← Book details Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 54 OF 68

Sashe 54

Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya langabe kai "ji kai, shiyasa nace kizo a yayata. kawai don kada na fama a sake gyaran ne. Yau fa na kusa kuka don ciwo"

Runtse ido tayi ta matso kusa dashi tana cewa zata tambayi Attahir kila yayi kukan.

Kasan rigar ta kama zata fara dagawa yace "wash kiyi min a hankali"

"A hankalin fa nake yi"

"Ni dai ki bude idonki sai ni na rufe nawa. Allah idan kika fama min kuka zanyi"

Bude ido tayi suka sauka cikin nasa suka yi dariya tare. Haka akayi ya rufe nasa idon "kuma saura ki kalleni"

Mawadda ta cije leben da ya kurawa ido ta soma mitar shi da ake taimakawa shine da sharudda "haka ma zaka ce, me zan kalla ma"

Sai da ya bari ta cire masa rigar tana ta kawar da kai daga shi sai vest da dogon wando sannan yace "ki ka ce babu abin kalla a jikina ko"

"To ai kai din ne"

Gabanta ta ga yana kara matsowa ta fara ja da baya yana biye da ita har bakin gado saura kadan ta fada.

"Ko zaki karasa ladanki a matsayin Yayata tunda babu abin ganin"

A tsorace take jiki har yana rawa tace "rufa min asiri akwai abin kallo a jikinka"

Saurin matsawa baya yayi harda rufe fuska da hannu "wayyo Matarmu kinsa ni jin kunya. Nifa nufina ko zaki iya tara min ruwan wankan"

Kifta idanu ta shiga yi ba kakkautawa sannan ta yi hanyar toilet din da sauri "kaine baka fada yadda zan gane ba"

"Ah....da me kike zato ina nufi? Huhhhhhh ba dai...ba dai...." ya sanya hannunsa ya wani kare jiki kamar an bude kwaila tana wanka.

"Na shiga uku Yayanmu!" Tace tamkar ta fasa ihu "Me yasa kake min haka ne? Ni ba haka nake nufi ba"

Abin da ta saba wato cizon lebe idan tana tunani ta soma yayi murmushi "yanzu ma banyi miki irin yadda ake yiwa amare ba kenan"

Ta gyada kai bakin nan tana juya shi ita kadai tasan me take cewa.

Bata san yadda aka yi ba sai ganinsa tayi a gabanta hannunsa mai lafiya ya zagaye ta bayanta ya matso da ita daf da jikinsa.

"Kinga farkon abinda ake yiwa amare idan sun tare"

Bata ankara ba taji ya hade bakinsu wuri daya dukkansu bugun zuciyoyinsu ya karu a lokaci guda.

******

"Mummy yanzu yau ta tare matar tasa?" Qareeba ta tambayi Dr Tani.

"Allah Ya takaita mata wahala daga shegen yaron nan an samu an ganta da wuri. Har gidan nasa zamu je dake don ina so in roketa ta yafe min itama"

Qareeba ta sa hannu ta share hawaye "yanzu ni Mummy a ta biyu zanje gidan kenan? Ina ta burin nima kamar ke na zauna ni kadai da miji"

Wani wawan duka Dr Tani ta kai mata a baya ta manta bata gama warkewa ba "Dahirun zaki aura don baki da hankali?"

Ta chuno baki "to ba son sa nake ba"

Takaici ya kama Dr Tani tace "yanzu ke Qareeba bayan duk wahalar nan ko warkewa baki gama ba idan aka ce miki ga namiji sai kije koda da aure yazo?"

Ta gyara kwanciya "me zai hana?"

Jinjina kai Dr Tani tayi "anya kan nan naki kalau kuwa?"

Cikin yanayin ko in kula tace "ina laifina don ina son raya sunnah Mummy? Ba don kin wulakanta dan gidan Antin gadon kaya ba tun ina secondary da yake sona kila da yanzu ina da 'ya kamar shekara shabiyu ai"

Tagumi Dr Tani tayi tana kallonta kawai babu amsar bayarwa.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰22

*Batul Mamman*💖

Har Dahiru ya saketa ya shige toilet yin wanka Mawadda tana tsaye ya barta da kaduwa. A hankali ta dora hannu akan bakinta daga bayanta kawai taji muryar Dahiru.

Kansa ya leko ta kofar da ya dan bude "na dawo ne kina jirana?"

Da sauri ta fice daga dakin kamar zata fadi.

Shima nasa bakin ya tsaya kallo a madubin toilet yana jin kamar ya koma gareta.

"Wai ba da zazzabi ka dawo bane" ya tambayi kansa sai kuma yayi murmushi "Dama na jin baki ne ga dukkan alamu"

Wankansa yayi ya shirya cikin kayan bacci. Falo ya fito Mawadda ko kallonsa bata yi ba ta shige dakin ta rufe kofa. Dariya ta bashi ya zauna yana jona wayoyin tv.

Itama wanka tayi har yanzu tana fama da kunya. Da ta shirya daki ya kaure da kamshin turarukan su ta nemi zani ta daura akan rigar baccinta da hijab ta sami wuri ta zauna.

Shirun da yaji ne ya biyo baya ya sameta a zaune. Zaro idanu ta fara tana ganinsa.

"Kina da mara lafiya kin dawo daki ko abinci baki bashi ba"

Mikewa tayi ta sha kunu "muje amma a yayarka"

Tana rufe baki ya matso ya rungumeta. Dama tunda ya shigo kamshin turarenta ya hargitsa masa lissafi.

Ture shi tayi "yayarka fa nace"

Ya sake riketa yana dariya "kanne ne ba'a hugging fa, amma yayye ana ganinsu ake makale musu musamman idan suna kula da kannensu"

Ta fuskanci jindadin tsokanarta yake ta sake ture shi zata gudu.

"Wash...wash hannuna"

Dawowa tayi da sauri "mu gani."

Runtse ido yayi ta yi tana masa sannu. Naman da ya kawo da juice ta zuba yanzu ma a baki ta bashi yana yi yana makale hannu. Wani lokacin sai taji kamar ba na gaske bane sai kuma ta tuna duk saboda ita yake ta fama hannun sai ta hakura.

Sun gama komai anzo kwanciya suka tsaya a gaban gadon. Ta kalle shi ta kalli gadon.

"Tare zamu kwanta ne?"

"Nayi zaton har yanzu yayata ce. Babu matsala ana haka dama mace da kani gado daya"

"Inji wa? Ni dai gaskiya..." ta turo baki.

"Assha ba sai kinyi kuka ba. Zan kwanta a kasan ko na koma falo na takure akan kujera. Hannu na nake ji dama mai gyaran yau har fada yayi min"

Pillow ya dauka ya marairaice mata "kina ganin bazan fama ba idan na kwanta a wuri mara laushi?"

Sai da tayi ajiyar zuciya tace ya kwanta ita zata koma falon yace tana fita zai bita shine namiji idan da mai hakura da gadon shine. Irin dogon pillon nan ta ajiye a tsakiyar gadon saboda a gajiye take idonta har ya soma yaji. Ta nuna masa bari daya

"Ka kwanta a can kuma kada ka wuce pillon nan"

"You are the best Yayarmu Mawadda. Sai da safe. Ki kashe fitilar bana son haske"

Kwanciyarsa yayi a barin da ta nuna masa ta lalubi makunnin fitilar ta kashe. Zata rama ne bari dai yaji saukin hannun nasa tace a ranta.

A darare ta kwanta ta takure jikinta ko hijabin bata cire ba sai zanin kawai ta kwance. Yau ita ce kwance gado daya da Dahiru a matsayin mijinta. Godiya ta yiwa Allah da Ya cika mata burin da ta fitar da tsammani daga tabbatuwarsa. Ba jimawa bacci ya fara fizgarta har Dahiru yaji sauyin yanayin saukar numfashinta.

Wani dadi ne ya kama shi ya matso ya dauke pillon ya cilla shi kasa "anyi kanekane tsakanin mata da miji"

A hankali don kada ya tasheta ya matsa kusa da ita ya lullubesu. Rungumota yayi dama baccin nata babu sakin jiki a take ta farka zuciyarta ta tsananta bugu. Yaji ta fara motsi tana neman kwacewa daga rikon da yayi mata.

"Assha don Allah kada ki koreni tsoro nake ji" yace da karamar murya.

"Tsoron me" ta fada itama a hankali.

"Dodo"

"Zan daure"

"Da me?"

"Mu kwanta a haka Yaya da kaninta matsoraci"

Zai sake magana ta dora hannunta akan bakinsa "bacci nake ji ka dena magana"

Murmushi yayi ransa fari kal kamar an zuba madara. Allah Yayi shi Dahiru zai auri Mawadda. A nata bangaren kuwa shiru tayi kawai zuciyarta kamar ta fito amma tana so ta danne don ta faranta masa. Gajiya da rashin baccin da yake kansu yasa basu dade cikin tunanin da suke yi ba bacci ya kwashe su duka.

*****

Bacci dadi sai da hasken rana ya fara shigowa dakin suka tashi. Mawadda ce ta fara farkawa ta gansu sun cure wuri daya ga hijabinta a gefen gadon ko yaushe ta cire bata sani ba. Matsawa tayi daga jikinsa da sauri. Hannun ciwon ta kalla, wannan hannu ya ga ta kansa ko yaushe zai sami sukunin warkewa.

Bandaki ta shige ta dauro alwala ta fito tazo tana dukan gefen gadon. Da kyar ya bude ido yana ganin haske ya ware su sosai ya tashi "Subhanallahi wane irin bacci nayi haka?"

"Na gajiya"

Ya kula tayi alwala yace ta jira shi suyi tare. Bayan sun idar ya duba wayarsa ko Attahir ya kira shi tunda sunyi akan wanda ya fara tashi ya tashi dan uwansa suje masallaci tare. Bai ga missed call ko daya ba yaji dadi ya sami abin tsokanarsa.

Bayan azkar a wurin Mawadda ta sake bingirewa ya saka mata pillow shima ya janyo wani ya kwanta. Bacci suka sha sosai sai shadaya wayarsa ta tashesu. Sunan Baffa ya gani ya gyara murya tare da yin sallama suka gaisa.

"Dahiru kayi hakuri zan fito da kai kana fama da wannan hannun. Ana nemanmu a ofishin 'yan sanda wai mahaifiyar yaron ce tazo"

Zama yayi sosai yana kallon Mawadda ransa ya soma baci. Ya tsani komai da zai sa ya tuna da BB to amma fa dole wannan karon a yiwa tufkar hanci ta yadda za'a kawo karshen abin once and for all.

Da sauri-sauri ya shirya motsinsa ya tashi Mawadda. Kunya taji ace tana bacci har wannan lokacin Dahiru ya tashi yayi wanka.

Hijabinta ta gyarawa zama "Yayanmu ina kwana".

"Lafiya kalau, na tasheki ko?"

"Yakamata na tashi dama, yaya hannun?"

"Da sauki. Kinga koma kiyi kwanciyarki kada ki tashi sai azahar. Baffa ke nemana zamu je police station akan case din BB"

Dukar da kanta tayi jikinta yayi sanyi lakwas da jin sunan mutumin da ya zame mata dodo. Dahiru ya saki fuska yazo gabanta ya tsaya ya dago da kanta da hannunsa. Rufe ido kawai tayi ya ga hawaye yana zuba. Matseta yayi kam a jikinsa ta fashe masa da kuka mai ban tausayi. Kyaleta yayi tayi kukan har don kanta ta dena ta koma ajiyar zuciya.
Chapter 54 · 0% Book details