Sashe 3
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baffansa yace "nifa nayi zargin da matsala don yau sau uku ina ganinsa a kofar gida kana ganinsa kasan bashi da nutsuwa. Amma kinsan Fatihu da kawaici sai ya kasa fadamin. Ban ga ta zama ba sun fita da la'asar sakaliya akwai matsala kila jikin Mawadda ne ba dadi sosai."
Inna tace "Baffa nima zani. Kuma kasan dole Dahiru ya bimu. Akwai kudi a jikinka dai koda zasu nema ko?"
Dan murmushi Baffa yayi. Inna akwai zurfin tunani da son taimako. Tasan yafi Mal Fatihu wadata shiyasa take masa inkiyi ya fita da kudi. Musamman ma da abin ya hada da surukarta.
Dahiru ne ya samo musu mota ba jimawa suka bi bayansu Baba. Kafin wani lokaci magana ta fara yawo ai an ga iyalin Mal Fatihu da na Mal Isiyaku duk sun shiga mota sun bar gari da yamma.
Su Baba na zuwa asibiti sunyi sa'a likitan da zaiyi aiki har dare yana nan. Ade dai hakuri yazo wuya da taji likitan yana tambayar me ya sameta Baba yana cewa ita da Yaya su fita.
Ranta a mugun bace ta soma fada "Wai yaya kuke min haka ne? Tun a hanya nake ta magana duka ku ka ki amsawa ita sai hawaye kamar wata mai lalurar ciwon kuka. Na hakura na daure kuma yanzu a nan dinma dabara zakuyi min ko me?"
Mawadda ta dago da take jikin Yaya "Ke me ya sameki?"
Likita yace tayi hakuri suyi aikinsu. Ba don taso ba suka fita ita da Yaya suka barsu da wata Nos mace. Kallon Yaya tayi tana goge hawaye da gefen mayafi ta sake harzuka sai dai ta danne. Yaya mutum ce a wurinta harda kari. Ita kuwa bata manta karamci komai kankantarsa.
Daga cikin dakin duba mara lafiyar taji Baba hankali a tashe yana cewa " 'yan sanda kuma likita? Yanzu bazaka taimaka mata ba sai na nemo 'yan sanda sai kace wadda tayi sata ko kisan kai. Ita fa aka cuta"
Tuni Ade ta banka kai cikin dakin tana huci ko kallon Baba batayi ba "Likita me yace ya sami yarinyar nan?"
Mawadda taja mayafinta ta rufa har ka tana daga kwance an sakaya wurin da labule saboda bakinciki da kunya yayin da Likitan cike da alhinin yadda zata dauki maganar don ga dukkan alamu mahaifiyarta ce yace "fyade akayi mata"
"ME???" Ta fada da karfi wanda ya janyo hankalinsu Baffa, Inna, Dahiru da Yaya wadda mamakin ganinsu ya kasheta a tsaye duk suka nufi kofar dakin duba marasa lafiyar.
Nos da take tare da likitan kuma ita ta duba Mawaddan ta dafa Ade ta zaunar da ita "kiyi hakuri alamu sun nuna fyade akayi mata wanda yayi sanadiyar ji mata mummunan rauni"
"Mun shiga uku" cewar Inna hakan ya janyo hankalin su Baba zuwa bakin kofar dakin.
[03/12 23:02] Meela Adeel: *GUMIN HALAK...*馃挵2
*Batul Mamman*馃挅
Baban Mawadda yana shiga cikin gidansa ya samesu a tsakar gida kan tabarma inda suka zauna tun shigowarta da Haj Mara. Yanzu tare take da kannenta suna ta hayaniya su kadai domin ita kanta kunshe yake cikin hijab kamar yadda aka bata umarni tun a hanya. Idanunta kawai ake gani tana ta rarrabasu tana bin kowa daidai. Kai ya girgiza yana murmushi a tunaninsa 'yan shiru-shirun ne a kusa. Maimakon ya kirata sai ya je har inda take ya dora hannunsa a kafadarta tare da yin gyaran murya. Ba karamin tsoro bane yakamata hantar cikinta ta kada ta saki kara iya karfinta ga zuciyarta tana matsanancin bugu. Hakan yasa kannenta darewa a tsorace suna kallonta.
Yaya dake wurin girki tana gyara wuta don tasan yau babu mai tayata aiki sun ga 'yar uwarsu ta hango fuskarta a kumbure saboda hijabin ya zame lokacin da ta tsorata. Da sauri ta sake janshi ta boye fuskar tana inda-inda rashin sanin me zata ce ya bata tsoro, to ashe shima Baba ya ga fuskar. Zuciyarsa a take tayi nauyi da sake-saken me ya sami 'yar tasa.
Yaya baro wurin girkin tayi ta sallami duka yaran da fadan basuyi sallar la'asar ba har babansu ya dawo daga masallaci. Haka suka tafi suna ta kananan maganganu da hasashen ko yayar tasu tayi gamo ne a birni. Baba kuma hanyar waje ya kama zai fita Yaya ta tsayar dashi.
"Malam ina kuma zaka je ko baka kula da fuskar Mawadda bane?"
Jiki a sanyaye yace mata yanzu zai dawo. Waje ya koma tun daga soro Dahiru yaji sautin tafiya yayi saurin gyara tsayuwarsa a zatonsa Mawadda ce. Ganin Baba ya sake fitowa yayi saurin tsugunawa yana dan tsintar tsakuwa kansa a duke.
Baba ya kakalo murmushin dole "Tashi Dahiru, ai cewa nayi bari na fito da kaina kada a barka a tsaye kannen suna sallah. Wato ina shiga na sameta ba yadda take zazzabi ya rufeta."
"Assha, Subhanallahi.." cewar Dahiru damuwa karara a fuskarsa ma'abociyar fara'a da murmushi.
Baba ya cigaba da karyar dole saboda rashin sanin ainihin abinda ya sami Mawadda "kasan ita ba mai son doguwar tafiya bace a mota, inajin zaman ne duk ya saka mata zazzabin"
Shi Dahiru kunya ce ta lullube shi da takaicin kansa na zuwa tadi daga saukarta a garin ko hutawa batayi ba. Ashe ma ba lafiya take ba.
"Baba Allah Ya bata lafiya. Ina dubata da jiki. Ko zuwa gobe idan taji dama sai nazo dubiya"
Daga haka ya tashi ya tafi Baba ya juya cikin sauri. Wannan karon ba kowa a tsakar gidan. Daga kofar dakinsa ya hango takalman Mawadda ya karasa da sassarfa.
Yana daga labulen ya samesu jigum ita da Yaya. Yaya ta rafka tagumi ita kuma tana kuka mara sauti.
"Me tace miki ya sameta? Hatsari sukayi a hanya?"
"Ko daya Malam, jira nayi ka dawo don nayi juyin duniya taki magana"
Wannan abu da mamaki yake. Yarinya wata bakwai bata gida ta dawo babu farinciki sai fuska a kumbure.
"Mawadda me ya sameki?" cewar Baba
Ko dagowa batayi ba sai kukanta da ya tsananta. Ga tsoron fadin gaskiya ga azabar ciwo.
"Kina da wasu da suka cancanci sanin halin da kike ciki?"
Ganin taki kulasu ran Yaya ya baci. Dama can ita mace ce mai zafi sai dai akwai kirki da sanin ya kamata. Hijabin tasa hannu ta cire ta karfin tsiya sai ga shatin belt kwance a wuyanta da hannu. Lebbanta kuwa na saman tsakiyarsa yayi ja alamun jini ya taru na kasa kuma girmansa yayi ukun yadda yake a da. Batun kumatu kuwa sai a lokacin suka gane ba karamin kumburi sukayi. Da yake kuma tana da haske daidai gwargwado shiyasa tabban suka nuna sosai.
Jikin Baba yayi mugun sanyi wannan kam ko ba'a fada ba kowa yasan duka ne. Yaya kuwa kuka ta fashe dashi ta rungume Mawadda.
"Sai da nace kar kije ko kadan hankalina bai kwanta da tafiyar ba" Yaya ta fada cikin kuka
Wurin minti ashirin kafin kukan ya tsagaita. Zuwa lokacin ma zazzabi yayi mugun kama Mawadda jikinta sai bari yake tana rawar sanyi. Hankali a tashe Yaya ta fita taje ta kira sauran 'yan matan suka tayata dora ruwa a babbar tukunya. Suna tambayarta lafiya tace yayarsu ce bata jindadi faduwa tayi a can gidan aikin nata.
Baba da kansa ya fita ya tafi kemis neman panadol. Da ya dawo tana bandaki tana wanka. Duk yadda Yaya taso taje ta gasa mata jiki taki yarda. Sai dai bata sani ba tun a lokacin Yayan take kula da tafiyarta da ta sauya.
*****
Dahiru yana komawa gida Inna ta tsare shi da tambayar yaya akayi ya dawo da wuri ko kunyar magana yasa shi dawowa. Murmushi yayi tace
"Wannan gulma ana so ana kaiwa kasuwa. Kana jin ta dawo ka diba a guje kamar gaske"
"Inna bata da lafiya ko haduwa bamuyi ba. Ashe zazzabi ne ya rufeta saboda zaman mota" yayi maganar a sanyaye cike da damuwa.
Nan da nan Inna ta rude. Yadda danta yake son Mawadda haka take kaunar yarinyar saboda nutsuwarta da tarbiya. An shaidi gidan Mal Fatihu da tarbiya duk da yawancin yaransa mata ne. Yaya akwai kokari da jajircewa.
Zakara babba mai rai da lafiya Inna tasa Danlami ya kama ya yanka mata. Yana zaune yana aikin figa sai tura baki yake yau an hanashi zuwa kwallo. Yana gamawa Inna tasa aka jajjaga mata kayan miya ta hada da kayan kamshi harda daddawarta mai kyau tayi farfesu mai dadi. Kai da kafa kawai ta cire a ciki aka bawa Danlami da Ummiyo mai bi masa suka lasa. Sauran kuwa maigidanta ta aiki Dahiru ya sanarwa a bakin kasuwa zata je dubiya idan anyi magariba.
*****
Inna da Dahiru suka tafi yace zai jirata a kiyos din wani abokinsa kada ya sake zuwa a ga rashin hakurinsa kuma.
Tunda Mawadda tayi wanka take kwance iyayenta sai kai kawo suke gashi taki magana balle cin abinci. Sallamar Inna yadda ta kada mata hanji haka ta kadawa su Yaya. Basa so kowa ya ganta a wannan yanayin har sai sun san abinda yake faruwa. Inda Allah Ya taimakesu babu wuta saboda haka bata ganta ba sosai. Da tayi yunkurin tashi ma Innar da kanta tace ta kwanta har tana basu shawarar idan zazzabin bai sauka ba da safe su kaita asibiti. Haka suka taba hira sama-sama ta kawo farfesun nan tace a bata. A mutumce sukayi sallama ta fito.
Fitarta tayi daidai da sauke ajiyar zuciyar Yaya. Rai a dan bace ta soma yiwa Mawadda fadan sai ta fadi me ya sameta. Wannan karon ma kukan ta soma sai ta kyaleta saboda yara.
Wuri karfe taran dare ta tashi zata zaga bayi Yaya ta kuma ganin tana tafiya kamar mai dingishi tana karkace kafa. Tsoro ne sosai ya kamata ta dai kama bakinta. Sai dai sam ranar ta kasa bacci. Baba yana kula da yadda take ta juyi cikin dare sai ta danyi tsaki ko ajiyar zuciya. Can dai da abin ya isheta ta tashi da sanda ta fita. Lokacin daya saura na dare.
Dakin yaran taje ta leka ta taga ta jiyo alamun kukan Mawadda. Dakin da suke ajiye kwanuka da tarkace taje ta dauko wuka ta dawo. A hankali ta shiga ta tabota. Yanzu ma zabura tayi kafin tayi ihu Yaya ta haskata da 'yar fitilar da batir din yayi sanyi ba haske sosai.
Inna tace "Baffa nima zani. Kuma kasan dole Dahiru ya bimu. Akwai kudi a jikinka dai koda zasu nema ko?"
Dan murmushi Baffa yayi. Inna akwai zurfin tunani da son taimako. Tasan yafi Mal Fatihu wadata shiyasa take masa inkiyi ya fita da kudi. Musamman ma da abin ya hada da surukarta.
Dahiru ne ya samo musu mota ba jimawa suka bi bayansu Baba. Kafin wani lokaci magana ta fara yawo ai an ga iyalin Mal Fatihu da na Mal Isiyaku duk sun shiga mota sun bar gari da yamma.
Su Baba na zuwa asibiti sunyi sa'a likitan da zaiyi aiki har dare yana nan. Ade dai hakuri yazo wuya da taji likitan yana tambayar me ya sameta Baba yana cewa ita da Yaya su fita.
Ranta a mugun bace ta soma fada "Wai yaya kuke min haka ne? Tun a hanya nake ta magana duka ku ka ki amsawa ita sai hawaye kamar wata mai lalurar ciwon kuka. Na hakura na daure kuma yanzu a nan dinma dabara zakuyi min ko me?"
Mawadda ta dago da take jikin Yaya "Ke me ya sameki?"
Likita yace tayi hakuri suyi aikinsu. Ba don taso ba suka fita ita da Yaya suka barsu da wata Nos mace. Kallon Yaya tayi tana goge hawaye da gefen mayafi ta sake harzuka sai dai ta danne. Yaya mutum ce a wurinta harda kari. Ita kuwa bata manta karamci komai kankantarsa.
Daga cikin dakin duba mara lafiyar taji Baba hankali a tashe yana cewa " 'yan sanda kuma likita? Yanzu bazaka taimaka mata ba sai na nemo 'yan sanda sai kace wadda tayi sata ko kisan kai. Ita fa aka cuta"
Tuni Ade ta banka kai cikin dakin tana huci ko kallon Baba batayi ba "Likita me yace ya sami yarinyar nan?"
Mawadda taja mayafinta ta rufa har ka tana daga kwance an sakaya wurin da labule saboda bakinciki da kunya yayin da Likitan cike da alhinin yadda zata dauki maganar don ga dukkan alamu mahaifiyarta ce yace "fyade akayi mata"
"ME???" Ta fada da karfi wanda ya janyo hankalinsu Baffa, Inna, Dahiru da Yaya wadda mamakin ganinsu ya kasheta a tsaye duk suka nufi kofar dakin duba marasa lafiyar.
Nos da take tare da likitan kuma ita ta duba Mawaddan ta dafa Ade ta zaunar da ita "kiyi hakuri alamu sun nuna fyade akayi mata wanda yayi sanadiyar ji mata mummunan rauni"
"Mun shiga uku" cewar Inna hakan ya janyo hankalin su Baba zuwa bakin kofar dakin.
[03/12 23:02] Meela Adeel: *GUMIN HALAK...*馃挵2
*Batul Mamman*馃挅
Baban Mawadda yana shiga cikin gidansa ya samesu a tsakar gida kan tabarma inda suka zauna tun shigowarta da Haj Mara. Yanzu tare take da kannenta suna ta hayaniya su kadai domin ita kanta kunshe yake cikin hijab kamar yadda aka bata umarni tun a hanya. Idanunta kawai ake gani tana ta rarrabasu tana bin kowa daidai. Kai ya girgiza yana murmushi a tunaninsa 'yan shiru-shirun ne a kusa. Maimakon ya kirata sai ya je har inda take ya dora hannunsa a kafadarta tare da yin gyaran murya. Ba karamin tsoro bane yakamata hantar cikinta ta kada ta saki kara iya karfinta ga zuciyarta tana matsanancin bugu. Hakan yasa kannenta darewa a tsorace suna kallonta.
Yaya dake wurin girki tana gyara wuta don tasan yau babu mai tayata aiki sun ga 'yar uwarsu ta hango fuskarta a kumbure saboda hijabin ya zame lokacin da ta tsorata. Da sauri ta sake janshi ta boye fuskar tana inda-inda rashin sanin me zata ce ya bata tsoro, to ashe shima Baba ya ga fuskar. Zuciyarsa a take tayi nauyi da sake-saken me ya sami 'yar tasa.
Yaya baro wurin girkin tayi ta sallami duka yaran da fadan basuyi sallar la'asar ba har babansu ya dawo daga masallaci. Haka suka tafi suna ta kananan maganganu da hasashen ko yayar tasu tayi gamo ne a birni. Baba kuma hanyar waje ya kama zai fita Yaya ta tsayar dashi.
"Malam ina kuma zaka je ko baka kula da fuskar Mawadda bane?"
Jiki a sanyaye yace mata yanzu zai dawo. Waje ya koma tun daga soro Dahiru yaji sautin tafiya yayi saurin gyara tsayuwarsa a zatonsa Mawadda ce. Ganin Baba ya sake fitowa yayi saurin tsugunawa yana dan tsintar tsakuwa kansa a duke.
Baba ya kakalo murmushin dole "Tashi Dahiru, ai cewa nayi bari na fito da kaina kada a barka a tsaye kannen suna sallah. Wato ina shiga na sameta ba yadda take zazzabi ya rufeta."
"Assha, Subhanallahi.." cewar Dahiru damuwa karara a fuskarsa ma'abociyar fara'a da murmushi.
Baba ya cigaba da karyar dole saboda rashin sanin ainihin abinda ya sami Mawadda "kasan ita ba mai son doguwar tafiya bace a mota, inajin zaman ne duk ya saka mata zazzabin"
Shi Dahiru kunya ce ta lullube shi da takaicin kansa na zuwa tadi daga saukarta a garin ko hutawa batayi ba. Ashe ma ba lafiya take ba.
"Baba Allah Ya bata lafiya. Ina dubata da jiki. Ko zuwa gobe idan taji dama sai nazo dubiya"
Daga haka ya tashi ya tafi Baba ya juya cikin sauri. Wannan karon ba kowa a tsakar gidan. Daga kofar dakinsa ya hango takalman Mawadda ya karasa da sassarfa.
Yana daga labulen ya samesu jigum ita da Yaya. Yaya ta rafka tagumi ita kuma tana kuka mara sauti.
"Me tace miki ya sameta? Hatsari sukayi a hanya?"
"Ko daya Malam, jira nayi ka dawo don nayi juyin duniya taki magana"
Wannan abu da mamaki yake. Yarinya wata bakwai bata gida ta dawo babu farinciki sai fuska a kumbure.
"Mawadda me ya sameki?" cewar Baba
Ko dagowa batayi ba sai kukanta da ya tsananta. Ga tsoron fadin gaskiya ga azabar ciwo.
"Kina da wasu da suka cancanci sanin halin da kike ciki?"
Ganin taki kulasu ran Yaya ya baci. Dama can ita mace ce mai zafi sai dai akwai kirki da sanin ya kamata. Hijabin tasa hannu ta cire ta karfin tsiya sai ga shatin belt kwance a wuyanta da hannu. Lebbanta kuwa na saman tsakiyarsa yayi ja alamun jini ya taru na kasa kuma girmansa yayi ukun yadda yake a da. Batun kumatu kuwa sai a lokacin suka gane ba karamin kumburi sukayi. Da yake kuma tana da haske daidai gwargwado shiyasa tabban suka nuna sosai.
Jikin Baba yayi mugun sanyi wannan kam ko ba'a fada ba kowa yasan duka ne. Yaya kuwa kuka ta fashe dashi ta rungume Mawadda.
"Sai da nace kar kije ko kadan hankalina bai kwanta da tafiyar ba" Yaya ta fada cikin kuka
Wurin minti ashirin kafin kukan ya tsagaita. Zuwa lokacin ma zazzabi yayi mugun kama Mawadda jikinta sai bari yake tana rawar sanyi. Hankali a tashe Yaya ta fita taje ta kira sauran 'yan matan suka tayata dora ruwa a babbar tukunya. Suna tambayarta lafiya tace yayarsu ce bata jindadi faduwa tayi a can gidan aikin nata.
Baba da kansa ya fita ya tafi kemis neman panadol. Da ya dawo tana bandaki tana wanka. Duk yadda Yaya taso taje ta gasa mata jiki taki yarda. Sai dai bata sani ba tun a lokacin Yayan take kula da tafiyarta da ta sauya.
*****
Dahiru yana komawa gida Inna ta tsare shi da tambayar yaya akayi ya dawo da wuri ko kunyar magana yasa shi dawowa. Murmushi yayi tace
"Wannan gulma ana so ana kaiwa kasuwa. Kana jin ta dawo ka diba a guje kamar gaske"
"Inna bata da lafiya ko haduwa bamuyi ba. Ashe zazzabi ne ya rufeta saboda zaman mota" yayi maganar a sanyaye cike da damuwa.
Nan da nan Inna ta rude. Yadda danta yake son Mawadda haka take kaunar yarinyar saboda nutsuwarta da tarbiya. An shaidi gidan Mal Fatihu da tarbiya duk da yawancin yaransa mata ne. Yaya akwai kokari da jajircewa.
Zakara babba mai rai da lafiya Inna tasa Danlami ya kama ya yanka mata. Yana zaune yana aikin figa sai tura baki yake yau an hanashi zuwa kwallo. Yana gamawa Inna tasa aka jajjaga mata kayan miya ta hada da kayan kamshi harda daddawarta mai kyau tayi farfesu mai dadi. Kai da kafa kawai ta cire a ciki aka bawa Danlami da Ummiyo mai bi masa suka lasa. Sauran kuwa maigidanta ta aiki Dahiru ya sanarwa a bakin kasuwa zata je dubiya idan anyi magariba.
*****
Inna da Dahiru suka tafi yace zai jirata a kiyos din wani abokinsa kada ya sake zuwa a ga rashin hakurinsa kuma.
Tunda Mawadda tayi wanka take kwance iyayenta sai kai kawo suke gashi taki magana balle cin abinci. Sallamar Inna yadda ta kada mata hanji haka ta kadawa su Yaya. Basa so kowa ya ganta a wannan yanayin har sai sun san abinda yake faruwa. Inda Allah Ya taimakesu babu wuta saboda haka bata ganta ba sosai. Da tayi yunkurin tashi ma Innar da kanta tace ta kwanta har tana basu shawarar idan zazzabin bai sauka ba da safe su kaita asibiti. Haka suka taba hira sama-sama ta kawo farfesun nan tace a bata. A mutumce sukayi sallama ta fito.
Fitarta tayi daidai da sauke ajiyar zuciyar Yaya. Rai a dan bace ta soma yiwa Mawadda fadan sai ta fadi me ya sameta. Wannan karon ma kukan ta soma sai ta kyaleta saboda yara.
Wuri karfe taran dare ta tashi zata zaga bayi Yaya ta kuma ganin tana tafiya kamar mai dingishi tana karkace kafa. Tsoro ne sosai ya kamata ta dai kama bakinta. Sai dai sam ranar ta kasa bacci. Baba yana kula da yadda take ta juyi cikin dare sai ta danyi tsaki ko ajiyar zuciya. Can dai da abin ya isheta ta tashi da sanda ta fita. Lokacin daya saura na dare.
Dakin yaran taje ta leka ta taga ta jiyo alamun kukan Mawadda. Dakin da suke ajiye kwanuka da tarkace taje ta dauko wuka ta dawo. A hankali ta shiga ta tabota. Yanzu ma zabura tayi kafin tayi ihu Yaya ta haskata da 'yar fitilar da batir din yayi sanyi ba haske sosai.