Sashe 63
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jikan kawun nata da aka aiko ya fada mata akwai abinci idan BB zai ci ya fita a guje ya tafi fadin hayaniyar da yake ji a dakin.
Kuka take kamar ranta zai fita saboda ba dukan wasa yake mata ba. Muryarta har ta shake saboda rokonsa kada ya keta haddin da yafi kowanne muni a gare shi. Da kyar ta lalubi fitilar da ta kashe ta kunna ta durkushe a kasa.
"Babawo ka dawo cikin hayyacinka don Allah nice Marakisiyya mahaifiyarka"
Kara bude idanuwansa yayi yaja tsaki "auuu ashe ma kece"
Suna haka taji muryar kawunta yana fada "Marakisiyya bude min kofar nan"
BB ya kalleta "a ina nake ne? Kada ki bude Hajiya 'yan sanda ne"
Bata saurare shi ba ta tashi zata bude ya damko hannunta ta saki ihu. Nan da nan samarin gidan suka yiwa kofar dukan maza sai gata tana lilo. Carko-carko akayi ana kallon kallon. Haj Mara dai rigarta kamar babu saboda BB tsargeta yayi sannan zanin duk ya tattare ya juye. Shi kuma gajeren wando ne kawai ya rage masa.
Salati aka dauka Kawunta ransa ya zo wuya "mutuniyar banza mutuniyar hofi ashe tsiyar da kuke shukawa kenan da dan naki shiyasa kowa ya juya muku baya. Allah wadaran wannan dabi'a kuma wallahi bazaku kwana min a gida ba"
Tana kuka kamar ranta zai fita ta hau yi masa bayanin cewa ba abinda yake zato bane. Tsawa ya daka mata har kokon ranta don dama mafadaci ne.
"Duk iskancin da yaron nan yake yi kina tarewa idan ba kuna naku a gefe bane ai yakamata ace kin tsawatar. Amma kinyi kunnen uwar shegu ke gaki wadda tafi kowa son da. Inace yanzu kin budewa kika yi saboda gudun tonon asiri. Nace ki kai shi dakin samari kin taho dashi naki tirrr da haihuwarki Mara"
Zaman dirshan tayi a kasa tana ji ana aibata ta kowa yaki sauraron bayaninta. Da BB yaga haka ya soma rashin kunya dama samarin a kagauce suke suka finciko shi suka hau duka ba ji ba gani karshe aka mika su ofishin Hisba.
******
A kan kujera Mawadda ta kwana ta dora kanta akan gadon daidai fuskarsa ga hawaye ya bushe mata. Dahiru ya bude ido yana ta kallonta. Goshinta ya sumbata ta bude ido da sauri tana tambayarsa jikinsa cikin kulawa.
"Mai jinya ta saki baki tana bacci har patient ya riga ta farkawa."
Murmushi tayi "bazanyi rigima da kai ba patient dina kai abin lallabawa ne"
Sallar asuba suka yi sannan ta jona musu ruwan wanka da heater din da ta sako a kayanta daga gida.
Jikinta babu kuzari sosai kamar ita ce mara lafiyar komai tana yi a sanyaye a dalilin fargabar yadda Baffa da Inna zasu dauki lamarin an kusa kashe musu da dominta. Yadda ta koma yasa shi jin babu dadi yace ta jawo kujera gaban gadon kusa dashi ta zauna.
"Meye yake damunki kuma, duk kinyi wani iri. Ko wuyanki ne na kula kina ta rikonsa tunda kika farka. Kwanciyar bata yi miki dadi ba" ya dora hannu a wurin ya soma murza mata jijiyar wuyan cikin nutsuwa.
Tun tana nokewa saboda rashin jindadin wuyan da zafi har ta sake da ta fara jin yana warwarewa. Kallonta yake yi har ya gama ta jujjuya wuyan tana dan murmushi.
"Nagode Yayanmu"
Ya kawar da kai "ni dai wallahi ba haka ake yi ba"
Dariya ya bata tasan ita ce mai masa wannan korafin "me akayi ba daidai ba?"
"Nine mara lafiyan amma kece kike langabewa kin barni da aikin jinya. Gaskiya bazan yarda ba"
Dadi taji ta fara tsokanarsa yau ta rama yadda yake mata.
"Sai kaji idan da dadi"
Tura baki yayi "sai kin biyani jinyata"
Ruwan wankan ta je ta kashe saboda ya tafasa ta dawo kusa da gadon ta tsaya "ayya sai hakuri babu wani biya da zanyi. Ga tawul zan sirka maka ruwa ka fara wanka kada a shigo bamuyi wanka ba"
Kwanciya ta ga yana shirin yi tace "yaya haka"
Ya dago yatsunsa biyu "nace sai kin biyani jinyata sai ki zabi dayan biyu. Ko dai kiyi min wankan nan ko kuma ki goyani."
Idanu ta zaro saboda mamaki sai kuma ta koma dariya "amma shagwabar taka harda rigima a ciki. Yanzu da wane bayan zan goya ka?"
Hannunta ya janyo ta dawo gabansa yana zaune ya zuro kafafunsa a kasa ya dora hannu a bayanta "wannan"
A take taji kunya ta runtse ido "kayi masa girma"
"Wankan fa?"
"Rufa min asiri"
"Kunya kike ji?"
Ta lumshe ido ya sunkuyar da kansa "Nima ina ji amma saboda lalura na roka kika ki. Ai shikenan"
Murmushi tayi bata ankara ba taji a hankali ya zaunar da ita a gabansa tsakiyar kafafunsa ya zura hannuwansa ta cikinta tare da dora kai a tsakanin wuyanta da kafada.
"Gashi kin goyani saura zani" yace yana kara karfin rikon da yayi mata don kada ta tashi. Dankwalinta ya zamo ta kasan hijab din jikinta ya daura musu daga bayansa zuwa cikinta ta rasa inda zata yi.
Ba karamar kunya taji ba shi kuwa ya sake lafewa a bayan nata wai bacci zaiyi. Ta daure tace ya tashi kafin ruwan ya huce.
"Ki rufe kofar dakin muje kiyi min don Allah Mawaddana...kinji. Bani da lafiya fa" ya marairaice mata.
"In rufe kofa kuma? so kake idan anzo an buga shiru ace...ace..." ta kasa karasawa.
Kanta ya dungure "Allah Ya shiryeki wato har kin fassara. Jikina inda na bugu nake so ki gasa min fa kike wani tunanin. Bawan Allah mai kafa daya da rabi salihi ne ba ruwansa"
Kwafa tayi ta tashi ta rufe kofar dakin ta dawo ta cire hijabinta ta mika masa sandunansa. Fuskarta babu alamun wasa tace.
"Tashi muje nayi maka"
Ya kalleta ya kalli kansa sai ya dan ja baya "me? Wankan?"
Ta sake hade rai "ba shi kake so ba da gasa jiki? Tashi muyi sauri nima sai nayi. Idan anzo anji kofar a rufe su jiramu kowa yasan jinyar amare sai hakuri"
Kamar gaske ya zaro ido "a gabana zakiyi wankan kuma kiyi min?"
Tawul dinta da yake cikin akwatin da ta hado musu kaya karami ta dauko "akwai wani abu ne?"
"Bazaki ji kunyata ba?"
"Ko digo" tace tana ware masa idanunta masu kada masa zuciya.
Mikewa yayi yana wani shu'umin murmushi da karfinsa har sai da yayi kara ya manta da kafar. Sandunan ta bashi yana gaba tana binsa yace "da nasan da haka kullum ciwon karya zanyi miki. Amma yanzu ma nagode I love you soooo much" da dokinsa yake tafiya.
Tana daga baya ta amsa "I love you too"
Yana shiga ta janyo kofar ta rufe shi ta waje tana dariya "kayi wanka idan ka gama kayi min magana in shigo in daddanna maka jiki da ruwan zafi"
"This is cheating" yace yana dariyar shima.
"Yayanmu?"
"Na'am" yadda ya amsa shi a dole yana fushi.
"I love you kaji banda mita kasan babu kyau surutu a bandaki"
Bai san haka zata ce ba ya hau murmushi sannan yayi wankan. Bayan ya gama taje ta gasa masa jiki ya ji dadin hakan kuwa sosai.
Yana shiryawa itama tayi nata wankan. Kafin takwas duk sun shirya sai ma bacci da ya sake daukesu. Kofar da aka buga ce ana sallama ta tayar da Mawadda. Muryar Inna da taji a kofar dakin tsoro ya ziyarci zuciyarta ta bude da fargabar da wace irin fuska zasu kalleta.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰26
*Batul Mamman*💖
Kana ganin Mawadda kasan ba karamin tsoro ne a ranta ba wanda Dahiru ya gano dalilinsa tun kafin ya tambayeta. Ga tsananin mamakinta Inna tana shigowa kallonta tayi cike da tausayi.
"Mawadda ya naga kin fada firgicin kwana guda har kinyi kashin wuya. Hakuri zaku yi da jarabawar rayuwa watarana zaku wayi gari kamar ba'ayi ba"
Sanyi ne ya ratsa zuciyarta ta rinka tasbihi ga Allah domin Ya sani ta kwana da tararrabin haduwa da su Innar sai gashi abin yazo ba yadda tayi tsammani ba.
Durkusawa tayi ta gaisheta kanta a kasa tana jin hawaye na barazanar sauko mata. Ita kanta Innar taji yadda muryarta take rawa ta kama hannuwanta ta tayar da ita.
"Ki sakawa zuciyarki hakuri domin sai kinyi hakan ne zaki iya kulawa da mijinki. Kuka ba naki bane tunda kin sani ko ba jima ko ba dade wannan tsinannen yaro sai ya hadu da fushin Allah idan bai tuba ba."
Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi "nagode Inna"
Inna ta mayar mata da murmushin ta karasa gaban gadon inda Dahiru yake zaune yana kallonsu. Farincikinsa a lokacin ya sassauta masa radadin bacin ran zuciyarsa da ma ciwukan jikinsa. Kafin yayi magana Baffa da Ummiyo suka shigo daga ciki Mawadda ta gaishe da Baffan shima ya jajanta mata tare da karfafa mata gwiwa cike da kulawa. Ummiyo ta kasa kallon Mawadda matsananciyar kunyar matar yayan nasu ta kamata. Rabonsu da haduwa tun kafin ta tafi aikatau Kaduna. Sanda ta dawo Tariwa bayan tsautsayin nan ya faru basu hadu ba har kuma maganar da ta fitar ta janyo aka hanata fita gabadaya.
Tunda Dahiru ya fadawa Mawadda yadda Ummiyo ta dauketa ta matsu su hadu. Yanzu da ta ga duk ta takura kanta sai ta saki fuska ta matsa ta riko hannunta. A dan firgice ta kalli Mawadda ita kuma tayi mata murmushi tana kallon Inna.
"Inna don Allah waye babba a shekaru ni da Ummiyo?"
Kallonta suka yi duk su biyun ita da Baffa suna dariya. Inna ta amsa mata "kece mana bare kuma yanzu girman naki ya karu"
Mawadda ta sake murmusawa "to sai ki gaisheni tunda kinji da kunnenki nice babba idan ba haka ba kuma duk inda muka hadu har kasa zan durkusa miki"
Ummiyo taja da baya da sauri sai ga hawaye "don Allah rufa min asiri abin sai yayi min yawa"
Hankalin Mawadda ya tashi ita da take kokarin ganin ta daidaita tsakaninsu "menene haka daga wasa"
Gefen mayafinta tasa tana goge hawaye "ki yafe min don Allah"
Dahiru da su Inna duka kallonsu suke yi. Shekara da shekaru Ummiyo tana fama da wannan damuwar saboda ta dorawa kanta laifin komai da ya biyo bayan rayuwar Mawadda. Shiyasa bata iya sakewa kamar da duk surutun ya tafi.
Kuka take kamar ranta zai fita saboda ba dukan wasa yake mata ba. Muryarta har ta shake saboda rokonsa kada ya keta haddin da yafi kowanne muni a gare shi. Da kyar ta lalubi fitilar da ta kashe ta kunna ta durkushe a kasa.
"Babawo ka dawo cikin hayyacinka don Allah nice Marakisiyya mahaifiyarka"
Kara bude idanuwansa yayi yaja tsaki "auuu ashe ma kece"
Suna haka taji muryar kawunta yana fada "Marakisiyya bude min kofar nan"
BB ya kalleta "a ina nake ne? Kada ki bude Hajiya 'yan sanda ne"
Bata saurare shi ba ta tashi zata bude ya damko hannunta ta saki ihu. Nan da nan samarin gidan suka yiwa kofar dukan maza sai gata tana lilo. Carko-carko akayi ana kallon kallon. Haj Mara dai rigarta kamar babu saboda BB tsargeta yayi sannan zanin duk ya tattare ya juye. Shi kuma gajeren wando ne kawai ya rage masa.
Salati aka dauka Kawunta ransa ya zo wuya "mutuniyar banza mutuniyar hofi ashe tsiyar da kuke shukawa kenan da dan naki shiyasa kowa ya juya muku baya. Allah wadaran wannan dabi'a kuma wallahi bazaku kwana min a gida ba"
Tana kuka kamar ranta zai fita ta hau yi masa bayanin cewa ba abinda yake zato bane. Tsawa ya daka mata har kokon ranta don dama mafadaci ne.
"Duk iskancin da yaron nan yake yi kina tarewa idan ba kuna naku a gefe bane ai yakamata ace kin tsawatar. Amma kinyi kunnen uwar shegu ke gaki wadda tafi kowa son da. Inace yanzu kin budewa kika yi saboda gudun tonon asiri. Nace ki kai shi dakin samari kin taho dashi naki tirrr da haihuwarki Mara"
Zaman dirshan tayi a kasa tana ji ana aibata ta kowa yaki sauraron bayaninta. Da BB yaga haka ya soma rashin kunya dama samarin a kagauce suke suka finciko shi suka hau duka ba ji ba gani karshe aka mika su ofishin Hisba.
******
A kan kujera Mawadda ta kwana ta dora kanta akan gadon daidai fuskarsa ga hawaye ya bushe mata. Dahiru ya bude ido yana ta kallonta. Goshinta ya sumbata ta bude ido da sauri tana tambayarsa jikinsa cikin kulawa.
"Mai jinya ta saki baki tana bacci har patient ya riga ta farkawa."
Murmushi tayi "bazanyi rigima da kai ba patient dina kai abin lallabawa ne"
Sallar asuba suka yi sannan ta jona musu ruwan wanka da heater din da ta sako a kayanta daga gida.
Jikinta babu kuzari sosai kamar ita ce mara lafiyar komai tana yi a sanyaye a dalilin fargabar yadda Baffa da Inna zasu dauki lamarin an kusa kashe musu da dominta. Yadda ta koma yasa shi jin babu dadi yace ta jawo kujera gaban gadon kusa dashi ta zauna.
"Meye yake damunki kuma, duk kinyi wani iri. Ko wuyanki ne na kula kina ta rikonsa tunda kika farka. Kwanciyar bata yi miki dadi ba" ya dora hannu a wurin ya soma murza mata jijiyar wuyan cikin nutsuwa.
Tun tana nokewa saboda rashin jindadin wuyan da zafi har ta sake da ta fara jin yana warwarewa. Kallonta yake yi har ya gama ta jujjuya wuyan tana dan murmushi.
"Nagode Yayanmu"
Ya kawar da kai "ni dai wallahi ba haka ake yi ba"
Dariya ya bata tasan ita ce mai masa wannan korafin "me akayi ba daidai ba?"
"Nine mara lafiyan amma kece kike langabewa kin barni da aikin jinya. Gaskiya bazan yarda ba"
Dadi taji ta fara tsokanarsa yau ta rama yadda yake mata.
"Sai kaji idan da dadi"
Tura baki yayi "sai kin biyani jinyata"
Ruwan wankan ta je ta kashe saboda ya tafasa ta dawo kusa da gadon ta tsaya "ayya sai hakuri babu wani biya da zanyi. Ga tawul zan sirka maka ruwa ka fara wanka kada a shigo bamuyi wanka ba"
Kwanciya ta ga yana shirin yi tace "yaya haka"
Ya dago yatsunsa biyu "nace sai kin biyani jinyata sai ki zabi dayan biyu. Ko dai kiyi min wankan nan ko kuma ki goyani."
Idanu ta zaro saboda mamaki sai kuma ta koma dariya "amma shagwabar taka harda rigima a ciki. Yanzu da wane bayan zan goya ka?"
Hannunta ya janyo ta dawo gabansa yana zaune ya zuro kafafunsa a kasa ya dora hannu a bayanta "wannan"
A take taji kunya ta runtse ido "kayi masa girma"
"Wankan fa?"
"Rufa min asiri"
"Kunya kike ji?"
Ta lumshe ido ya sunkuyar da kansa "Nima ina ji amma saboda lalura na roka kika ki. Ai shikenan"
Murmushi tayi bata ankara ba taji a hankali ya zaunar da ita a gabansa tsakiyar kafafunsa ya zura hannuwansa ta cikinta tare da dora kai a tsakanin wuyanta da kafada.
"Gashi kin goyani saura zani" yace yana kara karfin rikon da yayi mata don kada ta tashi. Dankwalinta ya zamo ta kasan hijab din jikinta ya daura musu daga bayansa zuwa cikinta ta rasa inda zata yi.
Ba karamar kunya taji ba shi kuwa ya sake lafewa a bayan nata wai bacci zaiyi. Ta daure tace ya tashi kafin ruwan ya huce.
"Ki rufe kofar dakin muje kiyi min don Allah Mawaddana...kinji. Bani da lafiya fa" ya marairaice mata.
"In rufe kofa kuma? so kake idan anzo an buga shiru ace...ace..." ta kasa karasawa.
Kanta ya dungure "Allah Ya shiryeki wato har kin fassara. Jikina inda na bugu nake so ki gasa min fa kike wani tunanin. Bawan Allah mai kafa daya da rabi salihi ne ba ruwansa"
Kwafa tayi ta tashi ta rufe kofar dakin ta dawo ta cire hijabinta ta mika masa sandunansa. Fuskarta babu alamun wasa tace.
"Tashi muje nayi maka"
Ya kalleta ya kalli kansa sai ya dan ja baya "me? Wankan?"
Ta sake hade rai "ba shi kake so ba da gasa jiki? Tashi muyi sauri nima sai nayi. Idan anzo anji kofar a rufe su jiramu kowa yasan jinyar amare sai hakuri"
Kamar gaske ya zaro ido "a gabana zakiyi wankan kuma kiyi min?"
Tawul dinta da yake cikin akwatin da ta hado musu kaya karami ta dauko "akwai wani abu ne?"
"Bazaki ji kunyata ba?"
"Ko digo" tace tana ware masa idanunta masu kada masa zuciya.
Mikewa yayi yana wani shu'umin murmushi da karfinsa har sai da yayi kara ya manta da kafar. Sandunan ta bashi yana gaba tana binsa yace "da nasan da haka kullum ciwon karya zanyi miki. Amma yanzu ma nagode I love you soooo much" da dokinsa yake tafiya.
Tana daga baya ta amsa "I love you too"
Yana shiga ta janyo kofar ta rufe shi ta waje tana dariya "kayi wanka idan ka gama kayi min magana in shigo in daddanna maka jiki da ruwan zafi"
"This is cheating" yace yana dariyar shima.
"Yayanmu?"
"Na'am" yadda ya amsa shi a dole yana fushi.
"I love you kaji banda mita kasan babu kyau surutu a bandaki"
Bai san haka zata ce ba ya hau murmushi sannan yayi wankan. Bayan ya gama taje ta gasa masa jiki ya ji dadin hakan kuwa sosai.
Yana shiryawa itama tayi nata wankan. Kafin takwas duk sun shirya sai ma bacci da ya sake daukesu. Kofar da aka buga ce ana sallama ta tayar da Mawadda. Muryar Inna da taji a kofar dakin tsoro ya ziyarci zuciyarta ta bude da fargabar da wace irin fuska zasu kalleta.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰26
*Batul Mamman*💖
Kana ganin Mawadda kasan ba karamin tsoro ne a ranta ba wanda Dahiru ya gano dalilinsa tun kafin ya tambayeta. Ga tsananin mamakinta Inna tana shigowa kallonta tayi cike da tausayi.
"Mawadda ya naga kin fada firgicin kwana guda har kinyi kashin wuya. Hakuri zaku yi da jarabawar rayuwa watarana zaku wayi gari kamar ba'ayi ba"
Sanyi ne ya ratsa zuciyarta ta rinka tasbihi ga Allah domin Ya sani ta kwana da tararrabin haduwa da su Innar sai gashi abin yazo ba yadda tayi tsammani ba.
Durkusawa tayi ta gaisheta kanta a kasa tana jin hawaye na barazanar sauko mata. Ita kanta Innar taji yadda muryarta take rawa ta kama hannuwanta ta tayar da ita.
"Ki sakawa zuciyarki hakuri domin sai kinyi hakan ne zaki iya kulawa da mijinki. Kuka ba naki bane tunda kin sani ko ba jima ko ba dade wannan tsinannen yaro sai ya hadu da fushin Allah idan bai tuba ba."
Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi "nagode Inna"
Inna ta mayar mata da murmushin ta karasa gaban gadon inda Dahiru yake zaune yana kallonsu. Farincikinsa a lokacin ya sassauta masa radadin bacin ran zuciyarsa da ma ciwukan jikinsa. Kafin yayi magana Baffa da Ummiyo suka shigo daga ciki Mawadda ta gaishe da Baffan shima ya jajanta mata tare da karfafa mata gwiwa cike da kulawa. Ummiyo ta kasa kallon Mawadda matsananciyar kunyar matar yayan nasu ta kamata. Rabonsu da haduwa tun kafin ta tafi aikatau Kaduna. Sanda ta dawo Tariwa bayan tsautsayin nan ya faru basu hadu ba har kuma maganar da ta fitar ta janyo aka hanata fita gabadaya.
Tunda Dahiru ya fadawa Mawadda yadda Ummiyo ta dauketa ta matsu su hadu. Yanzu da ta ga duk ta takura kanta sai ta saki fuska ta matsa ta riko hannunta. A dan firgice ta kalli Mawadda ita kuma tayi mata murmushi tana kallon Inna.
"Inna don Allah waye babba a shekaru ni da Ummiyo?"
Kallonta suka yi duk su biyun ita da Baffa suna dariya. Inna ta amsa mata "kece mana bare kuma yanzu girman naki ya karu"
Mawadda ta sake murmusawa "to sai ki gaisheni tunda kinji da kunnenki nice babba idan ba haka ba kuma duk inda muka hadu har kasa zan durkusa miki"
Ummiyo taja da baya da sauri sai ga hawaye "don Allah rufa min asiri abin sai yayi min yawa"
Hankalin Mawadda ya tashi ita da take kokarin ganin ta daidaita tsakaninsu "menene haka daga wasa"
Gefen mayafinta tasa tana goge hawaye "ki yafe min don Allah"
Dahiru da su Inna duka kallonsu suke yi. Shekara da shekaru Ummiyo tana fama da wannan damuwar saboda ta dorawa kanta laifin komai da ya biyo bayan rayuwar Mawadda. Shiyasa bata iya sakewa kamar da duk surutun ya tafi.