Sashe 17
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta daure fuska a zatonta yasan da sammancin.
"Kasan da matsalar ka ki gaya min da wuri sai da na gani yanzu"
"Ni dai kawai kiyi hakuri tunda kin sani yanzu a aura min ita. Wallahi kwanakin nam tunaninta baya barina ko baccin kirki nayi"
Haushi ya bata "kaga idan ba kashe wannan gobarar akayi ba babu abinda zaisa Dr. Tani ta baka auren 'yarta."
Ya wani hade gira "wai kin zata da wannan doluwar nake Qarira take ko wa. Nifa gaskiya bata yi min ba ko kadan. Shekaranjiyan ma da na zauna a gidan kawai don kada ranki ya baci ne. Maganar Mawadda nake miki, Hajiya sonta nake da aure"
Yadda maganarsa ta kona mata rai bata san lokacin da ta kwashe shi da mari ba. Yana rike da kumatun ta harzuka ta soma fada tare da jifansa da takardar.
"Idan ma kaje kayi shaye-shayenka ne ai baka manta yadda ake karatu ba ko. Shashashan banza"
Ko a jikinsa da ya karanta. Sai ma cewa yayi ta taimaka masa a kashe case din tun kafin aje kotu ta hanyar aura masa Mawadda.
Magana take son yi amma ta rasa abin cewa. Ta ga alama Babawo so yake ya kasheta da ranta. Fita tayi tana kuka ta koma dakinta tana sake gwada kiran Alh Sule amma shiru. Sai daga baya ta tuna lokacin ta tura masa sakon text.
Da safe haka ta tashi sukuku. Da wa zatayi shawara kuma meye mafita? Sauran yaranta ta nema amma duka tayi musu karyar sharri Mawadda ta yiwa BB kamar yadda ta fadawa 'yan uwanta da na mijinta sai dai kadan cikinsu ne suka yarda saboda sun san waye BB. Dole ta yiwa tufkar hanci kafin mutumcinsu ya zube.
*****
Yau kwana biyar kenan Dahiru da sauran ma'aikatan gidan suna jiran albashi. Inna da kanta tazo gidan Bilya ta sanar dashi su Mawadda zasu shiga kotu. Ta kuma dage akan cewa indai suka shiga kotun nan to wajibi ya manta da wata maganar aure. Ita a ganinta ba gara ma surutun Ummiyo iyakarsa kauyensu ba. Amma yanzu kila har a In Da Ranka sai an fada.
Shima dai hankalinsa ya tashi baya maraba da wannan terere. Gashi bata da waya ko magana da sunyi. Albashinsa yake jira ya tafi gida ko kwana biyu ne yayi. Ya gama daidaitawa da wani mai shagon waya a kusa da garejin su Bilya ya sami 'yar karama second hand da zai kaiwa Mawadda. Ga gwanjo da zai saya saboda sun kusa fara lacca. Sannan ma dai nauyinsa dake wuyan Bilya da gorin da Furaira take yi masa yasa ya kuma matsuwa da kudin. A kalla ko cefane zai rage masa ya bashi wani abin.
Yana ta hamma Kuku ta fito da abincinsa da na maigadi. Sun dan taba barkwanci sannan Maigadin yace
"Ni kuwa baki ji komai game da albashinmu ba? Yarona aka koro daga makaranta kayansa sun lalace. Kinsan halin maza gwiwar duk ta fashe. Bana son bashi tunda wata ya riga ya kare nace ya zauna ayi albashi tukunna."
Mikawa Dahiru kwanukan tayi shima hankalinsa yana kan zancen.
"Shekaranjiya bayan bakon nan na Qareeba ya tafi naje na tambayi Hajiya saboda nima ina da bukatarsu. Shine tace wai muyi hakuri maigidan bashi da halin biyanmu yanzu saboda shidimar sallah da akayi, sai mu jira wani watan a hada mana duka"
Hankalin maigadi ya tashi tsaye na Dahiru ya tashi sama. Abincin fice masa yayi daga rai ya rasa inda zaisa ransa yaji dadi. Ya dogara da kudin nan sosai. Bai gama fita daga wannan tashin hankalin ba Safwan ya leko yace masa ya shigo falo Mummy na kira.
A sanyaye ya tashi yabi bayansa. Hadadden falo ne da bai taba shiga irinsa ba.
"Daddy yace zaka je ganin gida karshen wata kunyi magana ko"
"Eh"
"Naji shiru baka tafi bane wani abin kake jira ko ka fasa?"
Ji yayi tambayar ma kamar wani rainin hankali.
"Dama albashi..."
Tayi dan murmshi "au ashe fa ban sanar daku ba. Albashi dai sai wani watan yanzu babu kudi. Sannan dubu takwas za'a baka"
Da sauri ya dago kai suka hada ido sai kuma ya sunkuyar da nasa. Dubu takwas din ma kudi ce kuma bai raina ba amma me zaisa su saka masa rai haka. Da dubu takwas anya zai iya rike Mawadda ga karatu? Ko dai ya sake neman wani aikin ne ya hada biyu?
Kallonsa tayi tsaf "kudin yayi kadan ne zaka fasa aikin?"
"A'a Allah Ya amfana. Gobe zan tafi in Allah Ya yarda." Tashi yayi kamar an zare masa laka ya fita ta bishi da dogon tsaki. Kasancewar kanin mijinta ne ya kawo shi yasa bata son shi ko kadan.
*****
Gari na wayewa ya gama shirinsa sai Tariwa. Abin takaici kudin mota ma Bilya ne ya bashi. Ganin Dahirun ya damu ya rinka bashi baki akan yayi hakuri neman halak da wuya. Haka nan ya kama hanya babu ko sisi sai kudin mota.
Iyayensa duk hakuri suka bashi akan rashin albashin. Allah Yaso shi ma baiyi gaggawar fada musu za'a bashi dubu ashirin ba da yaji kunya.
Rana na sanyi ya tafi gidan Mal Fatihu sai dai yayi rashin sa'a ba anan Mawadda take ba yanzu. Kaninta ne ya sanar dashi sannan yace ya jira Baba nason ganin shi.
"Mal Dahiru saukar yaushe? Ya ya Kano ya wurin aikin naka" Baba yace yana fitowa.
Kamar kullum a kunyace ya duka suka gaisa.
Baba ya soma magana "Mal Dahiru kaji maganar zuwa kotu ko?"
"Eh Baba Allah Ya bamu sa'a"
"To amin, amma na dakatar da kai ne saboda munyi magana jiya da Baffanku. Alal hakika idan na baka Mawadda na cuceka. Sannan mutane da dama basu goyi bayan karar da muka shigar ba. To amma bani da niyar janyewa. Yarinya an rabata da farinciki ya kamata ko yaya a kwatar mata hakkinta ta hanyar ganin an hukunta yaron nan"
"Amma Baba zamu iya daukar lauya ne?"
Bayani yayi masa cewa kotu ta basu lauyan gwamnati da zai waklicesu saboda haka kudaden da zasu biya babu yawa sosai. Yanzu haka nan da kwana biyu za'a fara shari'a. Amma gobe zasu koma Kanon saboda likita da Mawadda za ta gani.
"Sauran magana nasan zakuyi da su Mal Isiyaku. Nagode sosai Allah Ya shi maka albarka. Mawadda tana tare da Sa'ade amma ba sai kaje ba. Ku fara magana a gida"
Gidan ya koma ya sami Inna ta tabbatar masa cewa Baffa yaje sunyi magana da Baba an soke zancen aure.
Ummiyo ce ta fito zata kwashe kwanukan da ta wanke yana ganinta ya hambareta da kafa "munafuka mai bakin reza"
Kifewa tayi a kasa ta soma kuka Inna ta taso "kada ka kashe min 'ya don an hanaka auren wata Mawadda."
Kwalla ce ta taru a idonsa "Inna da kanki kike kiranta wata Mawadda? To wallahi duk ku shirya bata da miji sai ni in sha Allahu. Ba dai ni zan zauna da ita ba."
Baffa da ya shigo lokacin yace "sannu Dahiru wata guda a birni shine zaka nuna mana kaima ka waye ko"
Matsawa yayi kusa dashi "Baffa don Allah kada ka hanani aurenta. Kaddara ce fa ba kai kanta tayi ba. Yanzu idan da akan Ummiyo ya faru zaku ji dadi manemin aurenta ya gujeta"
Inna ta buge masa baki "bakinka ya sari danyen kashi. Aure kuma sai dai idan zaka daurawa kanka"
Dakinsu ya shiga rai a bace baya so iyayensa su zama masu son kansu. Meye laifinta? Ko basu kula da irin dukan da tasha fuskarta duk ta chanja ba. Shikenan sai duk wani jindadinta ya yanke saboda anyi mata fin karfi.
Kwanansa daya ya tattara ya koma. Inna tace ala raka taki gona, yafi ruwa gudu idan yaso. Aure ne dai baza'ayi ba duk nacinsa.
Su Baba ma dai ranar suka tafi. Daga asibiti matan zasu kwana a gidan Barira shi kuma zai nemi wani abokinsa ya kwana wurinsa da safe su hadu a tafi kotu.
****
Haj Mara ta fita hayyacinta cikin kankanin lokaci kai kace ita ce ma BB din. Shi uban gayyar hankalinsa a kwance in ka cire nacin a aura masa Mawadda. 'Yan uwa duk ta nuna musu ba abin damuwa bane saboda tana da shaidu akan sharrin da aka kulla musu. Kowa dai yaja jiki tunda ba wai wani mutumci gareta ba. Daga ita sai 'ya'yanta suke ta fama.
Sun dauko lauya wanda ya cajesu kudi ba kadan ba. Ita duk wannan bai dameta ba ma kamar Alh Sule da ya zare hannunsa a ciki kuma yace bazai katse aikinsa ya dawo ba kasar ba.
Bisa ka'ida ba'a son yiwa lauya karya domin ya sami dabarun kare wanda yake wakilta. Lauyan nasu bai ha'incesu ba yace ta daure taje su sasanta dasu kafin a shiga kotu saboda idan aka kama danta da laifi kulle shi za'ayi sannan ana iya cinsa tara mai tsoka saboda dukan da ya yi mata. Sannan BB da kansa ya nuna masa yana son yarinyar. Ganin da yake masa kamar wani dan kwaya yaji tsoron kada ya bata komai a gaban alkali shiyasa ma yace taje su sasanta.
Tariwa suka tafi suka daki gurbi babu kowa a gidan nasu. A makota ne aka sanar dasu sun tafi Kano. Haka suka kama hanya tayi ta kiran Gambo domin jin inda zata samesu ko ta sani.
Gambo tayi dariyar mugunta don bata mata karyar da tayi mata ba ta fada mata suna asibitin Malam domin kuwa ba jimawa da ta baro su suna jiran Dr Tani. Kwantar da kai Haj Mara tayi Gambo kuwa ta kwatanta mata bangaren da suke.
Ba tare da shan wahala ba ta iso. Daga inda take hangosu ta hango mata biyu da namiji daya sai Mawadda a bakin wata kofa. Da gani tasan iyayenta ne ta shafa jakarta ta jiyo envelop din da ta sako dubu dari da zata basu a kashe maganar. Sai dai ko rabin tafiya batayi ba ta hango Dr Tani ta isa garesu harda dafa kafadar Mawadda. A take hanjin cikin Haj Mara kada ta juya da sauri.
Mota ta koma a gigice ta shiga ta cewa dreban su fita da sauri. Gabadaya kanta ya dau zafi ta kasa tunani.
"Kasan da matsalar ka ki gaya min da wuri sai da na gani yanzu"
"Ni dai kawai kiyi hakuri tunda kin sani yanzu a aura min ita. Wallahi kwanakin nam tunaninta baya barina ko baccin kirki nayi"
Haushi ya bata "kaga idan ba kashe wannan gobarar akayi ba babu abinda zaisa Dr. Tani ta baka auren 'yarta."
Ya wani hade gira "wai kin zata da wannan doluwar nake Qarira take ko wa. Nifa gaskiya bata yi min ba ko kadan. Shekaranjiyan ma da na zauna a gidan kawai don kada ranki ya baci ne. Maganar Mawadda nake miki, Hajiya sonta nake da aure"
Yadda maganarsa ta kona mata rai bata san lokacin da ta kwashe shi da mari ba. Yana rike da kumatun ta harzuka ta soma fada tare da jifansa da takardar.
"Idan ma kaje kayi shaye-shayenka ne ai baka manta yadda ake karatu ba ko. Shashashan banza"
Ko a jikinsa da ya karanta. Sai ma cewa yayi ta taimaka masa a kashe case din tun kafin aje kotu ta hanyar aura masa Mawadda.
Magana take son yi amma ta rasa abin cewa. Ta ga alama Babawo so yake ya kasheta da ranta. Fita tayi tana kuka ta koma dakinta tana sake gwada kiran Alh Sule amma shiru. Sai daga baya ta tuna lokacin ta tura masa sakon text.
Da safe haka ta tashi sukuku. Da wa zatayi shawara kuma meye mafita? Sauran yaranta ta nema amma duka tayi musu karyar sharri Mawadda ta yiwa BB kamar yadda ta fadawa 'yan uwanta da na mijinta sai dai kadan cikinsu ne suka yarda saboda sun san waye BB. Dole ta yiwa tufkar hanci kafin mutumcinsu ya zube.
*****
Yau kwana biyar kenan Dahiru da sauran ma'aikatan gidan suna jiran albashi. Inna da kanta tazo gidan Bilya ta sanar dashi su Mawadda zasu shiga kotu. Ta kuma dage akan cewa indai suka shiga kotun nan to wajibi ya manta da wata maganar aure. Ita a ganinta ba gara ma surutun Ummiyo iyakarsa kauyensu ba. Amma yanzu kila har a In Da Ranka sai an fada.
Shima dai hankalinsa ya tashi baya maraba da wannan terere. Gashi bata da waya ko magana da sunyi. Albashinsa yake jira ya tafi gida ko kwana biyu ne yayi. Ya gama daidaitawa da wani mai shagon waya a kusa da garejin su Bilya ya sami 'yar karama second hand da zai kaiwa Mawadda. Ga gwanjo da zai saya saboda sun kusa fara lacca. Sannan ma dai nauyinsa dake wuyan Bilya da gorin da Furaira take yi masa yasa ya kuma matsuwa da kudin. A kalla ko cefane zai rage masa ya bashi wani abin.
Yana ta hamma Kuku ta fito da abincinsa da na maigadi. Sun dan taba barkwanci sannan Maigadin yace
"Ni kuwa baki ji komai game da albashinmu ba? Yarona aka koro daga makaranta kayansa sun lalace. Kinsan halin maza gwiwar duk ta fashe. Bana son bashi tunda wata ya riga ya kare nace ya zauna ayi albashi tukunna."
Mikawa Dahiru kwanukan tayi shima hankalinsa yana kan zancen.
"Shekaranjiya bayan bakon nan na Qareeba ya tafi naje na tambayi Hajiya saboda nima ina da bukatarsu. Shine tace wai muyi hakuri maigidan bashi da halin biyanmu yanzu saboda shidimar sallah da akayi, sai mu jira wani watan a hada mana duka"
Hankalin maigadi ya tashi tsaye na Dahiru ya tashi sama. Abincin fice masa yayi daga rai ya rasa inda zaisa ransa yaji dadi. Ya dogara da kudin nan sosai. Bai gama fita daga wannan tashin hankalin ba Safwan ya leko yace masa ya shigo falo Mummy na kira.
A sanyaye ya tashi yabi bayansa. Hadadden falo ne da bai taba shiga irinsa ba.
"Daddy yace zaka je ganin gida karshen wata kunyi magana ko"
"Eh"
"Naji shiru baka tafi bane wani abin kake jira ko ka fasa?"
Ji yayi tambayar ma kamar wani rainin hankali.
"Dama albashi..."
Tayi dan murmshi "au ashe fa ban sanar daku ba. Albashi dai sai wani watan yanzu babu kudi. Sannan dubu takwas za'a baka"
Da sauri ya dago kai suka hada ido sai kuma ya sunkuyar da nasa. Dubu takwas din ma kudi ce kuma bai raina ba amma me zaisa su saka masa rai haka. Da dubu takwas anya zai iya rike Mawadda ga karatu? Ko dai ya sake neman wani aikin ne ya hada biyu?
Kallonsa tayi tsaf "kudin yayi kadan ne zaka fasa aikin?"
"A'a Allah Ya amfana. Gobe zan tafi in Allah Ya yarda." Tashi yayi kamar an zare masa laka ya fita ta bishi da dogon tsaki. Kasancewar kanin mijinta ne ya kawo shi yasa bata son shi ko kadan.
*****
Gari na wayewa ya gama shirinsa sai Tariwa. Abin takaici kudin mota ma Bilya ne ya bashi. Ganin Dahirun ya damu ya rinka bashi baki akan yayi hakuri neman halak da wuya. Haka nan ya kama hanya babu ko sisi sai kudin mota.
Iyayensa duk hakuri suka bashi akan rashin albashin. Allah Yaso shi ma baiyi gaggawar fada musu za'a bashi dubu ashirin ba da yaji kunya.
Rana na sanyi ya tafi gidan Mal Fatihu sai dai yayi rashin sa'a ba anan Mawadda take ba yanzu. Kaninta ne ya sanar dashi sannan yace ya jira Baba nason ganin shi.
"Mal Dahiru saukar yaushe? Ya ya Kano ya wurin aikin naka" Baba yace yana fitowa.
Kamar kullum a kunyace ya duka suka gaisa.
Baba ya soma magana "Mal Dahiru kaji maganar zuwa kotu ko?"
"Eh Baba Allah Ya bamu sa'a"
"To amin, amma na dakatar da kai ne saboda munyi magana jiya da Baffanku. Alal hakika idan na baka Mawadda na cuceka. Sannan mutane da dama basu goyi bayan karar da muka shigar ba. To amma bani da niyar janyewa. Yarinya an rabata da farinciki ya kamata ko yaya a kwatar mata hakkinta ta hanyar ganin an hukunta yaron nan"
"Amma Baba zamu iya daukar lauya ne?"
Bayani yayi masa cewa kotu ta basu lauyan gwamnati da zai waklicesu saboda haka kudaden da zasu biya babu yawa sosai. Yanzu haka nan da kwana biyu za'a fara shari'a. Amma gobe zasu koma Kanon saboda likita da Mawadda za ta gani.
"Sauran magana nasan zakuyi da su Mal Isiyaku. Nagode sosai Allah Ya shi maka albarka. Mawadda tana tare da Sa'ade amma ba sai kaje ba. Ku fara magana a gida"
Gidan ya koma ya sami Inna ta tabbatar masa cewa Baffa yaje sunyi magana da Baba an soke zancen aure.
Ummiyo ce ta fito zata kwashe kwanukan da ta wanke yana ganinta ya hambareta da kafa "munafuka mai bakin reza"
Kifewa tayi a kasa ta soma kuka Inna ta taso "kada ka kashe min 'ya don an hanaka auren wata Mawadda."
Kwalla ce ta taru a idonsa "Inna da kanki kike kiranta wata Mawadda? To wallahi duk ku shirya bata da miji sai ni in sha Allahu. Ba dai ni zan zauna da ita ba."
Baffa da ya shigo lokacin yace "sannu Dahiru wata guda a birni shine zaka nuna mana kaima ka waye ko"
Matsawa yayi kusa dashi "Baffa don Allah kada ka hanani aurenta. Kaddara ce fa ba kai kanta tayi ba. Yanzu idan da akan Ummiyo ya faru zaku ji dadi manemin aurenta ya gujeta"
Inna ta buge masa baki "bakinka ya sari danyen kashi. Aure kuma sai dai idan zaka daurawa kanka"
Dakinsu ya shiga rai a bace baya so iyayensa su zama masu son kansu. Meye laifinta? Ko basu kula da irin dukan da tasha fuskarta duk ta chanja ba. Shikenan sai duk wani jindadinta ya yanke saboda anyi mata fin karfi.
Kwanansa daya ya tattara ya koma. Inna tace ala raka taki gona, yafi ruwa gudu idan yaso. Aure ne dai baza'ayi ba duk nacinsa.
Su Baba ma dai ranar suka tafi. Daga asibiti matan zasu kwana a gidan Barira shi kuma zai nemi wani abokinsa ya kwana wurinsa da safe su hadu a tafi kotu.
****
Haj Mara ta fita hayyacinta cikin kankanin lokaci kai kace ita ce ma BB din. Shi uban gayyar hankalinsa a kwance in ka cire nacin a aura masa Mawadda. 'Yan uwa duk ta nuna musu ba abin damuwa bane saboda tana da shaidu akan sharrin da aka kulla musu. Kowa dai yaja jiki tunda ba wai wani mutumci gareta ba. Daga ita sai 'ya'yanta suke ta fama.
Sun dauko lauya wanda ya cajesu kudi ba kadan ba. Ita duk wannan bai dameta ba ma kamar Alh Sule da ya zare hannunsa a ciki kuma yace bazai katse aikinsa ya dawo ba kasar ba.
Bisa ka'ida ba'a son yiwa lauya karya domin ya sami dabarun kare wanda yake wakilta. Lauyan nasu bai ha'incesu ba yace ta daure taje su sasanta dasu kafin a shiga kotu saboda idan aka kama danta da laifi kulle shi za'ayi sannan ana iya cinsa tara mai tsoka saboda dukan da ya yi mata. Sannan BB da kansa ya nuna masa yana son yarinyar. Ganin da yake masa kamar wani dan kwaya yaji tsoron kada ya bata komai a gaban alkali shiyasa ma yace taje su sasanta.
Tariwa suka tafi suka daki gurbi babu kowa a gidan nasu. A makota ne aka sanar dasu sun tafi Kano. Haka suka kama hanya tayi ta kiran Gambo domin jin inda zata samesu ko ta sani.
Gambo tayi dariyar mugunta don bata mata karyar da tayi mata ba ta fada mata suna asibitin Malam domin kuwa ba jimawa da ta baro su suna jiran Dr Tani. Kwantar da kai Haj Mara tayi Gambo kuwa ta kwatanta mata bangaren da suke.
Ba tare da shan wahala ba ta iso. Daga inda take hangosu ta hango mata biyu da namiji daya sai Mawadda a bakin wata kofa. Da gani tasan iyayenta ne ta shafa jakarta ta jiyo envelop din da ta sako dubu dari da zata basu a kashe maganar. Sai dai ko rabin tafiya batayi ba ta hango Dr Tani ta isa garesu harda dafa kafadar Mawadda. A take hanjin cikin Haj Mara kada ta juya da sauri.
Mota ta koma a gigice ta shiga ta cewa dreban su fita da sauri. Gabadaya kanta ya dau zafi ta kasa tunani.