Sashe 20
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Shi dan kauye ko talaka ba mutum bane? Meyasa idan dan birni ya nemi kudi ake jinjina masa idan dan kauye ya nema yake zama kwadayayye? Masu kudin da mutanen birnin me suke yi mana domin inganta rayuwa? Ko nan da Jigawa ban taba zuwa ba amma ina da tabbacin ko ina a fadin duniyar nan akwai masu kudi kuma akwai masu yi musu aiki talakawa kauyawa irinmu. Haka Allah Yaso kuma haka Ya tsara duniyar arzikin wani yana karkashin wani. Idan munyi bara kuce zukatanmu sun mutu idan mun nemi halak da guminmu ace mun kasa rike talauci. Wannan wane irin son kai ne da rashin adalci? Mune 'yan dako mune leburori mune masu kaskantacciyar sana'a amma duk ba'a gani. Talauci yasa yaro sa'an jikanka zai tsaya ka bude masa kofa ya shiga mota yana binka da harara. Mu maza mun nema a waje matanmu kuma su nema a cikin gidajen aure. Kuna da mata maaikata, suna bukatar masu tayasu raino, gyaran gida ko girki. Idan ba kaddara ta rabo mace da gidan mijinta ba ai dai bakwayi tsammanin matan aurenmu ne zasu baro nasu kananan yaran a kauye su fito aikatau ba. Dole yaran namu da suka kawo karfi zamu turo. Babu mai zurfafa tunani yaga cewa banda abinci muma fa muna rashin lafiya kamar 'yan birni waye zai bamu kudin asibiti, lalura da dama ta kudi tana taso mana. Kai da kake cewa muna turasu neman kudin kayan daki waye yace maka don muna kauye shikenan idan mun tashi sai mu aurar da 'ya mu kaita da tabarma? Haka al'adar bahaushe take waye yaki ya sami wani abu da zai taimaka masa yaji dadin rayuwarsa? Komai namu sai ya zama laifi saboda bamu da galihu. Mu yini muna muku aikin karfi ku sallamemu da dubu uku karshen wata har kuna ganin ba karamin karamci kuka yi mana ba. Yaranmu suna kauye da kokarinsu talauci yasa basa iya wuce sakandire idan sunyi sa'ar zana jarabawa. Ni Fatihu bazan boye ba kuma bazan fasa fada ba mu daku muna bukatar juna ne domin taimakekeniya ta rayuwa. A cikinmu da cikin kowacce sana'a akwai nagari akwai bata gari. 'Yata Mawadda da duk sauran masu zuwa aikatau ba kiyayya ko rashin sanin ciwon kai yasa muke turo muku su ba. Yanayi ne na kuncin rayuwa....Wallahil Azim bazan taba yafewa wannan yaro ba, babu wata riba da zamu tsinta don mun batawa dan wasu suna"
Kafin ya karashe maganar kuka ma yake yi sosai hawaye har gaban malun-malun dinsa ya jike. Masu daukar rahoto da 'yan kallo da dama sun zubar da kwalla. Haka zalika iyalansa da suke tsaye a bakin kofar kotun.
*****
Dahiru zaune gaban yayansa Bilya yana ta juya cokali cikin abinci.
"Kayi hakuri kada ka batawa su Baffa rai akan mace Dahiru komai mai wucewa ne"
"Na sani Yayanmu amma bazan taba iya cire Mawadda daga zuciyata ba. Yau aka fara shiga kotun ya dace ace ina tare dasu amma kaga banma san wace kotu bace"
Bilya yana tausayin kaninsa sosai amma Inna tayi masa gargadi mai karfi akan ya tsawatar masa da batun auren don bazata taba yarda ba duk runtsi.
Kasa cin abincin Dahiru yayi ya tashi ya fita wurin wani mai shayi a layin da suka saba zama. Ana ta hira ya zurfafa a tunani yaji muryar Baba a lokacin da yake maidawa wasu martani. Mai kawo rahoton yace hakika wannan mutumi ya nusar da mutane da dama abinda suka manta game da na kasa dasu a kowane matakin rayuwa. Komai talauci, rashin ilimi da wayewa mutum, mutum ne abin darajawa saboda haka zasu cigaba da bibiyar wannan shari'a da akeyi a kotu mai lamba biyar Court road domin jin yadda zata kaya.
Har kuka Dahiru yayi yana jin wannan labarai. Tashi yayi ya bar wurin da surutun jama'a ya ishe shi akan kukan me yake yi.
Washegari da sassafe yaje gidan aikinsa yayi shara da gyaran filawa ko sallama baiyi da kowa ba ya kama hanyar tasha. Yayi babbar sa'a su Mal Fatihu tun jiya suka koma Tariwa. Kai tsaye gidansa ya wuce sai ya tuna bata gidan ya kama hanyar gidan kakaninta.
Lokacin shadaya na safe yana tsaye yana jiran yaron da ya tura sai ga Baffa shima yazo. Da mamaki Baffa yace "Dahiru saukar yaushe?"
Gaishe shi yayi yaga bai amsa ba yace "isowata kenan"
"Shine ka fara zuwa nan? Ashe duk maganar da muke yi maka bayan kunnenka take bi. To billahillazi kaji na rantse ban lamunce maka auren yarinyar nan ba ka nemi wata. Garin nan kwana akayi ana zancen shigarsu kotu jiya shine nazo jajanta masa naje gidansa ance yana nan ashe rabon na ganka ne."
Kamar yayi kuka ya dan duka "Baffa don Allah kayi hakuri yanzu ne take bukata ta bai kamata na juya...."
"Dahiru kada ka bari na sauke maka bacin raina. Ka wuce muje jajen ma na fasa tunda shima ya kasa gane zuru da kawaici idan kazo maimakon yace ka dena zuwa aure tsakaninku bazai yiwu ba"
Duk yadda Dahiru ke rokon Baffansa haka ya saka shi a gaba suka tafi.
Mal Fatihu da ya dade a tsaye saboda yaron na cewa Dahiru ne ya kalli Mawadda da tayi shiru tana jiran taji ko za'a bata umarnin fita yace tayi hakuri a karo na karshe ta cire Dahiru daga ranta. Shima zai fita ya bashi baki ya bi maganar iyayensa. Kafin ya fito ne kunnuwansu suka jiye masa maganganun Mal Isiyaku. Wani irin zafi yaji a saitin zuciyarsa kamar ana daddaureta ya dafe kirjin ya koma ciki yana dafa bango.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK..*💰10
*Batul Mamman*💖
Su Inna da sauri suka karasa inda Baba yake kwance ko motsi baya yi tamkar babu rai a jikinsa.
Mutane suka yi dafifi a wurin ko iskar kirki babu. Mawadda tana durkushe tana kuka ta soma kokarin daga kansa wani dan sanda yace ta kyale shi kada wanda ya motsa shi. Waya ya shiga yi suka ji yana kwatanta inda suke da abinda ya faru.
Su Iya duk sun zagaye shi suna kuka Mawadda ta hango Haj Mara tana washe baki wasu mutane suna yi mata barka da arziki tana fada musu ai kudin tarar da alkali ya nema daga garesu ma sun yafe tunda gaskiya ta fito.
Yadda zuciyarta ke suya a lokacin duk wani tsoro ya fice mata. Tashi tayi da saurinta kada ta shige mota su tafi ta kutsa kai ta cikin mutanen ido a rufe ta samu ta damko hannunta.
"Ke meye haka?" Ta fada tana son kwacewa sai dai kusan janta Mawadda take yi tana son turjewa ta nuna hali amma tana tsoron kada ta bada kanta a gaban mutane.
Ba ita ta saketa ba sai da suka je inda Baba yake kwance Yaya tana masa firfita da mayafinta. Idanu jazur ta dubi Haj Mara cikin karaji tace
"Kinga hawayen da yake zuba daga idanun iyayena???"
Haj Mara ta tsorata da yadda Mawadda take dadinta daya suna fita ta danna BB a motar Dr Tani tace zata biyo bayansu idan ta gana da iyayen Mawadda. Ba komai yasa tayi hakan ba sai tsoron kada ya tona musu asiri a bainar jama'a.
Bangazar kirjinta Mawadda tayi ta sake maimaita tambayar. Mutane suka soma darewa ana mata kallon mara hankali. 'Yan sandan da suke wurin suka fara matsowa ta dago idanu wanda kallo daya zaka yi mata idan ba ka jajirce ba kaji firgici ya ziyarceka.
Sassauta murya tayi tace "Na gani Mawadda, kinga ki kwantar da hankalinki komai zai wuce kinji ko"
Iyayenta ta rinka nuna mata daya bayan daya hawaye yana bin kumatunta.
"Wannan hawayen nasu nake so ya zauna a ranki har abada Hajiya. Idan Babana ya mutu ne to shima ki samu wuri a zuciyarki ki ajiye saboda gaba"
Daga haka ta koma ta zauna a gefen Baba. Haj Mara ta kasa barin wurin sai mutane ne suke matsawa daga gareta. 'Yar wannan magana ta Mawadda tayi mugun tasiri a zuciyarta har tana ganin kamar har ta mutu fuskokin mutanen bazasu taba gogewa daga kwakwalwarta ba. 'Yan bani na iya tuni suka fara hasashen ko dai akwai wata a kasa ne.
Ba jimawa sai ga karar ambulance aka ajiyeta kusa da Baba. Cikin nutsuwa da kulawa suka dora shi akan gado akace mutum daya cikinsu ta shiga sauran su biyosu Aminu Kano bangaren emergency.
A gurguje suka fita suka tari adaidaita sahu yayin da Yaya ta bi Baba a cikin motar.
Lokacin da suka isa tana wajen reception tana bada bayanai kamar sunansa da shekaru. Shi kuma tuni likitoci sun amshe shi ana bashi taimakon gaggawa.
Duk wani abu da zasu yi na ceton ransa sunyi. Kusan awa biyu sannan aka tura shi dakin marasa lafiya idanu a rufe. Su Inna zuciya ta tsinke ganinsa a haka. Sai dai wata likita tace su kwantar da hankulansu in Allah Ya yarda zai tashi. Jininsa ne ya hau sosai ga dukkan alamu yana tattare da damuwar da tayi masa yawa.
Mawadda na jin haka taji ta tsani kanta sosai tana ganin ita ce sila. Mahaifinsu talaka ne amma mutumin kwarai wanda rayuwar kauye bata hana shi zama uba mai barkwanci da iyalinsa ba.
A gefen gadon nasa duk suka taru sai daga baya suka fara tafiya yin sallah. Ya rage Yaya kawai a wurin Mawadda ta fita siyo musu ruwan sha ya bude ido a hankali.
Yaya tayi maza zata fita kiran likita kamar yadda suka bada umarni yace ta dawo ta gyara masa kwanciya yaji kamar ya karkace.
Tana ta ce masa sannu ta shiga kici-kicin daga shi ta kasa.
"Malam ai ka sakar min nauyi dan yunkara mana"
Gwadawa yayi yaji ya kasa sai ga Ade ta shigo. Yaya tace tazo ta tayata. Dan turus tayi tana kallonsa Yaya tayi murmushi
"ni dai zo ki kama min jikin nasa yayi nauyi."
Tsohuwar kunya ce ta taso tazo ta kama sai dai duka sun kasa.
"Yaya Fatihu kaima baka motsawa"
Yaya tace "nima haka nace masa kafin ki shigo"
Kafin ya karashe maganar kuka ma yake yi sosai hawaye har gaban malun-malun dinsa ya jike. Masu daukar rahoto da 'yan kallo da dama sun zubar da kwalla. Haka zalika iyalansa da suke tsaye a bakin kofar kotun.
*****
Dahiru zaune gaban yayansa Bilya yana ta juya cokali cikin abinci.
"Kayi hakuri kada ka batawa su Baffa rai akan mace Dahiru komai mai wucewa ne"
"Na sani Yayanmu amma bazan taba iya cire Mawadda daga zuciyata ba. Yau aka fara shiga kotun ya dace ace ina tare dasu amma kaga banma san wace kotu bace"
Bilya yana tausayin kaninsa sosai amma Inna tayi masa gargadi mai karfi akan ya tsawatar masa da batun auren don bazata taba yarda ba duk runtsi.
Kasa cin abincin Dahiru yayi ya tashi ya fita wurin wani mai shayi a layin da suka saba zama. Ana ta hira ya zurfafa a tunani yaji muryar Baba a lokacin da yake maidawa wasu martani. Mai kawo rahoton yace hakika wannan mutumi ya nusar da mutane da dama abinda suka manta game da na kasa dasu a kowane matakin rayuwa. Komai talauci, rashin ilimi da wayewa mutum, mutum ne abin darajawa saboda haka zasu cigaba da bibiyar wannan shari'a da akeyi a kotu mai lamba biyar Court road domin jin yadda zata kaya.
Har kuka Dahiru yayi yana jin wannan labarai. Tashi yayi ya bar wurin da surutun jama'a ya ishe shi akan kukan me yake yi.
Washegari da sassafe yaje gidan aikinsa yayi shara da gyaran filawa ko sallama baiyi da kowa ba ya kama hanyar tasha. Yayi babbar sa'a su Mal Fatihu tun jiya suka koma Tariwa. Kai tsaye gidansa ya wuce sai ya tuna bata gidan ya kama hanyar gidan kakaninta.
Lokacin shadaya na safe yana tsaye yana jiran yaron da ya tura sai ga Baffa shima yazo. Da mamaki Baffa yace "Dahiru saukar yaushe?"
Gaishe shi yayi yaga bai amsa ba yace "isowata kenan"
"Shine ka fara zuwa nan? Ashe duk maganar da muke yi maka bayan kunnenka take bi. To billahillazi kaji na rantse ban lamunce maka auren yarinyar nan ba ka nemi wata. Garin nan kwana akayi ana zancen shigarsu kotu jiya shine nazo jajanta masa naje gidansa ance yana nan ashe rabon na ganka ne."
Kamar yayi kuka ya dan duka "Baffa don Allah kayi hakuri yanzu ne take bukata ta bai kamata na juya...."
"Dahiru kada ka bari na sauke maka bacin raina. Ka wuce muje jajen ma na fasa tunda shima ya kasa gane zuru da kawaici idan kazo maimakon yace ka dena zuwa aure tsakaninku bazai yiwu ba"
Duk yadda Dahiru ke rokon Baffansa haka ya saka shi a gaba suka tafi.
Mal Fatihu da ya dade a tsaye saboda yaron na cewa Dahiru ne ya kalli Mawadda da tayi shiru tana jiran taji ko za'a bata umarnin fita yace tayi hakuri a karo na karshe ta cire Dahiru daga ranta. Shima zai fita ya bashi baki ya bi maganar iyayensa. Kafin ya fito ne kunnuwansu suka jiye masa maganganun Mal Isiyaku. Wani irin zafi yaji a saitin zuciyarsa kamar ana daddaureta ya dafe kirjin ya koma ciki yana dafa bango.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK..*💰10
*Batul Mamman*💖
Su Inna da sauri suka karasa inda Baba yake kwance ko motsi baya yi tamkar babu rai a jikinsa.
Mutane suka yi dafifi a wurin ko iskar kirki babu. Mawadda tana durkushe tana kuka ta soma kokarin daga kansa wani dan sanda yace ta kyale shi kada wanda ya motsa shi. Waya ya shiga yi suka ji yana kwatanta inda suke da abinda ya faru.
Su Iya duk sun zagaye shi suna kuka Mawadda ta hango Haj Mara tana washe baki wasu mutane suna yi mata barka da arziki tana fada musu ai kudin tarar da alkali ya nema daga garesu ma sun yafe tunda gaskiya ta fito.
Yadda zuciyarta ke suya a lokacin duk wani tsoro ya fice mata. Tashi tayi da saurinta kada ta shige mota su tafi ta kutsa kai ta cikin mutanen ido a rufe ta samu ta damko hannunta.
"Ke meye haka?" Ta fada tana son kwacewa sai dai kusan janta Mawadda take yi tana son turjewa ta nuna hali amma tana tsoron kada ta bada kanta a gaban mutane.
Ba ita ta saketa ba sai da suka je inda Baba yake kwance Yaya tana masa firfita da mayafinta. Idanu jazur ta dubi Haj Mara cikin karaji tace
"Kinga hawayen da yake zuba daga idanun iyayena???"
Haj Mara ta tsorata da yadda Mawadda take dadinta daya suna fita ta danna BB a motar Dr Tani tace zata biyo bayansu idan ta gana da iyayen Mawadda. Ba komai yasa tayi hakan ba sai tsoron kada ya tona musu asiri a bainar jama'a.
Bangazar kirjinta Mawadda tayi ta sake maimaita tambayar. Mutane suka soma darewa ana mata kallon mara hankali. 'Yan sandan da suke wurin suka fara matsowa ta dago idanu wanda kallo daya zaka yi mata idan ba ka jajirce ba kaji firgici ya ziyarceka.
Sassauta murya tayi tace "Na gani Mawadda, kinga ki kwantar da hankalinki komai zai wuce kinji ko"
Iyayenta ta rinka nuna mata daya bayan daya hawaye yana bin kumatunta.
"Wannan hawayen nasu nake so ya zauna a ranki har abada Hajiya. Idan Babana ya mutu ne to shima ki samu wuri a zuciyarki ki ajiye saboda gaba"
Daga haka ta koma ta zauna a gefen Baba. Haj Mara ta kasa barin wurin sai mutane ne suke matsawa daga gareta. 'Yar wannan magana ta Mawadda tayi mugun tasiri a zuciyarta har tana ganin kamar har ta mutu fuskokin mutanen bazasu taba gogewa daga kwakwalwarta ba. 'Yan bani na iya tuni suka fara hasashen ko dai akwai wata a kasa ne.
Ba jimawa sai ga karar ambulance aka ajiyeta kusa da Baba. Cikin nutsuwa da kulawa suka dora shi akan gado akace mutum daya cikinsu ta shiga sauran su biyosu Aminu Kano bangaren emergency.
A gurguje suka fita suka tari adaidaita sahu yayin da Yaya ta bi Baba a cikin motar.
Lokacin da suka isa tana wajen reception tana bada bayanai kamar sunansa da shekaru. Shi kuma tuni likitoci sun amshe shi ana bashi taimakon gaggawa.
Duk wani abu da zasu yi na ceton ransa sunyi. Kusan awa biyu sannan aka tura shi dakin marasa lafiya idanu a rufe. Su Inna zuciya ta tsinke ganinsa a haka. Sai dai wata likita tace su kwantar da hankulansu in Allah Ya yarda zai tashi. Jininsa ne ya hau sosai ga dukkan alamu yana tattare da damuwar da tayi masa yawa.
Mawadda na jin haka taji ta tsani kanta sosai tana ganin ita ce sila. Mahaifinsu talaka ne amma mutumin kwarai wanda rayuwar kauye bata hana shi zama uba mai barkwanci da iyalinsa ba.
A gefen gadon nasa duk suka taru sai daga baya suka fara tafiya yin sallah. Ya rage Yaya kawai a wurin Mawadda ta fita siyo musu ruwan sha ya bude ido a hankali.
Yaya tayi maza zata fita kiran likita kamar yadda suka bada umarni yace ta dawo ta gyara masa kwanciya yaji kamar ya karkace.
Tana ta ce masa sannu ta shiga kici-kicin daga shi ta kasa.
"Malam ai ka sakar min nauyi dan yunkara mana"
Gwadawa yayi yaji ya kasa sai ga Ade ta shigo. Yaya tace tazo ta tayata. Dan turus tayi tana kallonsa Yaya tayi murmushi
"ni dai zo ki kama min jikin nasa yayi nauyi."
Tsohuwar kunya ce ta taso tazo ta kama sai dai duka sun kasa.
"Yaya Fatihu kaima baka motsawa"
Yaya tace "nima haka nace masa kafin ki shigo"