kowa daga cikin ‘ya’yansa sarauta ba, saboda kawaici. Sai da dattawa suka matsa masa, cewa idan bai nada ‘ya’yansa a sarauta ba, wa zai nada masa su.
Hakurinsa da dauriya suka sa Zazzau ta zama kowa ya zo karbabbe ne, zai zo ya sami karbuwa wajen al’umma ya yi kasuwanci, ko ya nemi ilimi, ko ya yi kasuwanci ko sana’a da sauransu.
Don haka, birnin Zariya ya zama wata matattarar kowacce kabila daga sassa daban-daban na Najeriya; ba kabilar da ba za ka samu ba a masarautar Zazzau.
Masallacin Juma’ar masarautar Zazzau
Zazzau wurin ne wanda tun kafin bullowar jihadin Shehu Usman Danfodiyo akwai rukuni-rukuni na Fulani a cikin gari da kauyuka wadanda aikinsu shi ne bayar da karatu na addinin musulunci. Kuma tun a wannan lokaci akwai masallacin juma’a a unguwar Juma cikin birnin Zariya, wanda aka gina a zamanin mulkin Isiyaku Jatau wanda Habe ne.
Malaman unguwar Juman nan ko da aka yi jihadi sun ci gaba da limanci, kuma har yau su ke limanci, tun da su ma Fulani, kuma an same su da iliminsu. Ko da Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim ya gina masallaci a kofar fada, wancan masallacin na unguwar Juma ya rushe, an ci gaba da yin sallar Juma’a tare da limanci wadannan Fulani na unguwar Juma.Har yau zuri’arsu ke limanci.Â
Abin da kasar Zazzau ta ginu a kai
Ita Zazzau kasa ce da ma da ta ginu ne a kan abubuwa biyu, wato ilimin addinin musulunci, da harkar noma da kiwo. Kuma ko da Shehu Usman Danfodiyo ya yi jihadinsa abin da ya karfafa kenan.
*Wasan Kanawa da Zage-zagi*
Kamar yadda masana tarihi kan fada, mai karfi shi ke da iko. To, a wancan zamani, daular da ta yi karfi sai ta yunkura ta je ta mamaye wata. To, inda aka yi nasara, sai ka ji, amma inda aka gwabza, aka yi kare jini biri, ko kuma kowa ya tare kan iyakarsa, sai ka ji irin wadannan wasannin suna aukuwa.
Haka ma inda aka sami nasarar cin su da yaki, sai ka ji irin wannan wasa yana faruwa. Misali za ka ga Katsinawa da Gobirawa ana irin wannan wasa.
To, Kanawa da Zage-zagi ma akwai wannan wasa, cewa ita Sarauniya Amina ta kai hari Kano har Kofar Mata. Wannan kofar ai ana cewa nan ne aka dakatar da Sarauniya Amina, aka hana ta shiga cikin birnin Kano.
A wancan zamani na mulkin Habe dai, an ce an wani sarkin Kano ya kawo farmaki har Zariya, amma aka tare shi a tsakanin yankin da a yanzu aka sani da karamar hukumar Kubau, wajen garin Kargi. Aka yi ba-ta-kashi.
Saboda haka, ba mamaki ka ji ana wasa tsakanin Fulani da Barebari, tsakanin Katsinawa da Gobirawa, tsakanin har Yarabawa da Gobirawa. Kuma za ka ga irin wannan wasa yana dada dinke zumunci ne, ba yana batawa ba ne.
Wannan dai duk a zamanin mulkin Habe ne aka yi ire-iren wadannan hare-hare. Amma yayin da aka sami shigowar daular Usumaniyya, back kasashen suka zama daya, addinin musulunci ya hade su. Saboda haka, wata kasa ba ta kai wa wata kasa farmaki ba a cikin titocin da Shehu Usumanu Danfodiyo ya kafa. Sun zama abokan aiki, abokan hulda, kuma abokan shawarar juna.
*Girman kasar masarautar Zazzau a halin yanzu*
Saboda haka, sai sarkin musulmi na wancan lokaci ya ga ya fi dacewa a dauko wani malami cikin daliban Shehu Danfodiyo a ba shi jagoranci, duk da ya manyanta a wannan lokaci. Kuma lokacin ya yi tsawo, Malam Musa ya yi shekaru goma sha, Yamusa ya yi shekaru goma sha, AbdulKarim ya yi shekaru goma sha, Hammada ya yi ’yan kwanaki, Mamman Sani ya yi shekaru, Sidi AbdulKadir ya yi wata takwas zuwa goma a gadon sarauta. To, idan ka tara wadannan shekaru, ka ga an dumfari shekaru arba’in.
To, shi Malam AbdulSalam idan ka dora shekara arba’in a kan shekarunsa, ka ga ya manyanta. Amma sai sarkin musulmi na wancan lokaci ya ce a ba AbdulSalami sarautar Zazzau ya rike. Da haka ya zama raba-gardama. Ba a ba kowa ba daga cikin ‘ya’yan wadancan sarakuna. Wannan kuma shi ne dalilin zuwan gida na hudu a sarautar Zazzau kenan, wato don a sami natsuwa.                                                                                                      Â
Ta haka ne aka sami wadannan khalifofi guda hudu, kuma kowannensu an ba shi sarauta ne a matsayin kansa na masanin addinin musulunci, na mai biyayya da gaskata abin da jihadin Shehu Usman Danfodiyo ya kawo bisa koyarwa Alkur’ani da Sunnar Manzon Allah (SAW).
Tarihin Mai Martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Dokta Shehu Idris
Haihuwa da Tsatson Sarki
Mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Dokta Shehu Idris, an haife shi ne a watan Maris na shekarar 1936. Wanda ya haife shi ne Mai Unguwa Auta. Sunan na Auta aka fi sani, amma sunansa na Littafi shi ne Idrisu. Shi da ne, dan autan Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Sambo.
Shi kuma Sarki Muhamadu Sambo da ne, kuma na biyu a cikin ‘ya’yan Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim. Shi kuma Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim shi ne na farko a daular Fulani karkashin jaddada addinin musulunci da Shehu Usumanu Danfodiyo ya yi a kasar Zazzau, kuma shi ne ya assasa gidan Katsinawa a sarautar Zazzau.
Ina Sarki ya taso?
Shi Mai martaba Sarki lokacin mahaifinsu yana Mai Unguwa a unguwar Iya a nan aka haife shi. Unguwar Iya wata unguwa ce da ke tsakanin unguwar Durumi da Kuyanbana. A nan ya girma, ya shekara akalla bakwai, inda har ya shiga makarantar allo, ya fara karatun addini.
A nan dai unguwar Iya ya yi makarantar farko da Bature ya gina a cikin birnin Zariya, wadda ake kira ‘Town School one�, ita ce kuma makaranatar ‘Kofar Kuyanbana Local Government Education Primary School�. Yanzu ana ce mata ‘Waziri Lawal Local Government Education Primary School�, a nan ya fara karatu.
Bayan ya gama sai ya tafi Alhudahuda College, lokacin ana kiran makarantar da sunan ‘Middle School�. Daga nan aka yi masa sauyi, ya koma makarantar koyar da malunta a Katsina lokacin ana kiran ta ‘Katsina Teachers� College�.To, a nan ya koyi aikin koyarwa, wanda shi ne babbar sana’arsa ta farko da ya iya.
Daga baya mai martaba ya sauya daga malamin makaranta ya shiga aikin mulki, wanda har ya je kasar Ostireliya (Australia). Yana cikin daliban farko da ofishin jakadancin Ostireliya suka dauki dawainiyarsu suka je suka yi karatu na koyon ilimin mulki a kasar ta Osireliya
Wuraren da ya yi aiki
Daga shekarar 1956 ya koyar a wurare daban-daban a cikin garin Zariya da kauyuka. Ya koyar a Zangon Aya, ya koyar a Paki, har ya yi hedimasta a Pakin. Ya kuma yi hedimasta a Hancin Kare a makarantar ‘Town School No.3’�.
A shekarar 1962 ya koma aikin mulki, lokacin da ya koma karkashin hukumar ‘NA� (Native Authority) ta Zariya a zamanin Sarkin Zazzau Aminu. Inda ya gwama aiki biyu, wato yana aiki a hukumar ‘NA�, kuma yana aiki a matsayin jami’in sadarwa na hukumar kula da kananan hukumomi da masarautu na jihar Arewa.
Daga baya Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu ya ba shi mukamin Babban sarakatare na musamman na sarki. Daga nan ne sai aka nada shi sarauta, ya zama wakilin ofis, wato mai daukar nauyin duk abin da ya shafi aikin masarauta a karkashin ‘Native Authorityâ€? a wannan lokacin.                              Â
Ya rike wannan mukami na tsawon kamar shekara biyu zuwa uku, sai Mai Martaba Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu ya nada shi hakimin birni da kewaye, mukamin da ya rike na tsawon shekara biyu zuwa uku, yana hakimi. Kuma Dan Madamin Zazzau.
A shekarar 1975 likafarsa ta yi gaba, aka ba shi a sarautar Sarkin Zazzau.
Sauyin da ya kawo a sarautar Zazzau cikin shekaru arba’in da biyar yana mulki
Makusantan Sarkin suna ganin ba wani al’amari da ya shafi rayuwar Zage-zagi a birnin Zariya ko a masarautar Zazzau ne da ba a sami ci gaba ba. Ta fuskar ilimi, tun daga kananan makarantun firamare zuwa sakandire, zuwa na gaba da sakandire, zuwa jami’o’i, makarantun sojoji da sauransu da aka yi a masarautarsa, akalla ba za a rasa makarantu ashirin ba.
Iyalin Sarki
Allah Ya albarkaci mai martaba Sarkin Zazzau Alhaji Dokta Shehu Idris da iyali masu yawa. Yana da mata hudu, da ‘ya’ya maza da mata da yawansu ba zai gaza arba’in da biyu ko da biyar ba.
Dabi’u da halayen Sarki
Daya daga cikin hakiman masarautar Zazzau, Salanken Zazzau, Dokta Muhammadu Bello AbdulKadir, ya ce, babbar baiwar da Allah Ya yi wa mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Shehu Idris, shi ne hakuri, yana da hakuri matuka.
Ga shi kuma yana da kawaici, wanda a sakamakon haka ne ya kai kusan shekara ashirin yana sarauta, amma bai nada kowa daga cikin ‘ya’yansa sarauta ba, saboda kawaici. Sai da dattawa suka matsa masa, cewa idan bai nada ‘ya’yansa a sarauta ba, wa zai nada masa su.
Hakurinsa da dauriya suka sa Zazzau ta zama kowa ya zo karbabbe ne, zai zo ya sami karbuwa wajen al’umma ya yi kasuwanci, ko ya nemi ilimi, ko ya yi kasuwanci ko sana’a da sauransu.
Don haka, birnin Zariya ya zama wata matattarar kowacce kabila daga sassa daban-daban na Najeriya; ba kabilar da ba za ka samu ba a masarautar Zazzau.
Masallacin Juma’ar masarautar Zazzau
Zazzau wurin ne wanda tun kafin bullowar jihadin Shehu Usman Danfodiyo akwai rukuni-rukuni na Fulani a cikin gari da kauyuka wadanda aikinsu shi ne bayar da karatu na addinin musulunci. Kuma tun a wannan lokaci akwai masallacin juma’a a unguwar Juma cikin birnin Zariya, wanda aka gina a zamanin mulkin Isiyaku Jatau wanda Habe ne.
Malaman unguwar Juman nan ko da aka yi jihadi sun ci gaba da limanci, kuma har yau su ke limanci, tun da su ma Fulani, kuma an same su da iliminsu. Ko da Sarkin Zazzau Malam AbdulKarim ya gina masallaci a kofar fada, wancan masallacin na unguwar Juma ya rushe, an ci gaba da yin sallar Juma’a tare da limanci wadannan Fulani na unguwar Juma.Har yau zuri’arsu ke limanci.Â
Abin da kasar Zazzau ta ginu a kai
Ita Zazzau kasa ce da ma da ta ginu ne a kan abubuwa biyu, wato ilimin addinin musulunci, da harkar noma da kiwo. Kuma ko da Shehu Usman Danfodiyo ya yi jihadinsa abin da ya karfafa kenan.
*Wasan Kanawa da Zage-zagi*
Kamar yadda masana tarihi kan fada, mai karfi shi ke da iko. To, a wancan zamani, daular da ta yi karfi sai ta yunkura ta je ta mamaye wata. To, inda aka yi nasara, sai ka ji, amma inda aka gwabza, aka yi kare jini biri, ko kuma kowa ya tare kan iyakarsa, sai ka ji irin wadannan wasannin suna aukuwa.
Haka ma inda aka sami nasarar cin su da yaki, sai ka ji irin wannan wasa yana faruwa. Misali za ka ga Katsinawa da Gobirawa ana irin wannan wasa.
To, Kanawa da Zage-zagi ma akwai wannan wasa, cewa ita Sarauniya Amina ta kai hari Kano har Kofar Mata. Wannan kofar ai ana cewa nan ne aka dakatar da Sarauniya Amina, aka hana ta shiga cikin birnin Kano.
A wancan zamani na mulkin Habe dai, an ce an wani sarkin Kano ya kawo farmaki har Zariya, amma aka tare shi a tsakanin yankin da a yanzu aka sani da karamar hukumar Kubau, wajen garin Kargi. Aka yi ba-ta-kashi.
Saboda haka, ba mamaki ka ji ana wasa tsakanin Fulani da Barebari, tsakanin Katsinawa da Gobirawa, tsakanin har Yarabawa da Gobirawa. Kuma za ka ga irin wannan wasa yana dada dinke zumunci ne, ba yana batawa ba ne.
Wannan dai duk a zamanin mulkin Habe ne aka yi ire-iren wadannan hare-hare. Amma yayin da aka sami shigowar daular Usumaniyya, back kasashen suka zama daya, addinin musulunci ya hade su. Saboda haka, wata kasa ba ta kai wa wata kasa farmaki ba a cikin titocin da Shehu Usumanu Danfodiyo ya kafa. Sun zama abokan aiki, abokan hulda, kuma abokan shawarar juna.
*Girman kasar masarautar Zazzau a halin yanzu*