Sashe 34
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"In sha Allah ni da kaina zanyi masa magana. Yanzu ma don naga bai dace bane daga zuwansa na dakatar dashi da gaggawa batare da sanin manufarsa ba. Ko menene ina tunanin zai sanar da ita a yau sai mu dauki matakin da ya dace"
Tausayinsu ne ya kama Ade don kuwa ta sani sarai kamar yadda Iya ta fada Mawadda har yanzu tana son Dahiru.
Daga bakin kofa yau ma ta zauna a kasa shi yana ciki akan kujera sai dai basu yiwa juna nisa sosai ba.
"Na fa jirgu Kanwarmu har na fara tunanin ko dai saurayi aka shanya ba yayan da yazo ganin kanwarsa ba" Dahiru yace yana mata murmushi.
Itama murmushin ta mayar masa "ai da saurayin ne karshenta sai dai ya gaji ya tafi gida"
Daga hannuwansa yayi "Allah Ya soni da aka yimin tayin zama yayan karfi da yaji na karba"
Wannan karon dariya Mawadda tayi sannan tace yayi hakuri yazo tana tsakar aiki ne. Ya nuna mata babu komai Yaya ta fada masa lokacin da ta kawo masa kayan ci da ke gabansa.
Mawadda ta kula ya sha kusan rabin jug din kunun ayar ta sake fuska "wato wanda na kawo rannan ne baka so shiyasa kaki shan komai"
"Kada ki fassara ni ranar ma kukan da na kula kinyi ne ya janyo. Yanzu kuwa da banci ba ai da na yiwa kaina. Wata awara naci mai dadi duk da bata dameni ba amma wannan gaskiya tayi dadi sosai"
"Kai dai Yayanmu santi kake yi. Baka san ko daga bakin titi idan kana neman gidan nan kace gidan awara za'a kawo ka ba? Tana cikin sana'ar da ta rikemu zuwa yanzu"
Kallonta yayi ita ce dai Mawaddansa amma ta chanja. Sai dai chanjin bai rage komai ba sai kara masa sonta a zuciyarsa.
"Yanzu ma aikin awarar ne ya hanaki fitowa da wuri?"
Gyara zama tayi kafin ta amsa masa "a'a ni sana'ata gyaran jiki. Idan ka tashi aure ka kawo min matarka nayi alkawarin yi mata kyauta"
Dagowa yayi sosai yace "alkawari fa, Allah Ya kaimu ko wace amaryar kice tun yanzu nasan an 'yanta ni daga kudin gyaran jiki."
Dadi kawai take ji ganinsa da magana dashi a haka. Itama tunanin tasa sauyawar take yi. Ya zama dan gayu sosai banda kamshin turarensa da ya cika falon shigarsa ma kawai ta isa ta sanya mace ta soshi.
Tayi nisa a tunani taji ya kada mata yatsunsa har sun bada sauti tayi saurin dauke kanta daga gareshi.
Shi kuwa yace "irin wannan kallon sai kisa nayi tunanin promotion na samu, har na fara murna."
Kunya taji ta jawo mayafinta ta sake rufe fuska. Shi kuwa sai dariya yace "Allah kuwa haka kawai aje a sa min rai ina dalili. Yanzu dai fara bani labarin da nake kwadayin ji"
Kasa dago kai tayi maganarsa tasa mata jin nauyinsa "labarina kayan kuka ne da bakinciki kawai a ciki"
"Assha Kanwarmu a rinka godewa Allah dubi yadda rayuwa ta koma miki fa. Ni dai ina son ji. Idan anzo wurin kuka muyi tare idan na bakinciki ne mu rarrashi juna. So nake wannan gap din shekaru na tsakaninmu mu cike shi ta hanyar sanar da juna komai. Kada ki manta na roki alfarmar zama dan uwa abokin sirrinki ne"
Ji tayi bazata iya yi masa musu ba ta soma bashi labarin tun daga shigarsu kotu na farko har zuwa yanzu. Tayi kuka sosai kafin ta gama. Dahiru kuma jijiyoyin kansa suka dago saboda bacin rai.
"Kiyi hakuri Mawadda ban so haka ta faru dake bama tare ba" yace murya na rawa saboda yadda yake ji.
Dago kanta tayi wanda ta kifa akan cinyarta ta turo baki "ni ban yarda ba yanzu kace idan abin kuka yazo tare zamuyi"
Yasan wasa take so ta sako domin sassauta musu yanayin da suka shiga sai ya biye mata.
"Kada kiso jin kukana don muryata sai ta cika gidan nan ga rashin dadin sauraro"
"Ni kam tana min dadi" tace ba tare da ta kawo komai a ranta ba. Kallon da yayi mata ne yasa ta rufe baki sai kuma tace saura nashi labarin.
Tun farkon zuwansa Kano ya soma fada mata har yau da yaje gidansu Qareeba.
Sai ga Mawadda tana dariya kamar ba ita ta gama kuka ba.
"Yanzu Yayanmu mace tace tana sonka shine kake ja mata aji. Huhmm gaskiya ka koma kace ka amince kawai don ni tayi min"
Dahiru yasha kunu da gaske baya son zancen Qareeba.
"Ita ce nace miki tana kirana Ahirin ko Dashiru da farkon labarin ko baki gane ba?"
Ta kuma dariya "Ahirin na Qareeba yaushe zamu sha biki?"
Kula yayi zolayarsa kawai take yi shiyasa ya dena biye mata. Sun cigaba da tattauna abubuwa da dama yace "amma likitan da taci amanarku a kotu baku sake binciken dalilinta ba?"
"Barta ta yiwa kanta ne. Kasan ranar Baba ya fadi muka taho asibiti shiyasa komai ya dakata"
Dahiru yace "naji dadi kinyi karatu yanzu Kanwarmu. Kinsan babban abinda ake cutarmu dashi bayan talauci shine rashin ilimi. Akwai abubuwa da dama da yakamata ace an kula dasu wancan lokacin. Kamar sanar da lauyan binciken farko na asibitin Bebeji, kawo wadancan 'yan sandan shaida da sauransu. Duk da haka kada ki damu hakkin da suka dauka bazai barsu ba"
Hawaye ne ya zubo mata tace "Yayanmu bazan taba yafe musu ba. Akwai ranar da abin ya ciyoni fa na kwana dashi a raina kawai sai gani a Kaduna"
Idanu ya zaro "me???"
Da sauri ta shiga girgiza hannunta tana kallon kofa "shhhhh babu wanda ya taba sani"
Yace "to wallahi fada min yadda abin ya faru ko na tona"
Wata harara ta doka masa wadda ta shiga ransa don yadda ta kada idanun ma burgeshi yayi "naji amma wallahi amanatul amana..."
"To ya isa kada ki karasa bazan fada ba bare ta cini." Ya yamutsa fuska "kai Kanwarmu ashe baki girma ba har yanzu wai amanatul amana"
"Rigakafi nake yi don kada ka janyo min duka"
Shekara biyu kenan lokacin tana ganiyar mafarkin BB tun da barayi suka shiga makotansu akace sun kusa yiwa matar gidan fyade. Shikenan abu ya dawo mata sabo tana kwanciya take farkawa a firgice. Ranar da abin ya isheta zuciya ta raya mata wai taje Kaduna ta hadasu da 'yan sanda a koma kotu. Karyar makaranta tayi sai gata a tasha kamar wasa. Taje Kaduna ta fadi sunan unguwar amma ta kasa gane ko ina. Tana cikin yawon tambaya kamar wata mahaukaciya Baba ya kirata yace ta taho masa da maganinsa na hawan jini a lamco pharmacy. Sai lokacin ta dawo hayyacinta a gaggauce ta koma tasha. Ranar sai bayan magariba ta dawo gida ta zuga musu karyar dalilin rashin dawowa da wuri. Babu wanda ya tuhumeta tunda ansan ba yawo take ba.
Dahiru na jin labarin ya sake tausaya mata da sabon kuduri a ransa na tunanin dole ma ya aureta ya nuna mata soyayyar da zata gusar mata da tunanin wannan azzalumin mutumin.
******
BB ne ya fito daga dakin Alh Sule yana ta gunaguni don me zai ce masa sai yayi aski. Kunyar yanayin shigarsa yasa sun kasa tura shi ya gaishe da 'yan uwa ma.
Yana saukowa Yasmin ta fito daga kitchen da food flask ta yiwa yaranta girki. Haj Mara tace masu aikinta bazasu yi girki da ita ba. A nata bangaren hakan yafi mata don yadda ta kula ta sawa yaran nan ido ba abin mamaki bane ta nemi hallaka su. Anyi sa'a damuwarta gabadaya tana ga BB yanzu.
Yasmin ya hango ya taho inda take kusa da dinning table ko kula Haj Mara baiyi ba da take tambayarsa yaya sukayi da Alhaji.
"Matar Alhaji wai yaya kanen nawa suke kiranki ne ba dadi ina cewa matar Alhaji dinnan."
Yasmin tayi murmushi ganin Haj Mara ta bata rai "Mama suke kirana"
"To ai nima kawai sai nabi ayari. Ni dasu ai same to same ne...so ba wani abu kingane ai" yace yana yin gaba.
Ita kuwa kai ta gyada kawai. Bayan ya wuce Haj Mara ta tashi zata bi bayansa taji Yasmin tace "ta inda aka hau ta nan ake sauka"
Dawowa tayi ta tsaya a gabanta "me ki ke nufi"
"Nayi miki magana ne?"
Rai a bace dama neman wurin huce takaici take ta cakumi wuyan Yasmin din.
"Ki bar ganin na kyaleki idan na dawo gareki bazaki ji dadi ba. Kina tunanin kin shigo min gida ne don ki kwace komai nawa?"
Bude baki tayi zata rama taji Alh Sule ya fito sai ta soma kuka tana bawa Haj Mara hakuri. Harda cewa idan saboda zuwansu ne zasu koma Abuja nan ba da dadewa ba.
Alh Sule yana saukowa ya kamata da fada sosai da ja mata kunne babu ruwanta da iyalinsa.
Mamaki ne ya hanata magana kawai ta bi bayan BB tana hawayen zuci.
*****
Kwana biyu da zuwan Dahiru tun ranar Qareeba ta dena walwala a gidan. Dr Tani ta sami maigidanta tace lokaci yayi da zasu nema mata lafiya a ajiye boko a gefe.
"Neman lafiya wane iri?" Yace yana kallonta.
"Daddy na tabbatar Qareeba aljanu gareta irin masu hana auren nan. Idan ba haka ba wane dalili zaisa ta kai har yanzu babu aure babu mijin auren a hannu"
Bayan gajeren nazari ya amince da bukatarta don shima ya gaji da gorin 'yan uwa. Abokansa ma wasu sukan yi masa maganar tun yana bada amsa har yayi shiru.
Maigadinsu suka sanarwa saboda ustazu ne. Washegari sai gashi da malami aka zo aka rinka yi mata karatu harda hayaki. Malamin gudun kada ace baiyi komai ba ya zaro bulala zai fara lafta mata wai aljanun masu taurin kai ne. Tana ganin haka ta tashi a guje ta koma ciki.
Bayan 'yan kwanaki ta sami Dr Tani har daki tace ita dai tana son aure tunda Dahirun bai samu ba su taimaka su sama mata miji.
Tausayinsu ne ya kama Ade don kuwa ta sani sarai kamar yadda Iya ta fada Mawadda har yanzu tana son Dahiru.
Daga bakin kofa yau ma ta zauna a kasa shi yana ciki akan kujera sai dai basu yiwa juna nisa sosai ba.
"Na fa jirgu Kanwarmu har na fara tunanin ko dai saurayi aka shanya ba yayan da yazo ganin kanwarsa ba" Dahiru yace yana mata murmushi.
Itama murmushin ta mayar masa "ai da saurayin ne karshenta sai dai ya gaji ya tafi gida"
Daga hannuwansa yayi "Allah Ya soni da aka yimin tayin zama yayan karfi da yaji na karba"
Wannan karon dariya Mawadda tayi sannan tace yayi hakuri yazo tana tsakar aiki ne. Ya nuna mata babu komai Yaya ta fada masa lokacin da ta kawo masa kayan ci da ke gabansa.
Mawadda ta kula ya sha kusan rabin jug din kunun ayar ta sake fuska "wato wanda na kawo rannan ne baka so shiyasa kaki shan komai"
"Kada ki fassara ni ranar ma kukan da na kula kinyi ne ya janyo. Yanzu kuwa da banci ba ai da na yiwa kaina. Wata awara naci mai dadi duk da bata dameni ba amma wannan gaskiya tayi dadi sosai"
"Kai dai Yayanmu santi kake yi. Baka san ko daga bakin titi idan kana neman gidan nan kace gidan awara za'a kawo ka ba? Tana cikin sana'ar da ta rikemu zuwa yanzu"
Kallonta yayi ita ce dai Mawaddansa amma ta chanja. Sai dai chanjin bai rage komai ba sai kara masa sonta a zuciyarsa.
"Yanzu ma aikin awarar ne ya hanaki fitowa da wuri?"
Gyara zama tayi kafin ta amsa masa "a'a ni sana'ata gyaran jiki. Idan ka tashi aure ka kawo min matarka nayi alkawarin yi mata kyauta"
Dagowa yayi sosai yace "alkawari fa, Allah Ya kaimu ko wace amaryar kice tun yanzu nasan an 'yanta ni daga kudin gyaran jiki."
Dadi kawai take ji ganinsa da magana dashi a haka. Itama tunanin tasa sauyawar take yi. Ya zama dan gayu sosai banda kamshin turarensa da ya cika falon shigarsa ma kawai ta isa ta sanya mace ta soshi.
Tayi nisa a tunani taji ya kada mata yatsunsa har sun bada sauti tayi saurin dauke kanta daga gareshi.
Shi kuwa yace "irin wannan kallon sai kisa nayi tunanin promotion na samu, har na fara murna."
Kunya taji ta jawo mayafinta ta sake rufe fuska. Shi kuwa sai dariya yace "Allah kuwa haka kawai aje a sa min rai ina dalili. Yanzu dai fara bani labarin da nake kwadayin ji"
Kasa dago kai tayi maganarsa tasa mata jin nauyinsa "labarina kayan kuka ne da bakinciki kawai a ciki"
"Assha Kanwarmu a rinka godewa Allah dubi yadda rayuwa ta koma miki fa. Ni dai ina son ji. Idan anzo wurin kuka muyi tare idan na bakinciki ne mu rarrashi juna. So nake wannan gap din shekaru na tsakaninmu mu cike shi ta hanyar sanar da juna komai. Kada ki manta na roki alfarmar zama dan uwa abokin sirrinki ne"
Ji tayi bazata iya yi masa musu ba ta soma bashi labarin tun daga shigarsu kotu na farko har zuwa yanzu. Tayi kuka sosai kafin ta gama. Dahiru kuma jijiyoyin kansa suka dago saboda bacin rai.
"Kiyi hakuri Mawadda ban so haka ta faru dake bama tare ba" yace murya na rawa saboda yadda yake ji.
Dago kanta tayi wanda ta kifa akan cinyarta ta turo baki "ni ban yarda ba yanzu kace idan abin kuka yazo tare zamuyi"
Yasan wasa take so ta sako domin sassauta musu yanayin da suka shiga sai ya biye mata.
"Kada kiso jin kukana don muryata sai ta cika gidan nan ga rashin dadin sauraro"
"Ni kam tana min dadi" tace ba tare da ta kawo komai a ranta ba. Kallon da yayi mata ne yasa ta rufe baki sai kuma tace saura nashi labarin.
Tun farkon zuwansa Kano ya soma fada mata har yau da yaje gidansu Qareeba.
Sai ga Mawadda tana dariya kamar ba ita ta gama kuka ba.
"Yanzu Yayanmu mace tace tana sonka shine kake ja mata aji. Huhmm gaskiya ka koma kace ka amince kawai don ni tayi min"
Dahiru yasha kunu da gaske baya son zancen Qareeba.
"Ita ce nace miki tana kirana Ahirin ko Dashiru da farkon labarin ko baki gane ba?"
Ta kuma dariya "Ahirin na Qareeba yaushe zamu sha biki?"
Kula yayi zolayarsa kawai take yi shiyasa ya dena biye mata. Sun cigaba da tattauna abubuwa da dama yace "amma likitan da taci amanarku a kotu baku sake binciken dalilinta ba?"
"Barta ta yiwa kanta ne. Kasan ranar Baba ya fadi muka taho asibiti shiyasa komai ya dakata"
Dahiru yace "naji dadi kinyi karatu yanzu Kanwarmu. Kinsan babban abinda ake cutarmu dashi bayan talauci shine rashin ilimi. Akwai abubuwa da dama da yakamata ace an kula dasu wancan lokacin. Kamar sanar da lauyan binciken farko na asibitin Bebeji, kawo wadancan 'yan sandan shaida da sauransu. Duk da haka kada ki damu hakkin da suka dauka bazai barsu ba"
Hawaye ne ya zubo mata tace "Yayanmu bazan taba yafe musu ba. Akwai ranar da abin ya ciyoni fa na kwana dashi a raina kawai sai gani a Kaduna"
Idanu ya zaro "me???"
Da sauri ta shiga girgiza hannunta tana kallon kofa "shhhhh babu wanda ya taba sani"
Yace "to wallahi fada min yadda abin ya faru ko na tona"
Wata harara ta doka masa wadda ta shiga ransa don yadda ta kada idanun ma burgeshi yayi "naji amma wallahi amanatul amana..."
"To ya isa kada ki karasa bazan fada ba bare ta cini." Ya yamutsa fuska "kai Kanwarmu ashe baki girma ba har yanzu wai amanatul amana"
"Rigakafi nake yi don kada ka janyo min duka"
Shekara biyu kenan lokacin tana ganiyar mafarkin BB tun da barayi suka shiga makotansu akace sun kusa yiwa matar gidan fyade. Shikenan abu ya dawo mata sabo tana kwanciya take farkawa a firgice. Ranar da abin ya isheta zuciya ta raya mata wai taje Kaduna ta hadasu da 'yan sanda a koma kotu. Karyar makaranta tayi sai gata a tasha kamar wasa. Taje Kaduna ta fadi sunan unguwar amma ta kasa gane ko ina. Tana cikin yawon tambaya kamar wata mahaukaciya Baba ya kirata yace ta taho masa da maganinsa na hawan jini a lamco pharmacy. Sai lokacin ta dawo hayyacinta a gaggauce ta koma tasha. Ranar sai bayan magariba ta dawo gida ta zuga musu karyar dalilin rashin dawowa da wuri. Babu wanda ya tuhumeta tunda ansan ba yawo take ba.
Dahiru na jin labarin ya sake tausaya mata da sabon kuduri a ransa na tunanin dole ma ya aureta ya nuna mata soyayyar da zata gusar mata da tunanin wannan azzalumin mutumin.
******
BB ne ya fito daga dakin Alh Sule yana ta gunaguni don me zai ce masa sai yayi aski. Kunyar yanayin shigarsa yasa sun kasa tura shi ya gaishe da 'yan uwa ma.
Yana saukowa Yasmin ta fito daga kitchen da food flask ta yiwa yaranta girki. Haj Mara tace masu aikinta bazasu yi girki da ita ba. A nata bangaren hakan yafi mata don yadda ta kula ta sawa yaran nan ido ba abin mamaki bane ta nemi hallaka su. Anyi sa'a damuwarta gabadaya tana ga BB yanzu.
Yasmin ya hango ya taho inda take kusa da dinning table ko kula Haj Mara baiyi ba da take tambayarsa yaya sukayi da Alhaji.
"Matar Alhaji wai yaya kanen nawa suke kiranki ne ba dadi ina cewa matar Alhaji dinnan."
Yasmin tayi murmushi ganin Haj Mara ta bata rai "Mama suke kirana"
"To ai nima kawai sai nabi ayari. Ni dasu ai same to same ne...so ba wani abu kingane ai" yace yana yin gaba.
Ita kuwa kai ta gyada kawai. Bayan ya wuce Haj Mara ta tashi zata bi bayansa taji Yasmin tace "ta inda aka hau ta nan ake sauka"
Dawowa tayi ta tsaya a gabanta "me ki ke nufi"
"Nayi miki magana ne?"
Rai a bace dama neman wurin huce takaici take ta cakumi wuyan Yasmin din.
"Ki bar ganin na kyaleki idan na dawo gareki bazaki ji dadi ba. Kina tunanin kin shigo min gida ne don ki kwace komai nawa?"
Bude baki tayi zata rama taji Alh Sule ya fito sai ta soma kuka tana bawa Haj Mara hakuri. Harda cewa idan saboda zuwansu ne zasu koma Abuja nan ba da dadewa ba.
Alh Sule yana saukowa ya kamata da fada sosai da ja mata kunne babu ruwanta da iyalinsa.
Mamaki ne ya hanata magana kawai ta bi bayan BB tana hawayen zuci.
*****
Kwana biyu da zuwan Dahiru tun ranar Qareeba ta dena walwala a gidan. Dr Tani ta sami maigidanta tace lokaci yayi da zasu nema mata lafiya a ajiye boko a gefe.
"Neman lafiya wane iri?" Yace yana kallonta.
"Daddy na tabbatar Qareeba aljanu gareta irin masu hana auren nan. Idan ba haka ba wane dalili zaisa ta kai har yanzu babu aure babu mijin auren a hannu"
Bayan gajeren nazari ya amince da bukatarta don shima ya gaji da gorin 'yan uwa. Abokansa ma wasu sukan yi masa maganar tun yana bada amsa har yayi shiru.
Maigadinsu suka sanarwa saboda ustazu ne. Washegari sai gashi da malami aka zo aka rinka yi mata karatu harda hayaki. Malamin gudun kada ace baiyi komai ba ya zaro bulala zai fara lafta mata wai aljanun masu taurin kai ne. Tana ganin haka ta tashi a guje ta koma ciki.
Bayan 'yan kwanaki ta sami Dr Tani har daki tace ita dai tana son aure tunda Dahirun bai samu ba su taimaka su sama mata miji.