Sashe 19
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Barista Shafa'atu ta mike da hanzari "objection my lord, Barista yana amfani da kalmoni domin cusa mata ra'ayin da ba nata ba"
"Objection sustained! Barista Dalhatu ka gyara kalamanka ko ka chanja tambayar" Alkali ya fada masa.
Dan sunkuyar da kai yayi "Nagode my lord. Idan kotu ta bani dama ina son yiwa wanda ake tuhuma tambayoyi"
Alkali ya bashi dama tare da umartar Mawadda ta koma ta zauna.
"Babawo Sule Chanji ko zamu iya jin takaitaccen tarihinka?" Ita ce tambayar da ya jefa masa.
Bai ko bude baki ba Barista Shafa'atu ta sake cewa objection wato bata amince da tambayar ba.
Baristar Dalhatu yayi saurin cewa "wannan tambayar tana da mahimmanci domin sanin wane ne Babawo kafin a tuhume shi da laifi irin wannan"
Alkali yace "objection over ruled, Barista ka cigaba da tambayarka"
Sai da ya bi Mawadda da kallo sannan ya fara basu labarin rayuwarsa da karatunsa da kuma dawowarsa wata hudu da suka wuce. Ya cigaba da sanar dasu cewa shi mutum ne mai mugun kyankyami ko kofi mai aiki ta wanke baya iya amfani dashi sai ya sake wankewa. Shi a ka'idarsa ma babu wani abu da yake hada shi da masu aiki koda maigadi ne kuwa.
Yana gama jawabinsa Barista Dalhatu yace "My lord daga bayanan Babawo zamu iya gane cewa abu ne mai matukar wahala ace ya yiwa mai aikin gidansu fyade. Muna da shaidu da dama da zasu tabbatar mana da halayyar Babawo. Sannan kuma ita kanta Mawadda maganarta taci karo da korafinta. Ta nuna cewa ya dade yana binta kuma tasan manufarsa amma ta kasa sanar da kowa. Da wadannan dalilai nake rokon kotu da ta wanke Babawo domin kazafi ne kawai Mawadda tayi masa don cimma wata manufa tata"
Tasowa Barista Shafa'atu tayi bayan an bata izinin yiwa Babawo tambaya.
Duk motsinsa dazu tana kula da yadda yake bin Mawadda da kallo.
"Babawo kace kai mutum ne mai kyankyami sai dai ina so ka tuna girman rantsuwar da kayi a kotu farkon tsayuwarka a nan. Ka dubi wannan yarinyar da kyau zaka iya sake rantsuwa baka taba binta ka roki ta baka hadin kai ba?"
Kallon Mawadda yayi yana kokarin yi mata murmushi yaji ance
"Objection my lord, Babawo ya riga ya tabbatarwa kotu tsakaninsa da masu aikin gidansu. Idan an bani dama zan gabatar da shaidata ta farko"
Korafin Barista Dalhatu ya karbo Alkali Dawud ya umarci Barista Shafa'atu da ta chanja tambayarta. Komawa tayi ta zauna tana jiran shaidar da zasu kawo domin tasan me ya kamata tayi.
Mal Ramadan maigadi ne ya gurfana gaban kotu. Barista Dalhatu yayi masa tambaya ya kuma tabbatar musu da cewa Babawo baya shiga sabgarsu. Kai hatta mota idan ya goge masa in zai fita sai yasa hankici yake budeta wai akwai kwayoyin cuta a hannun maigadin. Aka tambayeshi game da Mawadda ya kallota da dan murmushin tausayawa a fuskarsa.
"Yarinya ce mai nutsuwa don gidan basu taba mai aiki irinta ba. Bata da hayaniya ko kadan shiyasa Na'ibi mai kiyos yake matukar sonta"
Maganganu ne suka fara tashi da kuma kallon kallo daga Mawadda zuwa Babawo da Maigadi.
Shi kuwa Barista Dalhatu dama sun shiryo abinsu ne. Abaibai suka dunkulewa Mal Ramadan bayanin shaidar da zai kawo kotu ana neman wanda yayi mata fyade ne. Tausayinta yaji amma baiyi zaton nema ake a dorawa wanda bashi da hakki laifi ba. Duk wata dabarar boye gaskiya ita Barista yayi amfani da ita ya ha'inci maigadin.
"Ko za ka iya sanar da kotu tsahon yaushe kake aiki a gidan Alh Sule." Ya yi masa tambayar yana murmushi don abu ya fara tafiya yadda yake so.
"Shekara biyar da kusan rabi"
"A iya zamanka ka taba ganin Babawo wato BB yana kula wata mai aiki mace fiye da alakar ubangida da hadiminsa?"
"Oga BB bashi da sakin fuska kuma gashi baya boye kyamarmu da yake yi"
Hankalin su Ade ya soma tashi da jin amsoshin nan suna ganin kamar ma an gama shari'ar sun sha kasa.
"Naji kayi maganar wani mai kiyos muna bukatar karin haske game da mu'amalarsa da Mawadda"
"Ehhhh to, Na'ibi ya jima yana sonta don yana yawan bani sako haka su kayan kwadayi kamar biskit yace na mika mata....to amm..."
Bai bashi damar karasawa ba yayi wata shu'umar dariya "My lord nasan zuwa yanzu kowa ya fara fahimtar inda shari'ar nan ta dosa. Mawadda bata da alaka da Babawo amma akwai wani abu tsakaninta da Na'ibi mai kiyos. Anya babu lauje cikin nadi a zaman nan kuwa? Anya ba wani ne yasa Mawadda kama sunan dan ubangidanta ba domin su samu su tatsi wani abu a jikin mutane masu mutumci kamar su Haj Mara ba"
Ran Barista Shafa'atu ya soma baci ga shari'a tana neman komawa hannun abokan hamayya sannan ita ko kadan Mawadda bata ambaci sunan wani mai kiyos ba. Kanta ya kulle ta rasa me zatayi. Tashi tayi ta nuna bata gamsu da furucin Barista Dalhatu ba domin yana neman karkata akalar shari'ar kan wani daban bayan kuma har yanzu ba'a wanke Babawo ba.
Alkali ya karbi korafinta sannan aka bukaci Haj Mara ta taso. Hankali kwance taje ta tsaya.
Ajiyar zuciya Barista Shafa'atu tayi tana kallonta. Shigar mutumci tayi harda hijab fuskarta fayau kalar tausayi.
"Haj Mara a ranar shahudu ga watan Yuni kin koma gida kin tarar da danki ya yiwa mai aikinku fyade bayan mugun duka da yayi mata. Ke kika taimakata ma tayi wanka sannan tsoron tonon asiri duk da raunukan dake jikinta kika ki kaita asibiti. Dadin dadawa kika dauketa kika mayar gida batare da yiwa iyayenta bayani ba"
"As....as...sal...salam...as..."sai kawai kuka ya kufce mata mai sauti da tsuma zuciya. Ta kwashi wurin minti biyu tana kuka tana goge hawaye.
"Ku gafarceni, assalam alaikum. Ni dai sunana Marakisiyya kuma nice mahaifiyar Babawo. Nayi mamaki matuka ranar da sammacin kotun nan ya iso garemu har gani na rinka yi ko anyi kuskure ne."
Ta kalli Mawadda idanunta jazur "Mawadda me nayi miki a duniya zakiyi min wannan sakayyar? Tabbas nasan ni mutum ce mai zafi bazan boye ba. Amma hakan bai hanani rungumar duk wata maiaiki ba saboda nasan da na kowa ne. Me muka yi miki Mawadda har kika rasa wanda zaki kai kotu sai ni? Ni bazan tonawa kaina asirin zaman da mukayi ba balle na kwashe ladana da baki. Idan kotu ta kamamu da laifi ayi mana duk hukuncin da ya dace." Ta kare a raunane.
Mutane sai tausayinta suke ji. Mace kamar wannan wadda ko ba'a fada ba zaka san cewa arziki ya zauna mata take yiwa yarinya karama kuka.
Da kyar aka iya rarrashinta ta bada nata jawabin kamar haka.
"Banyi niyar tozartaki ba Mawadda amma kin nuna min da gaske ne da ake cewa kayiwa mutum inuwa shi kuma ya kaika rana. Ya maigirma mai shari'a yarinyar nan satar da take min bazata kirgu ba ina kawar da kai. Da zata tafi iyayenta shaida ne ba karamin tanadi nayi mata ba. Yaron da ake magana a kai wato Na'ibi, kiyos gareshi kusa damu. Daga aike a hankali na fuskanci ko ban nema ba sai tayi kwalliya tace min akwai aike? Idan nace babu sai tace zata dan fita. Ban kawo komai a rai ba nake kyaleta. Sai kawai wata rana aka kawo min zancen an ganta a dakinsa. Nayi kuka nagode Allah. Sakacina shine rashin mayar da hankali da na fuskanci ta fiye yawo amma banyi mata zaton yawon banza ba. Wannan abin shine ya daga min hankali nace gara ta koma gida kada a haifi da mara ido. Tayi kukan tayi magiya duk a banza don bazan boye muku ba ranar har dukanta nayi. Na hukuntata kamar yadda zanyiwa 'yar cikina. Ina fita ne ta shigar min daki sata Babawo ya kamata shima zuciya ta kwashe shi ya mareta. Washegari na maidata gida bamu sake jin komai ba sai kararmu da aka kawo"
Mawadda kuka iyayenta kuka. Hatta Baba hawaye yake yi sosai.
Alkali Dawud yace idan suna da shaidar da zasu kawo ana bukata. Waige waige suka soma yi ba Dr Tani ba dalilinta. Wani mai kaya irin na masinja ne ya fadi uzurinta cewa ta taho aka kirata patient din da ta yiwa aiki tana zubar da jini. Wannan dalilin ya sanya aka dage sauraron karar sai bayan kwana goma sha biyu.
A sanyaye suka tashi kafin su fita Barista Shafa'atu ta hau Mawadda da fadan me yasa bata yi mata zancen Na'ibi ba. Su Iya suka tsaya sauraronta tana fada mata cewa da gaske ne ya nuna yana sonta amma da wuri ta sanar dashi aure zata yi. Kuma duk wata kyauta da yake bawa Ramadan maigadi ko tsinke bata taba karba ba. Game da zuwa kiyos dinsa tun da ta gane yana sonta ta gwammace ta tsallaka titi idan an aiketa. Dama yawanci siyan katin waya ne yake kaita. Kafin faruwar wannan abu gareta kuwa yafi wata bata ganinsa. Kiyos din ma ya koma shagon renting din finafinan hausa shi kuma bata san inda yayi ba.
"Wato sun nemo wanda baya nan bare ya kare kansa shine za'a dora masa laifin da baiji ba bai gani ba" Barista Shafa'atu ta fada tana rubutu.
Mawadda ta kalleta "wallahi babu karya a duk abinda na fada miki"
Murmushi tayi "na sani Mawadda kuma in sha Allah sai an kulle BB an bi miki hakkinki"
"Idan ba mu muka ci shari'ar ba ni za'a kulle kenan?" Yadda tayi maganar da raunin murya yasa Baba fita hankalinsa duk a tashe yake ya rasa me zaiyi ya samarwa 'yarsa farincikin rayuwa.
Fitarsa waje ke da wuya yaji wasu suna tattaunawa suna aibata 'yan kauye a matsayin kwadayayyu wadanda basa iya rike talaucinsu.
"Tsabagen son zuciya ke dibarsu su kwaso rida-ridan 'yan mata a kawosu birni aiki."
Wani yace "sai ta kwabe musu ayi ta dauki ba dadi"
"Idan basuyi haka ba ai basu amsa sunansu na 'yan kauye ba. Da anyi magana sai ace an turo yarinya tara kudin da za'a yi mata kayan daki."
Zuciya ta kwaso Mal Fatihu, ransa ya kai makurar baci ya karasa gaban wadannan mazan cikin daga murya wanda ya janyowa kansa taruwar 'yan jarida yace
"Objection sustained! Barista Dalhatu ka gyara kalamanka ko ka chanja tambayar" Alkali ya fada masa.
Dan sunkuyar da kai yayi "Nagode my lord. Idan kotu ta bani dama ina son yiwa wanda ake tuhuma tambayoyi"
Alkali ya bashi dama tare da umartar Mawadda ta koma ta zauna.
"Babawo Sule Chanji ko zamu iya jin takaitaccen tarihinka?" Ita ce tambayar da ya jefa masa.
Bai ko bude baki ba Barista Shafa'atu ta sake cewa objection wato bata amince da tambayar ba.
Baristar Dalhatu yayi saurin cewa "wannan tambayar tana da mahimmanci domin sanin wane ne Babawo kafin a tuhume shi da laifi irin wannan"
Alkali yace "objection over ruled, Barista ka cigaba da tambayarka"
Sai da ya bi Mawadda da kallo sannan ya fara basu labarin rayuwarsa da karatunsa da kuma dawowarsa wata hudu da suka wuce. Ya cigaba da sanar dasu cewa shi mutum ne mai mugun kyankyami ko kofi mai aiki ta wanke baya iya amfani dashi sai ya sake wankewa. Shi a ka'idarsa ma babu wani abu da yake hada shi da masu aiki koda maigadi ne kuwa.
Yana gama jawabinsa Barista Dalhatu yace "My lord daga bayanan Babawo zamu iya gane cewa abu ne mai matukar wahala ace ya yiwa mai aikin gidansu fyade. Muna da shaidu da dama da zasu tabbatar mana da halayyar Babawo. Sannan kuma ita kanta Mawadda maganarta taci karo da korafinta. Ta nuna cewa ya dade yana binta kuma tasan manufarsa amma ta kasa sanar da kowa. Da wadannan dalilai nake rokon kotu da ta wanke Babawo domin kazafi ne kawai Mawadda tayi masa don cimma wata manufa tata"
Tasowa Barista Shafa'atu tayi bayan an bata izinin yiwa Babawo tambaya.
Duk motsinsa dazu tana kula da yadda yake bin Mawadda da kallo.
"Babawo kace kai mutum ne mai kyankyami sai dai ina so ka tuna girman rantsuwar da kayi a kotu farkon tsayuwarka a nan. Ka dubi wannan yarinyar da kyau zaka iya sake rantsuwa baka taba binta ka roki ta baka hadin kai ba?"
Kallon Mawadda yayi yana kokarin yi mata murmushi yaji ance
"Objection my lord, Babawo ya riga ya tabbatarwa kotu tsakaninsa da masu aikin gidansu. Idan an bani dama zan gabatar da shaidata ta farko"
Korafin Barista Dalhatu ya karbo Alkali Dawud ya umarci Barista Shafa'atu da ta chanja tambayarta. Komawa tayi ta zauna tana jiran shaidar da zasu kawo domin tasan me ya kamata tayi.
Mal Ramadan maigadi ne ya gurfana gaban kotu. Barista Dalhatu yayi masa tambaya ya kuma tabbatar musu da cewa Babawo baya shiga sabgarsu. Kai hatta mota idan ya goge masa in zai fita sai yasa hankici yake budeta wai akwai kwayoyin cuta a hannun maigadin. Aka tambayeshi game da Mawadda ya kallota da dan murmushin tausayawa a fuskarsa.
"Yarinya ce mai nutsuwa don gidan basu taba mai aiki irinta ba. Bata da hayaniya ko kadan shiyasa Na'ibi mai kiyos yake matukar sonta"
Maganganu ne suka fara tashi da kuma kallon kallo daga Mawadda zuwa Babawo da Maigadi.
Shi kuwa Barista Dalhatu dama sun shiryo abinsu ne. Abaibai suka dunkulewa Mal Ramadan bayanin shaidar da zai kawo kotu ana neman wanda yayi mata fyade ne. Tausayinta yaji amma baiyi zaton nema ake a dorawa wanda bashi da hakki laifi ba. Duk wata dabarar boye gaskiya ita Barista yayi amfani da ita ya ha'inci maigadin.
"Ko za ka iya sanar da kotu tsahon yaushe kake aiki a gidan Alh Sule." Ya yi masa tambayar yana murmushi don abu ya fara tafiya yadda yake so.
"Shekara biyar da kusan rabi"
"A iya zamanka ka taba ganin Babawo wato BB yana kula wata mai aiki mace fiye da alakar ubangida da hadiminsa?"
"Oga BB bashi da sakin fuska kuma gashi baya boye kyamarmu da yake yi"
Hankalin su Ade ya soma tashi da jin amsoshin nan suna ganin kamar ma an gama shari'ar sun sha kasa.
"Naji kayi maganar wani mai kiyos muna bukatar karin haske game da mu'amalarsa da Mawadda"
"Ehhhh to, Na'ibi ya jima yana sonta don yana yawan bani sako haka su kayan kwadayi kamar biskit yace na mika mata....to amm..."
Bai bashi damar karasawa ba yayi wata shu'umar dariya "My lord nasan zuwa yanzu kowa ya fara fahimtar inda shari'ar nan ta dosa. Mawadda bata da alaka da Babawo amma akwai wani abu tsakaninta da Na'ibi mai kiyos. Anya babu lauje cikin nadi a zaman nan kuwa? Anya ba wani ne yasa Mawadda kama sunan dan ubangidanta ba domin su samu su tatsi wani abu a jikin mutane masu mutumci kamar su Haj Mara ba"
Ran Barista Shafa'atu ya soma baci ga shari'a tana neman komawa hannun abokan hamayya sannan ita ko kadan Mawadda bata ambaci sunan wani mai kiyos ba. Kanta ya kulle ta rasa me zatayi. Tashi tayi ta nuna bata gamsu da furucin Barista Dalhatu ba domin yana neman karkata akalar shari'ar kan wani daban bayan kuma har yanzu ba'a wanke Babawo ba.
Alkali ya karbi korafinta sannan aka bukaci Haj Mara ta taso. Hankali kwance taje ta tsaya.
Ajiyar zuciya Barista Shafa'atu tayi tana kallonta. Shigar mutumci tayi harda hijab fuskarta fayau kalar tausayi.
"Haj Mara a ranar shahudu ga watan Yuni kin koma gida kin tarar da danki ya yiwa mai aikinku fyade bayan mugun duka da yayi mata. Ke kika taimakata ma tayi wanka sannan tsoron tonon asiri duk da raunukan dake jikinta kika ki kaita asibiti. Dadin dadawa kika dauketa kika mayar gida batare da yiwa iyayenta bayani ba"
"As....as...sal...salam...as..."sai kawai kuka ya kufce mata mai sauti da tsuma zuciya. Ta kwashi wurin minti biyu tana kuka tana goge hawaye.
"Ku gafarceni, assalam alaikum. Ni dai sunana Marakisiyya kuma nice mahaifiyar Babawo. Nayi mamaki matuka ranar da sammacin kotun nan ya iso garemu har gani na rinka yi ko anyi kuskure ne."
Ta kalli Mawadda idanunta jazur "Mawadda me nayi miki a duniya zakiyi min wannan sakayyar? Tabbas nasan ni mutum ce mai zafi bazan boye ba. Amma hakan bai hanani rungumar duk wata maiaiki ba saboda nasan da na kowa ne. Me muka yi miki Mawadda har kika rasa wanda zaki kai kotu sai ni? Ni bazan tonawa kaina asirin zaman da mukayi ba balle na kwashe ladana da baki. Idan kotu ta kamamu da laifi ayi mana duk hukuncin da ya dace." Ta kare a raunane.
Mutane sai tausayinta suke ji. Mace kamar wannan wadda ko ba'a fada ba zaka san cewa arziki ya zauna mata take yiwa yarinya karama kuka.
Da kyar aka iya rarrashinta ta bada nata jawabin kamar haka.
"Banyi niyar tozartaki ba Mawadda amma kin nuna min da gaske ne da ake cewa kayiwa mutum inuwa shi kuma ya kaika rana. Ya maigirma mai shari'a yarinyar nan satar da take min bazata kirgu ba ina kawar da kai. Da zata tafi iyayenta shaida ne ba karamin tanadi nayi mata ba. Yaron da ake magana a kai wato Na'ibi, kiyos gareshi kusa damu. Daga aike a hankali na fuskanci ko ban nema ba sai tayi kwalliya tace min akwai aike? Idan nace babu sai tace zata dan fita. Ban kawo komai a rai ba nake kyaleta. Sai kawai wata rana aka kawo min zancen an ganta a dakinsa. Nayi kuka nagode Allah. Sakacina shine rashin mayar da hankali da na fuskanci ta fiye yawo amma banyi mata zaton yawon banza ba. Wannan abin shine ya daga min hankali nace gara ta koma gida kada a haifi da mara ido. Tayi kukan tayi magiya duk a banza don bazan boye muku ba ranar har dukanta nayi. Na hukuntata kamar yadda zanyiwa 'yar cikina. Ina fita ne ta shigar min daki sata Babawo ya kamata shima zuciya ta kwashe shi ya mareta. Washegari na maidata gida bamu sake jin komai ba sai kararmu da aka kawo"
Mawadda kuka iyayenta kuka. Hatta Baba hawaye yake yi sosai.
Alkali Dawud yace idan suna da shaidar da zasu kawo ana bukata. Waige waige suka soma yi ba Dr Tani ba dalilinta. Wani mai kaya irin na masinja ne ya fadi uzurinta cewa ta taho aka kirata patient din da ta yiwa aiki tana zubar da jini. Wannan dalilin ya sanya aka dage sauraron karar sai bayan kwana goma sha biyu.
A sanyaye suka tashi kafin su fita Barista Shafa'atu ta hau Mawadda da fadan me yasa bata yi mata zancen Na'ibi ba. Su Iya suka tsaya sauraronta tana fada mata cewa da gaske ne ya nuna yana sonta amma da wuri ta sanar dashi aure zata yi. Kuma duk wata kyauta da yake bawa Ramadan maigadi ko tsinke bata taba karba ba. Game da zuwa kiyos dinsa tun da ta gane yana sonta ta gwammace ta tsallaka titi idan an aiketa. Dama yawanci siyan katin waya ne yake kaita. Kafin faruwar wannan abu gareta kuwa yafi wata bata ganinsa. Kiyos din ma ya koma shagon renting din finafinan hausa shi kuma bata san inda yayi ba.
"Wato sun nemo wanda baya nan bare ya kare kansa shine za'a dora masa laifin da baiji ba bai gani ba" Barista Shafa'atu ta fada tana rubutu.
Mawadda ta kalleta "wallahi babu karya a duk abinda na fada miki"
Murmushi tayi "na sani Mawadda kuma in sha Allah sai an kulle BB an bi miki hakkinki"
"Idan ba mu muka ci shari'ar ba ni za'a kulle kenan?" Yadda tayi maganar da raunin murya yasa Baba fita hankalinsa duk a tashe yake ya rasa me zaiyi ya samarwa 'yarsa farincikin rayuwa.
Fitarsa waje ke da wuya yaji wasu suna tattaunawa suna aibata 'yan kauye a matsayin kwadayayyu wadanda basa iya rike talaucinsu.
"Tsabagen son zuciya ke dibarsu su kwaso rida-ridan 'yan mata a kawosu birni aiki."
Wani yace "sai ta kwabe musu ayi ta dauki ba dadi"
"Idan basuyi haka ba ai basu amsa sunansu na 'yan kauye ba. Da anyi magana sai ace an turo yarinya tara kudin da za'a yi mata kayan daki."
Zuciya ta kwaso Mal Fatihu, ransa ya kai makurar baci ya karasa gaban wadannan mazan cikin daga murya wanda ya janyowa kansa taruwar 'yan jarida yace