Sashe 35
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar hankalin Dr Tani ba karamin tashi yayi ba don da kyar tayi bacci. A ina zata sami mai auren Qareeba? Bata son mijinta yaji wannan maganar sam domin a danginsa zai nema daga nan su sami na gori ace gwanjonta aka yi musu. Mutum daya gareta da ta rike kawa aminiya amma sun kwana biyu ko gaisuwar kirki bata shiga tsakaninsu ba. Duk da haka gani tayi gara ta sake gwada sa'arta a karo na karshe kafin a nemi wata mafitar.
Wayarta ta dauko ta jima tana sake-sake kafin ta danna kira.
Haj Mara tana zaune yau ko wanka ta kasa abin duniya ya isheta ta mika hannu ta dauki wayarta da take ruri. Sunan Dr Tani ta gani to itama damuwa ta isheta ta dauka da sauri ta gyara muryarta tayi sallama.
Dr Tani tana amsawa Haj Mara tayi wata shewa kamar bata san waye ba sai yanzu "Tani kece don Allah? Wayyo aminiyata shiru shiru na rasa nambarki ke kuma kin dena nemana"
Dr Tani taji dadi ashe dai Haj Mara bata ya da ita gabadaya ba rashin number ne amma sai ta dan dake.
"Haba Marakisiyya idan babu waya baki san gidana bane? "
Kamar zata yi kuka tace "na sani amma tun tafiyar Babawo naga kamar kinyi fushi dani. Kuma na fada miki Alhaji ne yace gara ya bar kasar kura ta lafa"
"Har shekara takwas? Ni mu bar wannan zancen dama kira nayi mu gaisa inji lafiyarku" ga dama ta samu na son jin yaya BB amma tana gudun kada ace yayi aure.
Kamar Haj Mara ta sani tace "ina 'yata kuwa Qareeba? Nasan yanzu kila tayi yara biyu ko uku. Ba rabonmu lokacin gashi shi yaki aure har yanzu"
Kankame wayar Dr Tani tayi dadi har kasan zuciyarta
"To ai nima har yau Qareeba dai tana nan in fada miki taki kowa. Nayi fadan nayi nasihar duk a banza. Wai tunda ta rasa BB na farko ta hakura da aure ke kiji"
Wata siririyar dariya Haj Mara tayi. Ta sani sarai Qareeba babu mashinshini ne tunda takan dan bibiyi me Dr Tani din take ciki. To amma dama ce ta karshe ta samu ta yiwa Babawo aure ko ya kintsu kamar kowa.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰15
*Batul Mamman*💖
Tsohon kango ne wanda yaran unguwar da yake ciki ma tsoron yin dare suke a kusa dashi saboda 'yan daban da suka mayar dashi wurin sheke ayarsu. Daidai ballallen gate din BB ne zaune cikin daya daga cikin motocin Alh Sule yana yiwa shugaban 'yan daban bayani.
"An fada min kaima dan Kano ne ina tunanin nemanta bazai yi muku wahala ba"
Garwashi yace "to Yallabai ka bamu hoto da adireshi mana saboda rage wahala ko ya kace."
Sosa yamutsatstsen kansa yayi wanda yaki yarda ya aske har yau yace da yasan address din me zai kawo shi wurinsu ma. Gajeren tsaki yaja sannan yace.
"Sunanta Mawadda kauyensu yana cikin Kabeji a nan Kano"
Me Garwashi zaiyi in ba dariya ba "Kabeji kuma Ranka ya dade kwadon salak zaka yi hala?....hahahahhh zan taho maka da caras da gurji"
A fusace BB ya fito daga motar ya damki wuyansa. Yaran Garwashi suka soma tasowa ganin an kama ubangidansu. Shaka sosai BB yayi masa yana huci "ba wasa bane ya kawoni. Sati daya na baka ka nemo min inda take koda gidan miji ne zan baku 500k."
Jin haka Garwashi ya daga hannu ya dakatar da yaransa. BB ya ture shi har ya kusa fadowa ya dago kai a wahale "zamu duba amma duk da haka ka bamu wata inkiya mana yadda zamu jidadin yi maka aiki na dai fahimta garinsu a Bebeji yake ko"
Sai da ya shiga mota ya zauna sannan yace "anyi mata fyade shekara takwas da suka wuce har kotu an shiga amma basuyi nasara ba"
Zaro idanu Garwashi yayi "wane dan...."
Sai kuma yayi shiru ganin irin kallon da BB yake yi masa kafin ya bada musu kura yaja motar yayi gaba.
Yaransa da suke gefe suka marmatso yana rike da wuya yana jujjuya shi.
Na hannun damansa cikin yaran yace "Baaba ina tunanin shine fa yayi fyaden kaga ai yayi kalar eh yane. Kuma don rainin sense ya shake maka wuya a fadarka don yana takamar tsohonsa yana da maiko"
Cecekuce yaran suka soma suna nuna takaicin hanasu su far wa BB lokacin da ya shake shi.
"Ku barni dashi zamu nemo yarinyar nan duk inda take. Amma kwarankwatsa zamu nuna mata solidarity tunda 'yar uwa ce bakanuwa. Gayis (guys) mu ware gobe akwai trabilin gabanmu."
******
Mawadda na zaune gaban Baba daga gefen tabarma a tsakar gidansu. Yaya da Ade suna dakunansu haka ma Iya da Inna.
Kamar kullum nasiha da yabonta ya soma yi don baya gajiya wurin karfafa mata gwiwa akan hakuri da tawakkali.
"Ina alfahari dake sosai da yadda ki ka karbi kaddara bata sanya kin zama daga cikin mutane masu gazawa imaninsu yayi rauni ba. Ki cigaba da mika lamuranki ga Allah da sannu zakiyi ta girbar alkhairi kinji."
"In sha Allahu Baba"
"Bayan wannan Mawadda ina so kada kiji kunyata ki fada min gaskiya yaya kuka yi da Dahiru?"
Faduwar gaba taji hade da kunya a lokaci guda ta dukar da kanta sannan ta fada masa gaskiya wato maganar aure da Dahiru yayi mata sai dai bata fada masa yadda suka kare da ya zama yayanta kawai ba. Ta dai sanar dashi bata amince ba.
"Baba kada ka damu nima na san ba zanyi aure ba saboda bazan yaudari kaina ba" ta fada cikin dakakkiyar murya tana kokarin boye karayar da zuciyarta take neman yi.
Tausayinta Mal Fatihu yaji sosai "Allah ne Masani ko kina da rabon aure ko babu. Abinda nake so ki kiyaye dai bai wuce kada kisa Dahiru a zuciyarki ba. Kinga yadda abubuwa suka kasance a da bana jin yanzu zata sauya zani. Duk yadda na matsu inga kina dakinki kamar sauran 'yan uwanki bazan taba yarda kije inda ba'a bukatarki ba. Na shaida Dahiru mutum ne managarci amma aure Mawadda ba alaka bace tsakanin mata da miji kawai. Ta hada da iyaye da 'yan uwa makusanta. Duk inda kika samu matsala da daya daga ciki ko iyayen miji ko 'yan uwansa to ina mai tabbatar miki miji ko hadiyarki yake don kyautatawa sai jindadinki ya ragu musamman idan iyayensa ne."
Kasa daurewa tayi hawaye ya soma fita a idanunta "Baba zan kiyaye in Allah Ya yarda" tana kaiwa nan ta tashi ta bar wurin da sauri saboda kukan da ya taso mata. Bandaki ta shige ta rufe kofa ta shiga kuka har tsakar gidan Baba yana jiyo shesshekarta.
Shi kanshi ba don namiji bane babu abinda zai hana shi tayata kukan. Zuciyarsa ce tayi masa nauyi yana kara ganin laifinsa ne na turata aiki tun farko har haka ta faru. Amma zasu cigaba da hakuri har Allah Ya kawo musu mafita.
*****
Washegari tana gama ayyukanta na gida asibiti ta tafi. Da yake da wuri taje bata dade sosai a layi ba.
Dr Imran ya gama jin duk wani bayani nata ya nuna mata file din gabansa.
"Duk wani bayani ko gwaji daga ranar da na fara dubaki har yanzu suna cikin nan. Ina fata kin rike duka bayannan da nayi miki game da ainihin abinda ya sameki har ya janyo miki lalurar?"
"Na gane Doctor. Nagode sosai" tace a hankali tana kokarin boye hawayenta. Tun maganarsu da Baba jiya haka ta tashi sukuku. Ba wai abin mamaki bane kuma itama kafin ya fada ta riga tasan da hakan. Sai dai yanzu tausayin rayuwarta take yi kawai. Bata taba hango rayuwarta zata zama haka ba. Tuni ta gama shiri da tsara rayuwarta da Dahiru a shekarun baya sai gashi Allah Ya zartar da ikonSa ta koma mai gyara amare wadda bata da ranar ganin nata auren.
Dr Imran tashi yayi ya dawo dayar kujerar marasa lafiyan wadda take kallonta ya zauna. Yana ganin yadda ta sake tura tata baya duk da cewa akwai tazara tsakaninsu tun farko. Ya sani irin haka yana daga cikin tsoron da yake bibiyarta har yanzu. A kokarinsa na taimaka mata ta rage ne yasa idan ta shiga office dinsa yake tilasta mata rufe kofa ko bata so don ta gane ba kowane namiji bane macuci. Tun tana zama tayi ta kallon kofa tana hawaye har ya samu ta dena kukan. Yanzu gashi ta yarda dashi zata zauna ba tare da tunanin komai ba.
"Mawadda."
"Na'am Doctor"
"A ka'ida yau ne last day da zan duba ki sai dai idan wata matsalar ta taso wadda bama fata."
Godiya tayi masa amma yadda ya gama karantarta na tsahon lokacin da take zuwa asibitinsu ya san tana da damuwa a ranta.
"Ko soyayyata ce tayi miki mugun kamu kike tunanin daga yau zamu rabu? Banyi niyar barinki ba yau ko kinki ko kinso zan zo gida neman izini wurin Baba"
Kai ta dago da sauri "don Allah kada kazo. Na fada maka bazanyi auren nan ba."
"Saboda wani banzan BB yake ko wa? Ki barshi haka duk inda yake sakayyar Allah zata kama shi" Ya fada ransa yana dan baci.
Kai ta girgiza tana soma kuka "ni dai kawai"
"Ke dai kawai me? Ko dai Dahiru ki ke jira?"
Dr Imran yasan labarin Mawadda domin kuwa bata boye masa komai ba bayan ya hillaceta da dabararsu ta likitoci a kokarin taimakonta. Duk duniya babu wanda take iya fadawa abubuwan da ba kowa ya sani ba bayan iyayenta sai shi.
Yanayin da yaga ta shiga yasa shi gane ko ma meye matsalarta da Dahirun a ciki. Rarrashi da shawara ya soma bata da kanta ta fada masa dawowar Dahiru cikin rayuwarta da kuma kudurinta na kin amince masa.
Dariya yayi ya shiga zolayarta "Akwai matsala kuwa don nima ba hakura zanyi ba. In fact kince na kara zage damtse mai rabo ya dauka. Wato ciwon soyayya zai tashi shine duk naga jikinki a mace yau kamar wata mara lafiya."
Sai da ya gama sawa ta saki ranta sannan yace ta yawaita addu'a da neman zabin Allah.
Wayarta ta dauko ta jima tana sake-sake kafin ta danna kira.
Haj Mara tana zaune yau ko wanka ta kasa abin duniya ya isheta ta mika hannu ta dauki wayarta da take ruri. Sunan Dr Tani ta gani to itama damuwa ta isheta ta dauka da sauri ta gyara muryarta tayi sallama.
Dr Tani tana amsawa Haj Mara tayi wata shewa kamar bata san waye ba sai yanzu "Tani kece don Allah? Wayyo aminiyata shiru shiru na rasa nambarki ke kuma kin dena nemana"
Dr Tani taji dadi ashe dai Haj Mara bata ya da ita gabadaya ba rashin number ne amma sai ta dan dake.
"Haba Marakisiyya idan babu waya baki san gidana bane? "
Kamar zata yi kuka tace "na sani amma tun tafiyar Babawo naga kamar kinyi fushi dani. Kuma na fada miki Alhaji ne yace gara ya bar kasar kura ta lafa"
"Har shekara takwas? Ni mu bar wannan zancen dama kira nayi mu gaisa inji lafiyarku" ga dama ta samu na son jin yaya BB amma tana gudun kada ace yayi aure.
Kamar Haj Mara ta sani tace "ina 'yata kuwa Qareeba? Nasan yanzu kila tayi yara biyu ko uku. Ba rabonmu lokacin gashi shi yaki aure har yanzu"
Kankame wayar Dr Tani tayi dadi har kasan zuciyarta
"To ai nima har yau Qareeba dai tana nan in fada miki taki kowa. Nayi fadan nayi nasihar duk a banza. Wai tunda ta rasa BB na farko ta hakura da aure ke kiji"
Wata siririyar dariya Haj Mara tayi. Ta sani sarai Qareeba babu mashinshini ne tunda takan dan bibiyi me Dr Tani din take ciki. To amma dama ce ta karshe ta samu ta yiwa Babawo aure ko ya kintsu kamar kowa.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰15
*Batul Mamman*💖
Tsohon kango ne wanda yaran unguwar da yake ciki ma tsoron yin dare suke a kusa dashi saboda 'yan daban da suka mayar dashi wurin sheke ayarsu. Daidai ballallen gate din BB ne zaune cikin daya daga cikin motocin Alh Sule yana yiwa shugaban 'yan daban bayani.
"An fada min kaima dan Kano ne ina tunanin nemanta bazai yi muku wahala ba"
Garwashi yace "to Yallabai ka bamu hoto da adireshi mana saboda rage wahala ko ya kace."
Sosa yamutsatstsen kansa yayi wanda yaki yarda ya aske har yau yace da yasan address din me zai kawo shi wurinsu ma. Gajeren tsaki yaja sannan yace.
"Sunanta Mawadda kauyensu yana cikin Kabeji a nan Kano"
Me Garwashi zaiyi in ba dariya ba "Kabeji kuma Ranka ya dade kwadon salak zaka yi hala?....hahahahhh zan taho maka da caras da gurji"
A fusace BB ya fito daga motar ya damki wuyansa. Yaran Garwashi suka soma tasowa ganin an kama ubangidansu. Shaka sosai BB yayi masa yana huci "ba wasa bane ya kawoni. Sati daya na baka ka nemo min inda take koda gidan miji ne zan baku 500k."
Jin haka Garwashi ya daga hannu ya dakatar da yaransa. BB ya ture shi har ya kusa fadowa ya dago kai a wahale "zamu duba amma duk da haka ka bamu wata inkiya mana yadda zamu jidadin yi maka aiki na dai fahimta garinsu a Bebeji yake ko"
Sai da ya shiga mota ya zauna sannan yace "anyi mata fyade shekara takwas da suka wuce har kotu an shiga amma basuyi nasara ba"
Zaro idanu Garwashi yayi "wane dan...."
Sai kuma yayi shiru ganin irin kallon da BB yake yi masa kafin ya bada musu kura yaja motar yayi gaba.
Yaransa da suke gefe suka marmatso yana rike da wuya yana jujjuya shi.
Na hannun damansa cikin yaran yace "Baaba ina tunanin shine fa yayi fyaden kaga ai yayi kalar eh yane. Kuma don rainin sense ya shake maka wuya a fadarka don yana takamar tsohonsa yana da maiko"
Cecekuce yaran suka soma suna nuna takaicin hanasu su far wa BB lokacin da ya shake shi.
"Ku barni dashi zamu nemo yarinyar nan duk inda take. Amma kwarankwatsa zamu nuna mata solidarity tunda 'yar uwa ce bakanuwa. Gayis (guys) mu ware gobe akwai trabilin gabanmu."
******
Mawadda na zaune gaban Baba daga gefen tabarma a tsakar gidansu. Yaya da Ade suna dakunansu haka ma Iya da Inna.
Kamar kullum nasiha da yabonta ya soma yi don baya gajiya wurin karfafa mata gwiwa akan hakuri da tawakkali.
"Ina alfahari dake sosai da yadda ki ka karbi kaddara bata sanya kin zama daga cikin mutane masu gazawa imaninsu yayi rauni ba. Ki cigaba da mika lamuranki ga Allah da sannu zakiyi ta girbar alkhairi kinji."
"In sha Allahu Baba"
"Bayan wannan Mawadda ina so kada kiji kunyata ki fada min gaskiya yaya kuka yi da Dahiru?"
Faduwar gaba taji hade da kunya a lokaci guda ta dukar da kanta sannan ta fada masa gaskiya wato maganar aure da Dahiru yayi mata sai dai bata fada masa yadda suka kare da ya zama yayanta kawai ba. Ta dai sanar dashi bata amince ba.
"Baba kada ka damu nima na san ba zanyi aure ba saboda bazan yaudari kaina ba" ta fada cikin dakakkiyar murya tana kokarin boye karayar da zuciyarta take neman yi.
Tausayinta Mal Fatihu yaji sosai "Allah ne Masani ko kina da rabon aure ko babu. Abinda nake so ki kiyaye dai bai wuce kada kisa Dahiru a zuciyarki ba. Kinga yadda abubuwa suka kasance a da bana jin yanzu zata sauya zani. Duk yadda na matsu inga kina dakinki kamar sauran 'yan uwanki bazan taba yarda kije inda ba'a bukatarki ba. Na shaida Dahiru mutum ne managarci amma aure Mawadda ba alaka bace tsakanin mata da miji kawai. Ta hada da iyaye da 'yan uwa makusanta. Duk inda kika samu matsala da daya daga ciki ko iyayen miji ko 'yan uwansa to ina mai tabbatar miki miji ko hadiyarki yake don kyautatawa sai jindadinki ya ragu musamman idan iyayensa ne."
Kasa daurewa tayi hawaye ya soma fita a idanunta "Baba zan kiyaye in Allah Ya yarda" tana kaiwa nan ta tashi ta bar wurin da sauri saboda kukan da ya taso mata. Bandaki ta shige ta rufe kofa ta shiga kuka har tsakar gidan Baba yana jiyo shesshekarta.
Shi kanshi ba don namiji bane babu abinda zai hana shi tayata kukan. Zuciyarsa ce tayi masa nauyi yana kara ganin laifinsa ne na turata aiki tun farko har haka ta faru. Amma zasu cigaba da hakuri har Allah Ya kawo musu mafita.
*****
Washegari tana gama ayyukanta na gida asibiti ta tafi. Da yake da wuri taje bata dade sosai a layi ba.
Dr Imran ya gama jin duk wani bayani nata ya nuna mata file din gabansa.
"Duk wani bayani ko gwaji daga ranar da na fara dubaki har yanzu suna cikin nan. Ina fata kin rike duka bayannan da nayi miki game da ainihin abinda ya sameki har ya janyo miki lalurar?"
"Na gane Doctor. Nagode sosai" tace a hankali tana kokarin boye hawayenta. Tun maganarsu da Baba jiya haka ta tashi sukuku. Ba wai abin mamaki bane kuma itama kafin ya fada ta riga tasan da hakan. Sai dai yanzu tausayin rayuwarta take yi kawai. Bata taba hango rayuwarta zata zama haka ba. Tuni ta gama shiri da tsara rayuwarta da Dahiru a shekarun baya sai gashi Allah Ya zartar da ikonSa ta koma mai gyara amare wadda bata da ranar ganin nata auren.
Dr Imran tashi yayi ya dawo dayar kujerar marasa lafiyan wadda take kallonta ya zauna. Yana ganin yadda ta sake tura tata baya duk da cewa akwai tazara tsakaninsu tun farko. Ya sani irin haka yana daga cikin tsoron da yake bibiyarta har yanzu. A kokarinsa na taimaka mata ta rage ne yasa idan ta shiga office dinsa yake tilasta mata rufe kofa ko bata so don ta gane ba kowane namiji bane macuci. Tun tana zama tayi ta kallon kofa tana hawaye har ya samu ta dena kukan. Yanzu gashi ta yarda dashi zata zauna ba tare da tunanin komai ba.
"Mawadda."
"Na'am Doctor"
"A ka'ida yau ne last day da zan duba ki sai dai idan wata matsalar ta taso wadda bama fata."
Godiya tayi masa amma yadda ya gama karantarta na tsahon lokacin da take zuwa asibitinsu ya san tana da damuwa a ranta.
"Ko soyayyata ce tayi miki mugun kamu kike tunanin daga yau zamu rabu? Banyi niyar barinki ba yau ko kinki ko kinso zan zo gida neman izini wurin Baba"
Kai ta dago da sauri "don Allah kada kazo. Na fada maka bazanyi auren nan ba."
"Saboda wani banzan BB yake ko wa? Ki barshi haka duk inda yake sakayyar Allah zata kama shi" Ya fada ransa yana dan baci.
Kai ta girgiza tana soma kuka "ni dai kawai"
"Ke dai kawai me? Ko dai Dahiru ki ke jira?"
Dr Imran yasan labarin Mawadda domin kuwa bata boye masa komai ba bayan ya hillaceta da dabararsu ta likitoci a kokarin taimakonta. Duk duniya babu wanda take iya fadawa abubuwan da ba kowa ya sani ba bayan iyayenta sai shi.
Yanayin da yaga ta shiga yasa shi gane ko ma meye matsalarta da Dahirun a ciki. Rarrashi da shawara ya soma bata da kanta ta fada masa dawowar Dahiru cikin rayuwarta da kuma kudurinta na kin amince masa.
Dariya yayi ya shiga zolayarta "Akwai matsala kuwa don nima ba hakura zanyi ba. In fact kince na kara zage damtse mai rabo ya dauka. Wato ciwon soyayya zai tashi shine duk naga jikinki a mace yau kamar wata mara lafiya."
Sai da ya gama sawa ta saki ranta sannan yace ta yawaita addu'a da neman zabin Allah.