Sashe 9
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ade ta kurawa Dahiru ido yana tsaye daga gefen kofa. Tun da ya gaishe su bai sake cewa komai ba. Tana ta lura da yadda yake kallon Mawadda. Ita dai tasan batun aure babu amma ga dukkan alamu akwai dalilinsa na dawowa wurinta a yau. Cike da hikima irin na iyaye mata ta kafe Baba da ido har sai da jikinsa ya bashi tana kallonsa. Yana dagowa ta cilla idanunta bakin kofa nan ya gano me take nufi. Gajeren murmushi yayi ya riko hannun mahaifinsa yana cewa gara su fara jin nawa za'a cajesu kudin asibiti tun wuri. Malam yayi na'am da hakan suka tashi.
Bayan fitarsu kuma har lokacin Dahiru bai fita ba Ade ta dan tabo Yaya. Iya na gani ta hade rai
"Ke ni fa na lura sai wani shishshigewa Haule kike yi ko irin tsohon kishin nan baya dan motsa miki. To idan ma wata gulmar za'ayi muje ayi dani. Mawadda kwanta ina zuwa"
Yaya da Ade duka murmushi suka yi sanin halin Iya. Tana gani kuwa ta hau waka tana yadawa Yaya habaici
"kishiyata idan sararki leke-leke, leka tukunya leka langa wata rana zaki sha ita ce a gadon baya...luba lubayye 'yan mata luba lubayye luba ta girma. Ehe idan mutum so yake ya shiga tsakanina da ahalina kurwarmu kur abadan wa tutur"
Kunya kamar Ade ta nutse a kasa. Duk da Yaya ta dade da sabawa da wannan habaici tun mutuwar auren Sa'ade amma bata jindadi duk ranar da Iya ta yaba mata magana. Musamman ma ga Dahiru a dakin.
Innar Fatihu abin ya kona mata rai ta bi bayansu tana ramawa Yaya. Ade ta dafe kai daga kokarin abin arziki rikici zai kaurewa tsofaffin. Kunya kuma bazata bari ta fadi gaskiya ba duk da ita Yayan ta ma fahimta.
Dakin yayi shiru sai sautin ajiyar zuciyar Mawadda. A hankali Dahiru ya soma takowa wurin gadon wani masifaffen tsoro ya ziyarci zuciyarta. Ita kadai a daki da namiji. Yanzu idan ya rufe kofa fa? Ina su Baba suka tafi? Wace hanya zata bi ta gudu kafin ya cutar da ita? Tunani barkatai ne suke yawo a kwakwalwarta sai dube-dube take yi ko zata ci karo da makamin da za ta kwala masa.
Ganin yadda ta rude ya sashi tsayuwa a inda yake sannan cikin muryar rarrashi ya kirata da sunan da ya sanya mata tun ranar da ya fara zuwa gidansu tadi.
"Mawaddatan wa Rahma"
Kamar an tsikareta a lokacin ta dawo hayyacinta ta soma neman nutsuwa. Ita kadai take ta nanatawa zuciyarta Dahiru ne. Dahirun da kika sani wanda zaku yi aure nan da 'yan watanni. Sai kuma ta girgiza kai, wane auren kina kwance a gadon asibiti anyi miki fy....
Kasa karasa tunanin tayi ta soma kuka. Yana lura da duk wani motsinta. Kukan ne ya sake taba shi.
"Assha, assha banyi zaton zuwana zai saka ki kuka ba. Kiyi hakuri bari na tafi"
Juyawarsa tasa ta jin wani iri a ranta. Shikenan BB ya rabata da masoyinta. Dahiru matashin da 'yan matan Tariwa suke rububi saboda ya maida hankali a karatun boko har turanci yana ji. Ranar da ya fara zuwa gidansu da maganar yana sonta har rawa tayi a daki ita kadai tsabar murna da samun abin da bata yi zato ba. Yanzu shikenan mafarkinta yazo karshe ba ma shi ba wani ma bazai so aurenta ba.
"Nagode jiya ma na ga kazo. Ka gaishe da su Inna. Kuma...kuma...uhmm Allah Ya baka mace tagari"
Girgiza kai yayi yana murmushi ganin yadda take kuka. A da sai yayi da gaske take iya yi masa magana. Wato yanzu a ganinta sunyi bankwana kenan.
"Ke kin fasa aurena ne ko fatan kishiya tagari kike yi tun kafin ayi bikin mu?"
Bata fahimce shi bata ta dan dago kai mayafin ya dan karkace har fuskar da yanzu kullum take lullubewa ta dan bayyana.
"Me kace?"
"Cewa nayi kin fasa aurena ne kike min addu'ar mata tagari?"
"To ai.." sai kuma ta sunkuyar da kanta. Ko ba'a fada ba ya kamata ya san cewa yanzu maganar aure ta tashi. Don ko shi yana so bata tunanin zata taba aure a rayuwarta.
Komai nata yanzu tausayi yake bashi. Minti daya tana magana, sai kuma tayi shiru ta hau tunani ita kadai sai dai a ga yanayin fuskarta na sauyawa ko tana girgiza kai.
"Kinga mu bar wannan magana ga kunun da aka zuba miki har ya huce baki sha ba."
"Na koshi" ta amsa a takaice.
"Kin taba ganin ciwo ya warke da yunwa?"
Bata son tsawaita magana dashi saboda duk da halin da take ciki har yanzu tana son sa. Rabuwarsu shine zai fi mata alkhairi. Ita duniyar ma gabadaya ta fice mata a rai.
"Su Iya ma na fada musu su kyaleni. Gara yunwa da damuwa suyi ajalina ko na huta da wannan abin da nake ji a raina"
Kofin kunun ya mika mata taki karba sai ma kuka da ta soma mai cin rai.
Kamar zai ajiye sai ya juyo yana kallonta
"Mawaddatan wa Rahma!" Ya kirata idanunsa suna kwalla
"Idan kin manta bari na tuna miki. Da wanda ya cakawa kansa wuka, da wanda ya rataye kansa, da kuma mai shirin yiwa kansa horon yunwa da gangan duka idan suka mutu sunansu kafirai. Yanzu ke kin yarda rayuwarki ta kare a haka? Kin rayu cikin talauci, talaucin nan dai ya rabaki da inuwar mahaifanki ya kaiki inda wani bunsuru ya cutar da ke. Talaucin dai shine yasa kike kwance a wannan asibitin. Kofar dakin tana rawa kamar zata fadowa mutane ga taga babu ko kyalle. Sai an sallameki ki dawo gida da alakoron maleriya"
Bata san lokacin da murmushi ya subuce mata ba. Dahiru yayi dariya zuciyarsa tana samun nishadi daga fara'ar da ya ga tayi.
Saurin rufe fuskarta tayi yace "ko ke fa da kin takurawa kanki da kuka. Zancen gaskiya nake miki. Ace duk wahalar da kika sha a duniya kin zabi a lahirar ma...."
Da hannu ta dakatar dashi "naji bani kunun zan sha"
Dadi ya kama shi ya mika mata. Juyar da kanta tayi ga mayafi ta rufe kai ta kafa kai bata sauke kofin ba sai da ta shanye. Ashe ba karamar yunwa taji ba. Yana ganin ta shanye yace ta kawo ya kara mata. A kunyace ta mika kofin amma har ranta tana bukatar karin nan.
Yana cikin zuba mata su Iya suka dawo. Ganin Dahiru yana zuba kunu ta rike baki.
"Iko sai Rabbani, Dahiru daga jinya kuma sai ka nemi shanye kunun mara lafiya. Banda abinka ga tuwo sabo ne ma nayi mata yau da shi ka ci. Ita saboda yanayin jiki sai da abu ruwa-ruwa"
Wayyo kunya ba Dahirun ba, ba Mawaddan ba sannan ba iyayensu ba.
Ji yayi kamar ya saki kofin a kasa ya kwasa a guje. Yadda yayu tsamo ya bawa Mawadda tausayi.
Ade ta wayance "ke dai Iya ba kya rabo da zolaya abin harda suruki kuma"
Dahiru yana tsaye da kofi ya kasa karasa zubawa sai juya dan tsohon filas din kunun da kofin yake yi.
Iya ta isa gabansa kafin Innar Fatihu ta karasa. Karbar filas din tayi tana dan yin sama da kasa dashi ta auna yawan kunun
"Ya naji ba nauyi? Da bamu shigo ba sai ka shanye ko?"
Innar Fatihu taja tsaki "wai meye haka ne Ta Rasulu? Kinsa yaro ko motsin kirki ya kasa yi"
Duk sai ya basu tausayi musamman Mawadda. Tayi karfin halin cewa "Iya wallahi ni nasha karamin zaiyi"
"Ki bari dan Manzo" cewar Iya dadi ya kama ta. Ta dan dungure Dahiru "to kuma sai kayi shiru maimakom kayi min bayani? Kai da ita ashe zani ce ta tadda muje mu. Duk taron marasa magana ne"
Ganin yayi murmushi ne yana sosa keya yasa hankalin Ade da Yaya ya kwanta.
Iya ta sake cika kofin taf ta mikawa Mawadda "ungo"
Yamutsa fuska tayi tana satar kallon Dahiru "na koshi"
"Kin ma isa?" Har zata soma fada sai kuma ta hau dariya.
"Au, auho gulmammu, ashe da gangan kike kin cin abinci kina jiran na hanun masoyi. Oh ni Ta Rasulu kun gane min fitsarar yaran zamani. Ashe fitarmu dadi tayi muku."
Kan kace meye wannan Dahiru ya fice daga dakin Mawadda ta tura kanta a cinyar Iyan da ta zauna kusa da ita don kunya. Innar Fatihu duk abinta sai da ta dara. Ade kuwa kunya ta hana. Ita kuma Yaya tana tsoron tayi a watso mata maganar da zata yi mata ciwo.
******
Yana tsaye yana jiran abin hawa sai murmushi yake shi kadai saboda nasarar sanya Mawadda cikin nishadi da yayi. Da ya tuna tijarar da Iya tayi masa kuwa hannu ya dora a ka yana dariyar halin da ta jefa shi gaban Ade da Yaya.
Bai jima ba ya sami bus ya tafi gida. Rumfar Inna ya shiga jin taku ta taso daga kishingidar da tayi
"Ummiyo ina kika je tun dazu ina nemanki?"
"Inna ni ne" ya fada yana daga labulen ya shigo ya zauna sannan ya gaisheta.
Maimakon ta amsa ta bishi da kallon tuhuma "daga ina kake? Ina ka tafi da sanyin safiya ko karyawa baka yi ba?"
"Asibiti na koma kinsan jiya kafin mu taho dinnan jikin nata ba dadi"
Rai a bace ta daga yatsa tana karkada masa alamun gargadi
"saurare ni da kyau Dahiru. Zamuyi magana mai bullewa da Baffanku amma kafin nan tun wuri ka cireta a ranka. Duk garin nan babu mai yarda dansa ya auri yarinyar da irin wannan kaddara ta sameta. To nima baza'ayi a gidana ba."
Duk da dama yayi zaton haka saboda maganar da yaji sunyi da Ade jiya amma baiji dadi ba. Sunkuyar da kansa yayi cikin tausasa harshe ya soma magana
"Inna kiyi hakuri kada kice na fasa aurenta. Kema gashi kin kira abin da kaddara ai ba kai kanta tayi ba tsautsayi ne"
Ta san za'a rina dama indai Dahiru ne sai ta tashi tsaye. Ana masa kallon shiru-shiru mai hakuri da iya zama da mutane amma a zahirin gaskiya mutum ne kaifi daya ga zafin zuciya idan ransa bai so abu ba. Idan tana so tayi nasarar raba shi da auren nadama sai ta bi a sannu.
Bayan fitarsu kuma har lokacin Dahiru bai fita ba Ade ta dan tabo Yaya. Iya na gani ta hade rai
"Ke ni fa na lura sai wani shishshigewa Haule kike yi ko irin tsohon kishin nan baya dan motsa miki. To idan ma wata gulmar za'ayi muje ayi dani. Mawadda kwanta ina zuwa"
Yaya da Ade duka murmushi suka yi sanin halin Iya. Tana gani kuwa ta hau waka tana yadawa Yaya habaici
"kishiyata idan sararki leke-leke, leka tukunya leka langa wata rana zaki sha ita ce a gadon baya...luba lubayye 'yan mata luba lubayye luba ta girma. Ehe idan mutum so yake ya shiga tsakanina da ahalina kurwarmu kur abadan wa tutur"
Kunya kamar Ade ta nutse a kasa. Duk da Yaya ta dade da sabawa da wannan habaici tun mutuwar auren Sa'ade amma bata jindadi duk ranar da Iya ta yaba mata magana. Musamman ma ga Dahiru a dakin.
Innar Fatihu abin ya kona mata rai ta bi bayansu tana ramawa Yaya. Ade ta dafe kai daga kokarin abin arziki rikici zai kaurewa tsofaffin. Kunya kuma bazata bari ta fadi gaskiya ba duk da ita Yayan ta ma fahimta.
Dakin yayi shiru sai sautin ajiyar zuciyar Mawadda. A hankali Dahiru ya soma takowa wurin gadon wani masifaffen tsoro ya ziyarci zuciyarta. Ita kadai a daki da namiji. Yanzu idan ya rufe kofa fa? Ina su Baba suka tafi? Wace hanya zata bi ta gudu kafin ya cutar da ita? Tunani barkatai ne suke yawo a kwakwalwarta sai dube-dube take yi ko zata ci karo da makamin da za ta kwala masa.
Ganin yadda ta rude ya sashi tsayuwa a inda yake sannan cikin muryar rarrashi ya kirata da sunan da ya sanya mata tun ranar da ya fara zuwa gidansu tadi.
"Mawaddatan wa Rahma"
Kamar an tsikareta a lokacin ta dawo hayyacinta ta soma neman nutsuwa. Ita kadai take ta nanatawa zuciyarta Dahiru ne. Dahirun da kika sani wanda zaku yi aure nan da 'yan watanni. Sai kuma ta girgiza kai, wane auren kina kwance a gadon asibiti anyi miki fy....
Kasa karasa tunanin tayi ta soma kuka. Yana lura da duk wani motsinta. Kukan ne ya sake taba shi.
"Assha, assha banyi zaton zuwana zai saka ki kuka ba. Kiyi hakuri bari na tafi"
Juyawarsa tasa ta jin wani iri a ranta. Shikenan BB ya rabata da masoyinta. Dahiru matashin da 'yan matan Tariwa suke rububi saboda ya maida hankali a karatun boko har turanci yana ji. Ranar da ya fara zuwa gidansu da maganar yana sonta har rawa tayi a daki ita kadai tsabar murna da samun abin da bata yi zato ba. Yanzu shikenan mafarkinta yazo karshe ba ma shi ba wani ma bazai so aurenta ba.
"Nagode jiya ma na ga kazo. Ka gaishe da su Inna. Kuma...kuma...uhmm Allah Ya baka mace tagari"
Girgiza kai yayi yana murmushi ganin yadda take kuka. A da sai yayi da gaske take iya yi masa magana. Wato yanzu a ganinta sunyi bankwana kenan.
"Ke kin fasa aurena ne ko fatan kishiya tagari kike yi tun kafin ayi bikin mu?"
Bata fahimce shi bata ta dan dago kai mayafin ya dan karkace har fuskar da yanzu kullum take lullubewa ta dan bayyana.
"Me kace?"
"Cewa nayi kin fasa aurena ne kike min addu'ar mata tagari?"
"To ai.." sai kuma ta sunkuyar da kanta. Ko ba'a fada ba ya kamata ya san cewa yanzu maganar aure ta tashi. Don ko shi yana so bata tunanin zata taba aure a rayuwarta.
Komai nata yanzu tausayi yake bashi. Minti daya tana magana, sai kuma tayi shiru ta hau tunani ita kadai sai dai a ga yanayin fuskarta na sauyawa ko tana girgiza kai.
"Kinga mu bar wannan magana ga kunun da aka zuba miki har ya huce baki sha ba."
"Na koshi" ta amsa a takaice.
"Kin taba ganin ciwo ya warke da yunwa?"
Bata son tsawaita magana dashi saboda duk da halin da take ciki har yanzu tana son sa. Rabuwarsu shine zai fi mata alkhairi. Ita duniyar ma gabadaya ta fice mata a rai.
"Su Iya ma na fada musu su kyaleni. Gara yunwa da damuwa suyi ajalina ko na huta da wannan abin da nake ji a raina"
Kofin kunun ya mika mata taki karba sai ma kuka da ta soma mai cin rai.
Kamar zai ajiye sai ya juyo yana kallonta
"Mawaddatan wa Rahma!" Ya kirata idanunsa suna kwalla
"Idan kin manta bari na tuna miki. Da wanda ya cakawa kansa wuka, da wanda ya rataye kansa, da kuma mai shirin yiwa kansa horon yunwa da gangan duka idan suka mutu sunansu kafirai. Yanzu ke kin yarda rayuwarki ta kare a haka? Kin rayu cikin talauci, talaucin nan dai ya rabaki da inuwar mahaifanki ya kaiki inda wani bunsuru ya cutar da ke. Talaucin dai shine yasa kike kwance a wannan asibitin. Kofar dakin tana rawa kamar zata fadowa mutane ga taga babu ko kyalle. Sai an sallameki ki dawo gida da alakoron maleriya"
Bata san lokacin da murmushi ya subuce mata ba. Dahiru yayi dariya zuciyarsa tana samun nishadi daga fara'ar da ya ga tayi.
Saurin rufe fuskarta tayi yace "ko ke fa da kin takurawa kanki da kuka. Zancen gaskiya nake miki. Ace duk wahalar da kika sha a duniya kin zabi a lahirar ma...."
Da hannu ta dakatar dashi "naji bani kunun zan sha"
Dadi ya kama shi ya mika mata. Juyar da kanta tayi ga mayafi ta rufe kai ta kafa kai bata sauke kofin ba sai da ta shanye. Ashe ba karamar yunwa taji ba. Yana ganin ta shanye yace ta kawo ya kara mata. A kunyace ta mika kofin amma har ranta tana bukatar karin nan.
Yana cikin zuba mata su Iya suka dawo. Ganin Dahiru yana zuba kunu ta rike baki.
"Iko sai Rabbani, Dahiru daga jinya kuma sai ka nemi shanye kunun mara lafiya. Banda abinka ga tuwo sabo ne ma nayi mata yau da shi ka ci. Ita saboda yanayin jiki sai da abu ruwa-ruwa"
Wayyo kunya ba Dahirun ba, ba Mawaddan ba sannan ba iyayensu ba.
Ji yayi kamar ya saki kofin a kasa ya kwasa a guje. Yadda yayu tsamo ya bawa Mawadda tausayi.
Ade ta wayance "ke dai Iya ba kya rabo da zolaya abin harda suruki kuma"
Dahiru yana tsaye da kofi ya kasa karasa zubawa sai juya dan tsohon filas din kunun da kofin yake yi.
Iya ta isa gabansa kafin Innar Fatihu ta karasa. Karbar filas din tayi tana dan yin sama da kasa dashi ta auna yawan kunun
"Ya naji ba nauyi? Da bamu shigo ba sai ka shanye ko?"
Innar Fatihu taja tsaki "wai meye haka ne Ta Rasulu? Kinsa yaro ko motsin kirki ya kasa yi"
Duk sai ya basu tausayi musamman Mawadda. Tayi karfin halin cewa "Iya wallahi ni nasha karamin zaiyi"
"Ki bari dan Manzo" cewar Iya dadi ya kama ta. Ta dan dungure Dahiru "to kuma sai kayi shiru maimakom kayi min bayani? Kai da ita ashe zani ce ta tadda muje mu. Duk taron marasa magana ne"
Ganin yayi murmushi ne yana sosa keya yasa hankalin Ade da Yaya ya kwanta.
Iya ta sake cika kofin taf ta mikawa Mawadda "ungo"
Yamutsa fuska tayi tana satar kallon Dahiru "na koshi"
"Kin ma isa?" Har zata soma fada sai kuma ta hau dariya.
"Au, auho gulmammu, ashe da gangan kike kin cin abinci kina jiran na hanun masoyi. Oh ni Ta Rasulu kun gane min fitsarar yaran zamani. Ashe fitarmu dadi tayi muku."
Kan kace meye wannan Dahiru ya fice daga dakin Mawadda ta tura kanta a cinyar Iyan da ta zauna kusa da ita don kunya. Innar Fatihu duk abinta sai da ta dara. Ade kuwa kunya ta hana. Ita kuma Yaya tana tsoron tayi a watso mata maganar da zata yi mata ciwo.
******
Yana tsaye yana jiran abin hawa sai murmushi yake shi kadai saboda nasarar sanya Mawadda cikin nishadi da yayi. Da ya tuna tijarar da Iya tayi masa kuwa hannu ya dora a ka yana dariyar halin da ta jefa shi gaban Ade da Yaya.
Bai jima ba ya sami bus ya tafi gida. Rumfar Inna ya shiga jin taku ta taso daga kishingidar da tayi
"Ummiyo ina kika je tun dazu ina nemanki?"
"Inna ni ne" ya fada yana daga labulen ya shigo ya zauna sannan ya gaisheta.
Maimakon ta amsa ta bishi da kallon tuhuma "daga ina kake? Ina ka tafi da sanyin safiya ko karyawa baka yi ba?"
"Asibiti na koma kinsan jiya kafin mu taho dinnan jikin nata ba dadi"
Rai a bace ta daga yatsa tana karkada masa alamun gargadi
"saurare ni da kyau Dahiru. Zamuyi magana mai bullewa da Baffanku amma kafin nan tun wuri ka cireta a ranka. Duk garin nan babu mai yarda dansa ya auri yarinyar da irin wannan kaddara ta sameta. To nima baza'ayi a gidana ba."
Duk da dama yayi zaton haka saboda maganar da yaji sunyi da Ade jiya amma baiji dadi ba. Sunkuyar da kansa yayi cikin tausasa harshe ya soma magana
"Inna kiyi hakuri kada kice na fasa aurenta. Kema gashi kin kira abin da kaddara ai ba kai kanta tayi ba tsautsayi ne"
Ta san za'a rina dama indai Dahiru ne sai ta tashi tsaye. Ana masa kallon shiru-shiru mai hakuri da iya zama da mutane amma a zahirin gaskiya mutum ne kaifi daya ga zafin zuciya idan ransa bai so abu ba. Idan tana so tayi nasarar raba shi da auren nadama sai ta bi a sannu.