Sashe 24
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mu kuma aikin gini mukeyi a nan an kusa gamawa"
Addu'ar gamawa lafiya Dahiru yayi har ya juya zai tafi mutumin ya dakatar dashi suka je masallaci tare. Bayan sunyi sallah Dahiru yace zai shiga ya karbi abincinsa ya wuce gida. Mutumin yace to yana jiransa.
Ko da ya fito baiga yaron ba sai yayi zaton ko yana wurin ainihin masu gidan tunda ga dankareriyar mota an paka ta a wajen gate din. Da ya ga mutumin bai tafi ba sai yayi masa tayi abinci shi kuma yace ya koshi.
'Yar hira suka taba anan Dahiru yake ce masa gobe zai fara shiga aji daukar darasi
"Mu mun saba karatunmu a kauye nan sai fargabar gobe nake yi zan hadu da 'yan gayun birni"
Mutumin nan yayi ta dariya. Dahiru kansa mamakin yadda ya sake dashi yake yi da yaga Isha na neman yi yace masa zai wuce gida ya sake goge rigarsa don kada 'yan birni su raina shi.
"Dannan kace 'yan mata zaka nema ba karatu ba"
Shiru Dahiru yayi yana tunanin Mawadda "ina da matar da zan aura a kauyenmu, karatu kawai zanyi na koma wurinta"
Yanayin maganarsa kadai ya nuna akwai babbar damuwa a tattare da shi. Mutumin ya sami kansa da tausayin Dahiru sosai. Gashi matashi don yace masa shekarunsa ashirin da biyar amma ba girman kai ga son cigaba yazo yana aiki domin yayi karatu. Kati ya ciro a aljihunsa ya mikawa Dahiru.
"Ga wannan inji Kakan Khalil yaron da ka taimakawa yace na baka ka neme shi"
"Kakansa ne mai gidan nan kenan"
"Eh"
Godiya yayi masa sosai da korafin baici abincinsa ba sannan ya tashi yayi gaba. Mutum ya bishi da kallo, da farko kudi yayi niyar bashi amma 'yar hirarsu tasa ya shiga ransa.
*****
A daddafe iyalin Mal Fatihu suka karasa kwanakin da kotu ta diba kafin a cigaba da zama. Tsagwama da bakaken maganganu kullum yi ake. Hatta 'ya'yansa masu aure su Bilki basu tsira ba. Makota suyi musu dangin mazajensu suyi. Abu ya taru ya cakude musu.
A wannan lokacin Mawadda ji tayi inama bata taba rayuwar duniya ba. Ko kuma da BB ya keta mata haddi dama harda ranta ya hada. Bakar rana guda daya ta zame musu bala'i ita da duk wani makusanci nata. Hatta Dahiru wasu sun fara yawo da zancen kila shine yake nemanta suke neman dorawa dan iyayen gidanta.
Abubuwa sai gasu nan babu dadi ko kadan. Kannenta ma yanzu ko kofar gida basa so a aikesu.
Da sassafe suka shirya suka tafi Kano saboda Baba yace baya jindadin yadda yake rara gefe yana takurawa mutane akan wurin kwana.
Shabiyu za'a fara sauraren tasu karar amma ko da suka isa wurin goma da rabi kotu ta cika da 'yan kallo da 'yan jarida.
Haj Mara a gidan aminyarta ta kwana shi Dr Auwal maigidan bai san wainar da ake tonawa ba. Matarsa dai ta fada masa zata je kotu shaida akan wata yarinya yace sai ta dawo.
Da hillata Haj Mara tasa BB ya amince yazo gidan. Qareeba duniya kamar an bata sweet-kamfo jinta take tafi kowa sai wani yauki akeyi.
Shi kuma BB komai yana yi ne kawai saboda biyan bukatarsa na samun Mawadda. Sun gama shiri zasu tafi kotu yana jingine da mota Qareeba tana tsaye a gefensa suna jiran fitowar iyayensu sai ga Dahiru zai wuce.
Sauri yake yi ya gama aikinsa Danlami ya tsegumta masa yau za'a sake zaman shari'ar su Mawadda da karfe shabiyu. Da yake mutum ne mai shige-shige kuma yana yawan zuwa Kano yawo yasan court road din ya kwatanta masa. A ka'idar karatunsa ma yana da aji yau hudu zuwa shida amma bai damu ba ko zai rasa indai zai ganta.
Qareeba ta kalle shi ya kwaso shara zai wuce tace "kai Ahirin meye haka baka ganin Man dina bazaka gaishe shi ba"
Dahiru yayi banza kamar baiji ba ta kuwa daga murya "Dashiru mai ahirin baka ji na ne? Tsaya nan dalla can ko na fadawa Mummyna"
BB ya dan daga ido ya kalleta sai yake baki take da suka hada ido "Man kaga wannan shine Dashiru din da nake fada maka yace ahirin....hehehe..." tayi dariya ita a dole 'yan mata zata burge masoyi.
Dahiru ganin zasu bata masa lokaci yace "barka dai Man"
Qareeba ta cika da haushi "me yasa kake min haka ne, ni kadai nake kiransa Man meye naka na fada. Kada kace min a kauyancinka baka san akwai sunaye da ake warewa na kiran wanda ake so ba"
BB duk ta ishe shi da hayaniya ya rasa me ya zaunar dasu Hajiyarsa a ciki. Ji yayi ta sake cewa
"Man kasan 'irinsu Ahirin basu san komai na love ba har tausayi suke bani ga auren wuri. Kai Dashiru me kake kiran budurwarka ta kauye"
Har ransa tausayi ma take bashi saboda yana ganim yadda saurayin nata yake ta wani yatsina shi a dole ya hadu. Yasan idan baiyi yadda take so ba karshenta Mummynta ta hana shi fita idan ya nemi uzuri kafin lokacin laccarsa don har timetable dinsa tasa ya kawo mata.
Dan buga kafa ta soma na shagwaba tana kyabe baki "Man please mana kace ya fada maka muji muyi dariya"
BB ya tsani wannan suna na Man kamar ya bugeta ya dai maida hankalinsa ga Dahiru.
Shi kuma ganin haka yace "Qulqulatul qurabati nake kiranta. Zan iya tafiya ko"
Haba Qareeba dariya har da kaiwa kasa. Muryarta kuwa har bakin gate maigadi sai da ya jiyota. Dr. Tani suna doso wurin taji takaici ya rufeta har da kunyar idon Haj Mara. Ita kuwa nunawa tayi ba komai tunda bukatarta zata biya a kashe case ta tura danta wata kasar ta yakice Dr. Tani. Dan zamanta a gidan duk sun gundureta ita da 'ya'yan. Wai jiya gotai gotai dasu suka rinka fada lomar wa tafi girma ana cin abinci.
Dr Tani ta jefi Dahiru da kallon banza don tasan shi kadai ke kara kunna Qareeba tayi ta rashin hankali.
"Kai me kake a nan kamar mara aikin yi? Ka wuce yau nasan sai la'asar zaka shiga aji ga wanki can mun hada ka wankesu tas a goge zan bar sallahu a tada inji. Asabar ba sai kazo ba"
Uzurinsa ya gabatar mata yana da wurin zuwa ta haushi da fada harda cewa idan ba so yake ya bar aikin ba ya rufe mata baki. Duk bakincikinta dariyar da yasa Qareeba a gaban BB da babarsa.
Ba don yaso ba haka ya tafi yana jira su fita shima ya saci jiki ya fice.
*****
Lauyoyi sun gabatar da kawunansu sannan Alkali ya bukaci a cigaba. Wani matashi aka gabatar wanda yace shi abokin Na'ibi mai kiyos ne kuma shine ya ga Mawadda a dakinsa har ya sanar da Haj Mara.
Barista Shafa'atu tayi dariya "kuma kana ganinsu baka yi tunanin yin yekuwa jama'a suzo ka sami shaida ba ko ka kira wani da yasan Na'ibin sai uwardakin Mawadda ce kawai ta fado maka a rai?"
In-ina ya dan soma "saboda nasan zata dauki mataki ta hana ne"
"Ashe akwai alaka tsakaninka da Haj Marakisiyya kenan"
"Eh to....a'a babu kawai dai nasan a gidan Mawadda take kuma zata bata min aboki tunda da ba halinsa bane"
"Da gaskiyarka kuma. To zamu so ka kwatanta mana hanyar da ake bi daga gidan Hajiya Marakisiyya zuwa dakin Na'ibi" tayi maganar tana kallon Haj Mara wadda taji cikinta ya kulle.
Saurayin ya soma raba ido domin shi gaskiya ko Na'ibin bai taba gani ba hasali ma ba dan unguwar bane.
"Ni bansan gidan Hajiyar ba amma nasan dakin nasa"
"Kace kuma kasanta har kasan zata dauki mataki idan ka sanar da ita halin da mai aikinta take ciki"
"Objection my lord" cewar Barista Dalhatu. "Barista tana neman juya zancen shaidarmu. Babban abin nema shine ya gansu kuma yaje ya sanar da uwardakinta"
Alkali ya karbi korafinsa yace ta kiyaye. Jin haka tace zata gabatar da shaidarta wato Dr Tani.
Wata yar musabaha Dr Tani da Haj Mara suka yi sannan ta tashi taje ta tsaya. Iyayen Mawadda dukkansu da Mawadda suka zuba mata idanu.
"Dr Tani ko zaki iya fada mana meye aikinki da shekarunki a wannan sana'a"
Sunanta ta sake nanata musu da bayanin kanta a matsayin likita da ta kwashi shekaru ashirin da uku tana aiki. Gashi har asibiti gareta wanda gwamnati ta bawa lasisin aiki.
Barista Shafa'atu tace "My lord munji wace ce Dr Tani saboda ina so kotu tayi duba da nazari mai kyau game da shaidun da zata kawo"
Alkali Dawud ya gyada kai ita kuma taci gaba.
"Doctor muna bukatar kiyi mana bayani game da halin da kika sami Mawadda ranar da tazo asibitinku"
"Tazo asibitin ne da lalura ta rashin iya rike fitsari sosai sannan tace anyi mata fyade ne shine dalilin wannan lalura"
Magana take babu wani alamu na damuwa kai tsaye kamar wadda tazo wurin a bisa tilastawa. Yanayinta kadai ya dagawa Barista Shafa'atu hankali sai dai ta cigaba da tambayarta.
"Idan na fahimceki kenan kina nufin fyade yakan iya janyo sakin jijiyoyin jikin mace har ta kasa rike fitsari hakane?"
"Gaskiya kamar yadda kowa ya sani yoyon fitsari ana samunsa ne ta dalilin haihuwa, tsufa ko infection wato idan kwayoyin cuta suka shiga mafitsara. Ni a tsahon lokacin da na dauka ina aiki ban taba jin ance fyade ya zama sanadin yoyon fitsari ba"
Barista Shafa'atu tun a lokacin ta gane inda Dr Tani ta dosa jikinta yayi matukar yin sanyi. Ta daure tace "amma ba yoyo take yi sosai ba tunda kadan kadan yake fita wannan ba alama bace dake nuni da cewa abinda ya janyo shi bai kai haihuwa ba?"
"Ga takardu na gwajin da muka yi mata mun tabbatar ba infection bane yake damunta. Sauran bayani kuma mun dogara ne da abinda ta fada da bakinta. Shawarata a nan shine idan da hali a sake bincikenta ko ta taba haihuwa ko yunkurin zubar da cikin da yayi kwari..."
Wani kukan kura Ade tayi ta taso daga inda take ta nufi Dr Tani take tsaye tana kuka sosai "Dafta amanarmu zaki ci? Nawa suka biyaki zaki yiwa 'yata kazafi irin wannan"
Addu'ar gamawa lafiya Dahiru yayi har ya juya zai tafi mutumin ya dakatar dashi suka je masallaci tare. Bayan sunyi sallah Dahiru yace zai shiga ya karbi abincinsa ya wuce gida. Mutumin yace to yana jiransa.
Ko da ya fito baiga yaron ba sai yayi zaton ko yana wurin ainihin masu gidan tunda ga dankareriyar mota an paka ta a wajen gate din. Da ya ga mutumin bai tafi ba sai yayi masa tayi abinci shi kuma yace ya koshi.
'Yar hira suka taba anan Dahiru yake ce masa gobe zai fara shiga aji daukar darasi
"Mu mun saba karatunmu a kauye nan sai fargabar gobe nake yi zan hadu da 'yan gayun birni"
Mutumin nan yayi ta dariya. Dahiru kansa mamakin yadda ya sake dashi yake yi da yaga Isha na neman yi yace masa zai wuce gida ya sake goge rigarsa don kada 'yan birni su raina shi.
"Dannan kace 'yan mata zaka nema ba karatu ba"
Shiru Dahiru yayi yana tunanin Mawadda "ina da matar da zan aura a kauyenmu, karatu kawai zanyi na koma wurinta"
Yanayin maganarsa kadai ya nuna akwai babbar damuwa a tattare da shi. Mutumin ya sami kansa da tausayin Dahiru sosai. Gashi matashi don yace masa shekarunsa ashirin da biyar amma ba girman kai ga son cigaba yazo yana aiki domin yayi karatu. Kati ya ciro a aljihunsa ya mikawa Dahiru.
"Ga wannan inji Kakan Khalil yaron da ka taimakawa yace na baka ka neme shi"
"Kakansa ne mai gidan nan kenan"
"Eh"
Godiya yayi masa sosai da korafin baici abincinsa ba sannan ya tashi yayi gaba. Mutum ya bishi da kallo, da farko kudi yayi niyar bashi amma 'yar hirarsu tasa ya shiga ransa.
*****
A daddafe iyalin Mal Fatihu suka karasa kwanakin da kotu ta diba kafin a cigaba da zama. Tsagwama da bakaken maganganu kullum yi ake. Hatta 'ya'yansa masu aure su Bilki basu tsira ba. Makota suyi musu dangin mazajensu suyi. Abu ya taru ya cakude musu.
A wannan lokacin Mawadda ji tayi inama bata taba rayuwar duniya ba. Ko kuma da BB ya keta mata haddi dama harda ranta ya hada. Bakar rana guda daya ta zame musu bala'i ita da duk wani makusanci nata. Hatta Dahiru wasu sun fara yawo da zancen kila shine yake nemanta suke neman dorawa dan iyayen gidanta.
Abubuwa sai gasu nan babu dadi ko kadan. Kannenta ma yanzu ko kofar gida basa so a aikesu.
Da sassafe suka shirya suka tafi Kano saboda Baba yace baya jindadin yadda yake rara gefe yana takurawa mutane akan wurin kwana.
Shabiyu za'a fara sauraren tasu karar amma ko da suka isa wurin goma da rabi kotu ta cika da 'yan kallo da 'yan jarida.
Haj Mara a gidan aminyarta ta kwana shi Dr Auwal maigidan bai san wainar da ake tonawa ba. Matarsa dai ta fada masa zata je kotu shaida akan wata yarinya yace sai ta dawo.
Da hillata Haj Mara tasa BB ya amince yazo gidan. Qareeba duniya kamar an bata sweet-kamfo jinta take tafi kowa sai wani yauki akeyi.
Shi kuma BB komai yana yi ne kawai saboda biyan bukatarsa na samun Mawadda. Sun gama shiri zasu tafi kotu yana jingine da mota Qareeba tana tsaye a gefensa suna jiran fitowar iyayensu sai ga Dahiru zai wuce.
Sauri yake yi ya gama aikinsa Danlami ya tsegumta masa yau za'a sake zaman shari'ar su Mawadda da karfe shabiyu. Da yake mutum ne mai shige-shige kuma yana yawan zuwa Kano yawo yasan court road din ya kwatanta masa. A ka'idar karatunsa ma yana da aji yau hudu zuwa shida amma bai damu ba ko zai rasa indai zai ganta.
Qareeba ta kalle shi ya kwaso shara zai wuce tace "kai Ahirin meye haka baka ganin Man dina bazaka gaishe shi ba"
Dahiru yayi banza kamar baiji ba ta kuwa daga murya "Dashiru mai ahirin baka ji na ne? Tsaya nan dalla can ko na fadawa Mummyna"
BB ya dan daga ido ya kalleta sai yake baki take da suka hada ido "Man kaga wannan shine Dashiru din da nake fada maka yace ahirin....hehehe..." tayi dariya ita a dole 'yan mata zata burge masoyi.
Dahiru ganin zasu bata masa lokaci yace "barka dai Man"
Qareeba ta cika da haushi "me yasa kake min haka ne, ni kadai nake kiransa Man meye naka na fada. Kada kace min a kauyancinka baka san akwai sunaye da ake warewa na kiran wanda ake so ba"
BB duk ta ishe shi da hayaniya ya rasa me ya zaunar dasu Hajiyarsa a ciki. Ji yayi ta sake cewa
"Man kasan 'irinsu Ahirin basu san komai na love ba har tausayi suke bani ga auren wuri. Kai Dashiru me kake kiran budurwarka ta kauye"
Har ransa tausayi ma take bashi saboda yana ganim yadda saurayin nata yake ta wani yatsina shi a dole ya hadu. Yasan idan baiyi yadda take so ba karshenta Mummynta ta hana shi fita idan ya nemi uzuri kafin lokacin laccarsa don har timetable dinsa tasa ya kawo mata.
Dan buga kafa ta soma na shagwaba tana kyabe baki "Man please mana kace ya fada maka muji muyi dariya"
BB ya tsani wannan suna na Man kamar ya bugeta ya dai maida hankalinsa ga Dahiru.
Shi kuma ganin haka yace "Qulqulatul qurabati nake kiranta. Zan iya tafiya ko"
Haba Qareeba dariya har da kaiwa kasa. Muryarta kuwa har bakin gate maigadi sai da ya jiyota. Dr. Tani suna doso wurin taji takaici ya rufeta har da kunyar idon Haj Mara. Ita kuwa nunawa tayi ba komai tunda bukatarta zata biya a kashe case ta tura danta wata kasar ta yakice Dr. Tani. Dan zamanta a gidan duk sun gundureta ita da 'ya'yan. Wai jiya gotai gotai dasu suka rinka fada lomar wa tafi girma ana cin abinci.
Dr Tani ta jefi Dahiru da kallon banza don tasan shi kadai ke kara kunna Qareeba tayi ta rashin hankali.
"Kai me kake a nan kamar mara aikin yi? Ka wuce yau nasan sai la'asar zaka shiga aji ga wanki can mun hada ka wankesu tas a goge zan bar sallahu a tada inji. Asabar ba sai kazo ba"
Uzurinsa ya gabatar mata yana da wurin zuwa ta haushi da fada harda cewa idan ba so yake ya bar aikin ba ya rufe mata baki. Duk bakincikinta dariyar da yasa Qareeba a gaban BB da babarsa.
Ba don yaso ba haka ya tafi yana jira su fita shima ya saci jiki ya fice.
*****
Lauyoyi sun gabatar da kawunansu sannan Alkali ya bukaci a cigaba. Wani matashi aka gabatar wanda yace shi abokin Na'ibi mai kiyos ne kuma shine ya ga Mawadda a dakinsa har ya sanar da Haj Mara.
Barista Shafa'atu tayi dariya "kuma kana ganinsu baka yi tunanin yin yekuwa jama'a suzo ka sami shaida ba ko ka kira wani da yasan Na'ibin sai uwardakin Mawadda ce kawai ta fado maka a rai?"
In-ina ya dan soma "saboda nasan zata dauki mataki ta hana ne"
"Ashe akwai alaka tsakaninka da Haj Marakisiyya kenan"
"Eh to....a'a babu kawai dai nasan a gidan Mawadda take kuma zata bata min aboki tunda da ba halinsa bane"
"Da gaskiyarka kuma. To zamu so ka kwatanta mana hanyar da ake bi daga gidan Hajiya Marakisiyya zuwa dakin Na'ibi" tayi maganar tana kallon Haj Mara wadda taji cikinta ya kulle.
Saurayin ya soma raba ido domin shi gaskiya ko Na'ibin bai taba gani ba hasali ma ba dan unguwar bane.
"Ni bansan gidan Hajiyar ba amma nasan dakin nasa"
"Kace kuma kasanta har kasan zata dauki mataki idan ka sanar da ita halin da mai aikinta take ciki"
"Objection my lord" cewar Barista Dalhatu. "Barista tana neman juya zancen shaidarmu. Babban abin nema shine ya gansu kuma yaje ya sanar da uwardakinta"
Alkali ya karbi korafinsa yace ta kiyaye. Jin haka tace zata gabatar da shaidarta wato Dr Tani.
Wata yar musabaha Dr Tani da Haj Mara suka yi sannan ta tashi taje ta tsaya. Iyayen Mawadda dukkansu da Mawadda suka zuba mata idanu.
"Dr Tani ko zaki iya fada mana meye aikinki da shekarunki a wannan sana'a"
Sunanta ta sake nanata musu da bayanin kanta a matsayin likita da ta kwashi shekaru ashirin da uku tana aiki. Gashi har asibiti gareta wanda gwamnati ta bawa lasisin aiki.
Barista Shafa'atu tace "My lord munji wace ce Dr Tani saboda ina so kotu tayi duba da nazari mai kyau game da shaidun da zata kawo"
Alkali Dawud ya gyada kai ita kuma taci gaba.
"Doctor muna bukatar kiyi mana bayani game da halin da kika sami Mawadda ranar da tazo asibitinku"
"Tazo asibitin ne da lalura ta rashin iya rike fitsari sosai sannan tace anyi mata fyade ne shine dalilin wannan lalura"
Magana take babu wani alamu na damuwa kai tsaye kamar wadda tazo wurin a bisa tilastawa. Yanayinta kadai ya dagawa Barista Shafa'atu hankali sai dai ta cigaba da tambayarta.
"Idan na fahimceki kenan kina nufin fyade yakan iya janyo sakin jijiyoyin jikin mace har ta kasa rike fitsari hakane?"
"Gaskiya kamar yadda kowa ya sani yoyon fitsari ana samunsa ne ta dalilin haihuwa, tsufa ko infection wato idan kwayoyin cuta suka shiga mafitsara. Ni a tsahon lokacin da na dauka ina aiki ban taba jin ance fyade ya zama sanadin yoyon fitsari ba"
Barista Shafa'atu tun a lokacin ta gane inda Dr Tani ta dosa jikinta yayi matukar yin sanyi. Ta daure tace "amma ba yoyo take yi sosai ba tunda kadan kadan yake fita wannan ba alama bace dake nuni da cewa abinda ya janyo shi bai kai haihuwa ba?"
"Ga takardu na gwajin da muka yi mata mun tabbatar ba infection bane yake damunta. Sauran bayani kuma mun dogara ne da abinda ta fada da bakinta. Shawarata a nan shine idan da hali a sake bincikenta ko ta taba haihuwa ko yunkurin zubar da cikin da yayi kwari..."
Wani kukan kura Ade tayi ta taso daga inda take ta nufi Dr Tani take tsaye tana kuka sosai "Dafta amanarmu zaki ci? Nawa suka biyaki zaki yiwa 'yata kazafi irin wannan"