Sashe 56
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanun Dahiru ne suka kara girma saboda wata idea da ta fado masa. Shi kadai yake ayyanawa a ransa lokaci yayi da Anti Qareeba zata hadu da Man.
Suna bakin mota da Inna yake tambayarta game da rashin zuwan Ummiyo.
"Kaima kasan dalili dai"
"In sha Allahu har tsakar dakinta zan kai Mawadda komai ya wuce"
******
Sahad ya wuce ya siyo kayan da yake tunanin suna bukata. Sauran ko nan da sati sai ya fita da Mawadda su saya ko tayi masa list. Daga nan ya tsaya ya sayi kayan miya da nama. Dariya abin ya bashi wai cefane.
Mawadda tana zaune a falo tayi kwalliya cikin wani material mai santsi anyi mata gown me siririn hannu. Irin daurin nan na murde jelar dankwali ta gaba a zagaya dashi daga bari daya tayi. Tayi matukar kyau kamar a sace. Gidan kuwa tun daga kofar hawa saman yake zuba kamshi.
Dahiru na tsayuwa da mota ya fita da sauri yana burin saka matarsa a ido. Da sauri ya hau saman yana bude kofa ya ganta tana fitowa daga daki.
Tamkar numfashinsa zai tsaya tsabar kyaun da tayi masa. A tare suka sakarwa juna murmushi ta ware mayafin da ta dauko da niyar idan ya dawo ta yafa saboda haka kawai taji kuma nauyin zama da rigar.
"Kada ki yafa ki bata min kwalliya mana" yace yana ware mata hannuwansa ta taho gare shi.
Dage gira tayi tana dariya "Yanzu a Gwaggo nake sai ka karaso mu gaisa ka sami wuri ka zauna"
Dariya yayi harda hamdala sannan ya nufota gadan-gadan. Bayan kujera ta koma da sauri ya biyota tana gudu tsakanin kujeru.
"Yayanmu ba kyau wayo Gwaggo nace fa"
Yana bayan kujera ita kuma ta zagayo gaban yace "haba Gwaggo don Allah ki tsaya duk na gaji"
"To ita Gwaggo ana rungumeta ne?" Ta turo baki.
"In kinji runguma daya kenan. Tsakaninmu da Gwaggonni rungume-rungume ne. Haka ake yi idan an gansu har kwanciya ake yi a jikinsu"
"To waye ba'a rungumewa?"
Ya dan kalli sama "amare saboda kowa ya sansu da kunya"
"Wayo kake son yi min to ban yarda ba"
Kai ta ga ya dukar "na hakura bari na koma akwai kaya a motar da ban dauko ba"
Da jan kafa ya soma tafiya har ya kusa kofa ta bishi da sauri ta kamo hannunsa. Wani abu suka ji duka su biyun ya juyo yana kallonta.
Daurewa tayi tace "rabin minti a matar Dahiru"
Wani irin kallo yayi mata mai tattare da soyayya da kauna.
"Kin tabbata?"
"Ko in fasa?"
"Maganar farko Sarki yake karba."
Hannun nata da ta rikeshi da shi ya janyo ta fada jikinsa. Wata kyakkyawar runguma yayi mata suna jin bugun zukatan juna.
Muryarta a sanyaye tace "rabin minti ya cika"
"Me ki kace?"
"Ra...."
Hadiye kalmar tayi lokacin da ya hade bakinsa da nata. Sun dauki lokaci a cikin yanayin da su kansu basu san yadda zasu fassara shi ba.
Ya dago kai yana neman idanunta ta rufe su.
"Kunya?"
Ta gyada kai tana kara hannunwanta akan fuskarta.
"Nima haka" yace yana rufe tashi fuskar.
Sosai taji kunyarsa ta juya bayanta ya tsaya yana kallonta daga sama har kasa yana dada godewa Allah da Ya bashi ita.
Sauka yayi ya dauko ledoji biyu da hannu daya. Tana gani tazo ta karba sai ta koma bakin benen idan ya dauko sai ta karba har suka gama hawowa dasu.
Daukar komai tayi tana kaishi inda ya dace shi kuma ya tafi yayi wanka. Yadda take aikin tana tunanin Dahiru haka yake shiryawa yana tunaninta da jin kewarta ta dame shi kamar wadda bata gidan.
Kananun kaya ya saka ya fito bata falo amma ga abinci akan dinning table.
Kitchen ya shiga tana gaban sink tana wanke nama.
"A ina muka sami abinci?"
"Wani yaro ne yace inji Haj Mama"
"Allah Ya saka musu da alkhairi."
"Amin"
Shiru taji na dan lokaci kafin ta juyo taji shi a tsaye a bayanta.
Wani iri taji zata motsa ya sauko da fuskarsa daidai kunnenta yana mata magana kamar mai rada "apron zan saka miki kada ki bata kayanki"
Zura mata yayi ta saman sannan ya janyota jikinsa ya daure mata igiyar a kugunta.
Dena komai tayi saboda yadda take ji a lokacin ya dora kansa a kafadarta tare da zagaye hannuwansa a cikinta "cigaba da aikin Matar Dahiru"
Da kyar tace "uhmmm na koma Yaya"
"Da wuri haka ba notice"
"Eh ni dai na koma" tasan idan suka cigaba da zama a haka da wuya ta iya karasa aikin. Soyayyarsa na ranta da kuma fargabar da take kasan zuciyarta.
"A bani rabin minti please"
Wuyanta taji yana sumbata ko ta ina sannan ya daure ya rabu da ita ba don yaso ba.
"Yaya in tayaki?"
"Jeka kaci abinci" ta kakaro maganar da kyar.
"Mawadda ina son ki!"
"Wallahi nima ina sonka Yayanmu" ta fada tana kallonsa.
Kallon juna suka tsaya yi kafin ta nuna masa kofa da yatsanta.
"Ko baki ce ba tafiya zanyi ko don tseratar da kaina daga soyewa"
"Me zai soyaka ana zaune kalau?"
"Ke mana da idanunki masu hanani sukuni"
Kofar ta sake nuna masa ya fice yana dariya ita kuma ta cigaba da aikinta cikin tunanin mijinta abin son ta Dahiru.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰24
*Batul Mamman*💖
Annurin fuskarta ne ya bace bat kamar anyi ruwa an dauke ta hade rai "me kace?"
Dahiru an sami abinda ake so ya wani kashingida akan kujera ya basar "cewa nayi zamu je neman auren Anti Qareeba"
Wani abu taji ya tokare mata a wuya ta tashi ta shige daki ta barshi a wurin. Shafa kansa yayi wanda gashinsa irin na Fulani da suka gada wurin mahaifinsu har ya fara taruwa ya ce "Allah nagode Maka Mawaddata tana sona"
Kusan minti uku tana daki tana kuka. Aure ko wata bai cika ba Dahiru yake fada mata zaije neman aure. Don karfin hali harda cewa taje wurin Nawal wato ma dare zasu raba. Yanzu haka Attahir zaiyi mata duk irin girmamawar da take masa. Shi kuma Bilya karshenta matarsa ce ta fada masa tayi mata ba daidai ba da suka zo shine zaice ayi mata kishiya. Allah Sarki rayuwarta daga wannan sai wannan. Amma tayi alkawarin daurewa bazata taba bijirewa Dahiru ba. Wani matsanancin tausayin kanta ne ya kara kamata ta kifa kai akan filo tana kuka haikan kamar yau za'a kawo mata amaryar.
Dahiru ya taso yana rangaji abinsa don shi idan ya ga alamun kishinsa a idanun Mawadda wani kara sonta yake ji. Kukanta ya jiyo kafin ya bude kofar yaji gabansa ya fadi. Da sauri ya tura kofar ya ganta kwance a tsakiyar gadon tayi rub da ciki sai sautin kuka ke tashi.
Gadon ya hau yayi kokarin juyata ta makale jiki.
"Subhanallahi Mawadda me ya sameki?"
Shiru tayi tana mamakin rainin wayo na maza. Yanzun nan ya juyar mata da duniyar farincikinta shine kuma yake tambayar me ya faru.
"Don Allah fada min. Baki da lafiya ne?"
Nan ma babu amsa. Duk yadda zaiyi taki shiru sai da kyar ne ma ya samu tace masa ya rabu da ita ya tafi wurin wadda yake so. Sai lokacin ya harbo jirginta ya danne dariyarsa ya gyara zama daga gefenta ya bude baki sai jiyo shi tayi kamar yana kuka.
Da farko ta zaci wasa ne ta kyale shi sai daga baya taji ya bude murya yana neman cika mata kunne. Jiki na rawa ta tashi ta ma manta da nata kukan "menene?"
Kara sauti yayi ta saka hannu akan bakinsa da sauri ta toshe ga nata hawayen na zuba cikin muryar kuka tace "Yayanmu me ya sameka kuma?"
Ya kwabe kyakkyawar fuskarsa ma'abociyar saje wanda ya hade duka gefen fuskarsa.
"Ba ke bace kike kuka kuma na tambayeki kinki yi min magana"
Harara ta dalla masa idanun nan kamar su fado ya daure iyakar dauriya kada yayi mata dariya.
"Kishiya fa kace zaka yi min ba dole nayi kuka ba" ta fada tana turo baki.
Sake bude baki yayi harda daga murya ta dora hannu a ka tana salati "so kake a jiyo mu ne?"
"Gara wasu daga waje su zo su rarrashemu duka mu biyun tunda ni baki son nawa"
Hawayenta ta goge da sauri ta tattaro wani murmushin dole ta yaba a fuskarta "na dena don Allah kaima kayi shiru idan aka shigo ai kunya zaka bani"
"Saboda kada kiji kunya kike son nayi shiru....Allah Sarki Dahiru bawan Allah" matso kwalla yake ta son yi abu ta gagara yana ta kikkifta idanu.
"Ba haka bane, ai kai dinne kukan naka har yafi nawa"
Yatsanta karami ya kama ya murda da nasa yana murmyshi "na dena amma kiyi min alkawarin kin dena zama kina kuka ke kadai."
"Nayi" tace ba don ta so ba.
"Ranar da ki ka karya idan na kamaki hukuncinki shine nima kukan zan tayaki in bude murya banda su Attahir makotan hagu da dama duk sai sunji sun shigo"
Ta zaro idanu "kace Allah"
Ya matso kusa da ita "ko a gwada ne?"
Girgiza kai tayi da sauri "rufa min asiri"
Janyota yayi jikinsa suka kwanta ya rungumeta "kukan me kike yi to daga tambayata ina zani?"
Sai da taja hanci ita a dole abar tausayi tace "aure kace min zaka nema na Anti Qareeba anjima"
"Don nace zani neman aurenta ba ina nufin nemawa kaina ba. Solidarity zanyi mata na hadata da Yayanmu Bilya"
Dariya ce ta kwacewa Mawadda farincikinta bai buya ta tashi ta zauna ta goge hawayenta tas "Yayanmu ka rinka bayani dalla-dalla ko don gaba. Kaine baka yi yadda zan fahimta ba amma yanzu komai ya wuce kamar iska"
Hannunta ya riko ta fada kansa gabadayanta fuskokinsu na kallon juna "don Allah kema kina jin yadda nake ji akanki? Sonki nake sosai"
Bayan hannunta tasa ta shafi gefen fuskarsa "nima haka"
Ya sake narke mata a jiki "Kema me?"
"Abinda kace mana"
Noke kafada yayi yana kara matseta "ni gaskiya a'a ki fada yadda na fada"
Kallonsa tayi yadda ya koma mata shagwababbe tun bayan aurensu. Duk wani ture turen baki ya iya ya sata yin abu ko babu niyya.
Suna bakin mota da Inna yake tambayarta game da rashin zuwan Ummiyo.
"Kaima kasan dalili dai"
"In sha Allahu har tsakar dakinta zan kai Mawadda komai ya wuce"
******
Sahad ya wuce ya siyo kayan da yake tunanin suna bukata. Sauran ko nan da sati sai ya fita da Mawadda su saya ko tayi masa list. Daga nan ya tsaya ya sayi kayan miya da nama. Dariya abin ya bashi wai cefane.
Mawadda tana zaune a falo tayi kwalliya cikin wani material mai santsi anyi mata gown me siririn hannu. Irin daurin nan na murde jelar dankwali ta gaba a zagaya dashi daga bari daya tayi. Tayi matukar kyau kamar a sace. Gidan kuwa tun daga kofar hawa saman yake zuba kamshi.
Dahiru na tsayuwa da mota ya fita da sauri yana burin saka matarsa a ido. Da sauri ya hau saman yana bude kofa ya ganta tana fitowa daga daki.
Tamkar numfashinsa zai tsaya tsabar kyaun da tayi masa. A tare suka sakarwa juna murmushi ta ware mayafin da ta dauko da niyar idan ya dawo ta yafa saboda haka kawai taji kuma nauyin zama da rigar.
"Kada ki yafa ki bata min kwalliya mana" yace yana ware mata hannuwansa ta taho gare shi.
Dage gira tayi tana dariya "Yanzu a Gwaggo nake sai ka karaso mu gaisa ka sami wuri ka zauna"
Dariya yayi harda hamdala sannan ya nufota gadan-gadan. Bayan kujera ta koma da sauri ya biyota tana gudu tsakanin kujeru.
"Yayanmu ba kyau wayo Gwaggo nace fa"
Yana bayan kujera ita kuma ta zagayo gaban yace "haba Gwaggo don Allah ki tsaya duk na gaji"
"To ita Gwaggo ana rungumeta ne?" Ta turo baki.
"In kinji runguma daya kenan. Tsakaninmu da Gwaggonni rungume-rungume ne. Haka ake yi idan an gansu har kwanciya ake yi a jikinsu"
"To waye ba'a rungumewa?"
Ya dan kalli sama "amare saboda kowa ya sansu da kunya"
"Wayo kake son yi min to ban yarda ba"
Kai ta ga ya dukar "na hakura bari na koma akwai kaya a motar da ban dauko ba"
Da jan kafa ya soma tafiya har ya kusa kofa ta bishi da sauri ta kamo hannunsa. Wani abu suka ji duka su biyun ya juyo yana kallonta.
Daurewa tayi tace "rabin minti a matar Dahiru"
Wani irin kallo yayi mata mai tattare da soyayya da kauna.
"Kin tabbata?"
"Ko in fasa?"
"Maganar farko Sarki yake karba."
Hannun nata da ta rikeshi da shi ya janyo ta fada jikinsa. Wata kyakkyawar runguma yayi mata suna jin bugun zukatan juna.
Muryarta a sanyaye tace "rabin minti ya cika"
"Me ki kace?"
"Ra...."
Hadiye kalmar tayi lokacin da ya hade bakinsa da nata. Sun dauki lokaci a cikin yanayin da su kansu basu san yadda zasu fassara shi ba.
Ya dago kai yana neman idanunta ta rufe su.
"Kunya?"
Ta gyada kai tana kara hannunwanta akan fuskarta.
"Nima haka" yace yana rufe tashi fuskar.
Sosai taji kunyarsa ta juya bayanta ya tsaya yana kallonta daga sama har kasa yana dada godewa Allah da Ya bashi ita.
Sauka yayi ya dauko ledoji biyu da hannu daya. Tana gani tazo ta karba sai ta koma bakin benen idan ya dauko sai ta karba har suka gama hawowa dasu.
Daukar komai tayi tana kaishi inda ya dace shi kuma ya tafi yayi wanka. Yadda take aikin tana tunanin Dahiru haka yake shiryawa yana tunaninta da jin kewarta ta dame shi kamar wadda bata gidan.
Kananun kaya ya saka ya fito bata falo amma ga abinci akan dinning table.
Kitchen ya shiga tana gaban sink tana wanke nama.
"A ina muka sami abinci?"
"Wani yaro ne yace inji Haj Mama"
"Allah Ya saka musu da alkhairi."
"Amin"
Shiru taji na dan lokaci kafin ta juyo taji shi a tsaye a bayanta.
Wani iri taji zata motsa ya sauko da fuskarsa daidai kunnenta yana mata magana kamar mai rada "apron zan saka miki kada ki bata kayanki"
Zura mata yayi ta saman sannan ya janyota jikinsa ya daure mata igiyar a kugunta.
Dena komai tayi saboda yadda take ji a lokacin ya dora kansa a kafadarta tare da zagaye hannuwansa a cikinta "cigaba da aikin Matar Dahiru"
Da kyar tace "uhmmm na koma Yaya"
"Da wuri haka ba notice"
"Eh ni dai na koma" tasan idan suka cigaba da zama a haka da wuya ta iya karasa aikin. Soyayyarsa na ranta da kuma fargabar da take kasan zuciyarta.
"A bani rabin minti please"
Wuyanta taji yana sumbata ko ta ina sannan ya daure ya rabu da ita ba don yaso ba.
"Yaya in tayaki?"
"Jeka kaci abinci" ta kakaro maganar da kyar.
"Mawadda ina son ki!"
"Wallahi nima ina sonka Yayanmu" ta fada tana kallonsa.
Kallon juna suka tsaya yi kafin ta nuna masa kofa da yatsanta.
"Ko baki ce ba tafiya zanyi ko don tseratar da kaina daga soyewa"
"Me zai soyaka ana zaune kalau?"
"Ke mana da idanunki masu hanani sukuni"
Kofar ta sake nuna masa ya fice yana dariya ita kuma ta cigaba da aikinta cikin tunanin mijinta abin son ta Dahiru.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰24
*Batul Mamman*💖
Annurin fuskarta ne ya bace bat kamar anyi ruwa an dauke ta hade rai "me kace?"
Dahiru an sami abinda ake so ya wani kashingida akan kujera ya basar "cewa nayi zamu je neman auren Anti Qareeba"
Wani abu taji ya tokare mata a wuya ta tashi ta shige daki ta barshi a wurin. Shafa kansa yayi wanda gashinsa irin na Fulani da suka gada wurin mahaifinsu har ya fara taruwa ya ce "Allah nagode Maka Mawaddata tana sona"
Kusan minti uku tana daki tana kuka. Aure ko wata bai cika ba Dahiru yake fada mata zaije neman aure. Don karfin hali harda cewa taje wurin Nawal wato ma dare zasu raba. Yanzu haka Attahir zaiyi mata duk irin girmamawar da take masa. Shi kuma Bilya karshenta matarsa ce ta fada masa tayi mata ba daidai ba da suka zo shine zaice ayi mata kishiya. Allah Sarki rayuwarta daga wannan sai wannan. Amma tayi alkawarin daurewa bazata taba bijirewa Dahiru ba. Wani matsanancin tausayin kanta ne ya kara kamata ta kifa kai akan filo tana kuka haikan kamar yau za'a kawo mata amaryar.
Dahiru ya taso yana rangaji abinsa don shi idan ya ga alamun kishinsa a idanun Mawadda wani kara sonta yake ji. Kukanta ya jiyo kafin ya bude kofar yaji gabansa ya fadi. Da sauri ya tura kofar ya ganta kwance a tsakiyar gadon tayi rub da ciki sai sautin kuka ke tashi.
Gadon ya hau yayi kokarin juyata ta makale jiki.
"Subhanallahi Mawadda me ya sameki?"
Shiru tayi tana mamakin rainin wayo na maza. Yanzun nan ya juyar mata da duniyar farincikinta shine kuma yake tambayar me ya faru.
"Don Allah fada min. Baki da lafiya ne?"
Nan ma babu amsa. Duk yadda zaiyi taki shiru sai da kyar ne ma ya samu tace masa ya rabu da ita ya tafi wurin wadda yake so. Sai lokacin ya harbo jirginta ya danne dariyarsa ya gyara zama daga gefenta ya bude baki sai jiyo shi tayi kamar yana kuka.
Da farko ta zaci wasa ne ta kyale shi sai daga baya taji ya bude murya yana neman cika mata kunne. Jiki na rawa ta tashi ta ma manta da nata kukan "menene?"
Kara sauti yayi ta saka hannu akan bakinsa da sauri ta toshe ga nata hawayen na zuba cikin muryar kuka tace "Yayanmu me ya sameka kuma?"
Ya kwabe kyakkyawar fuskarsa ma'abociyar saje wanda ya hade duka gefen fuskarsa.
"Ba ke bace kike kuka kuma na tambayeki kinki yi min magana"
Harara ta dalla masa idanun nan kamar su fado ya daure iyakar dauriya kada yayi mata dariya.
"Kishiya fa kace zaka yi min ba dole nayi kuka ba" ta fada tana turo baki.
Sake bude baki yayi harda daga murya ta dora hannu a ka tana salati "so kake a jiyo mu ne?"
"Gara wasu daga waje su zo su rarrashemu duka mu biyun tunda ni baki son nawa"
Hawayenta ta goge da sauri ta tattaro wani murmushin dole ta yaba a fuskarta "na dena don Allah kaima kayi shiru idan aka shigo ai kunya zaka bani"
"Saboda kada kiji kunya kike son nayi shiru....Allah Sarki Dahiru bawan Allah" matso kwalla yake ta son yi abu ta gagara yana ta kikkifta idanu.
"Ba haka bane, ai kai dinne kukan naka har yafi nawa"
Yatsanta karami ya kama ya murda da nasa yana murmyshi "na dena amma kiyi min alkawarin kin dena zama kina kuka ke kadai."
"Nayi" tace ba don ta so ba.
"Ranar da ki ka karya idan na kamaki hukuncinki shine nima kukan zan tayaki in bude murya banda su Attahir makotan hagu da dama duk sai sunji sun shigo"
Ta zaro idanu "kace Allah"
Ya matso kusa da ita "ko a gwada ne?"
Girgiza kai tayi da sauri "rufa min asiri"
Janyota yayi jikinsa suka kwanta ya rungumeta "kukan me kike yi to daga tambayata ina zani?"
Sai da taja hanci ita a dole abar tausayi tace "aure kace min zaka nema na Anti Qareeba anjima"
"Don nace zani neman aurenta ba ina nufin nemawa kaina ba. Solidarity zanyi mata na hadata da Yayanmu Bilya"
Dariya ce ta kwacewa Mawadda farincikinta bai buya ta tashi ta zauna ta goge hawayenta tas "Yayanmu ka rinka bayani dalla-dalla ko don gaba. Kaine baka yi yadda zan fahimta ba amma yanzu komai ya wuce kamar iska"
Hannunta ya riko ta fada kansa gabadayanta fuskokinsu na kallon juna "don Allah kema kina jin yadda nake ji akanki? Sonki nake sosai"
Bayan hannunta tasa ta shafi gefen fuskarsa "nima haka"
Ya sake narke mata a jiki "Kema me?"
"Abinda kace mana"
Noke kafada yayi yana kara matseta "ni gaskiya a'a ki fada yadda na fada"
Kallonsa tayi yadda ya koma mata shagwababbe tun bayan aurensu. Duk wani ture turen baki ya iya ya sata yin abu ko babu niyya.