Sashe 67
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi tayi Nawal ta zungureta.
"Ade na kallonki dai hajiyar soyayya"
Tana dagowa suka hada ido da Ade kuwa ta rufe ido tana dariya. Sai dare suka bar gidan bayan doguwar nasiha daga Baba da kuma karin godiya ga Dahiru.
A wannan rana da hankulansu suke a kwance Dahiru da Mawadda sunyi kwanan farinciki da dimbin soyayya. Basa ji basa ganin kowa sai junansu.
Bayan kwana biyu suka wuce Tariwa harda su Baba gabadaya. Gabanta har faduwa ya rinka yi akan hanya saboda yadda take ji. Yara da manya tun a hanya suka yiwa motocin dafifi aka rakasu har kofar gidan Maigari dattijon arziki irin albarka.
Shima fitowa yayi yana zaune jamaa sun zagaye shi ta kowane bangare yayi musu nasiha da jankunne akan rayuwa. Mawadda da take sanye da kaya na alfarma kana ganinta kasan ta wuce sa'a ya nuna musu tare da tunatar dasu babban abinda ya kamata a hadu a yiwa mutane irinta wato tsayawa juna da kuma tausasawa.
Ita da su Yaya sun sha kuka mata suka yi ta rumgumarsu ana murna. Satinsu guda a garin suna zaga 'yan uwa sannan suka koma gida.
*****
Sati uku kenan da gama shari'arsu BB aka kira Dahiru da Mawadda kotu domin karbar kudin tarar da aka yankewa Haj Mara.
Alh Sule suka gani ya bada cheque na miliyan biyar. Dahiru ya duba da kyau yace ba haka Alkali tace ba.
Nannauyan numfashi Alh Sule ya saukar "na sani kuma kudin da na kara ba fansar mutumcin Mawadda bane da dana ya tozarta. Na bata ne domin tun shekarun baya naso haduwa da ita Allah bai nufa ba. Allah Ya gani ban goyi bayan abinda akayi miki ba amma bansan inda zan same ki ba. Wannan kudin duka harda na Marakisiyya ne. Shine abu na karshe da zan iya yi mata don nasan ko wuka zaa saka mata yanzu bata da inda zata fitar da wannan kudin. Idan da hali ko don rage nauyi da hakki kuji tausayina don Allah ku yafewa Babawo. Nasan zaku ce wannan tsoho da son kai yake. Sai dai kaddara idan ta hadu da son zuciya rayuwar mutum sai ta lalace. Babawo bashi da sauran gata sai yafiyarku a gareshi"
Fuskar kamala da dattako ta Alh Sule Chanji ita ta sanya Dahiru ya dubi Mawadda.
"Idan har na isa...."
"Ka isa Yayanmu" ta katse shi "Na yafe masa Alhaji"
Bata kara cewa komai ba bayan wannan ta fita daga wurin ta nufi motarsu. Dahiru ne ya karasa komai yazo ya sameta jingine da motar tana tunani. A gefenta ya tsaya.
"Kinsan me na tuna?"
Ta juyo ta kalle shi "me?"
"Ranar da na fara sake ganinki. Wallahi da kika fito ba karamar dauriya da jarumta nayi wurin kin fitowa na rungumeki ba. You looked so sweet lokacin"
"Yanzu fa?" Ta tsare shi da ido.
"Mawadda ce Dahiru, Dahiru kuma Mawadda..."
Kallon fuskarsa tayi suka hada ido a hankali tace "I love you"
Bude mata kofa yayi ta zauna ya rufe sannan ya zagaya ya zauna shima. Hannunta ya kamo ya sarke yatsunsu yana kallon yadda nata suka yi kyau sun sha jan lalle.
"Ina rokon Allah Ya kara min sonki da kaunarki kuma Ya bani ikon kulawa dake har karshen rayuwarmu."
Kwalla ce ta cika mata ido yana gani hawayen ya soma diga duk ya rude.
"Na bata miki rai ne?"
Ta girgiza kai da sauri sannan ta kwantar da kanta a jikin kujera soyayyar Dahiru tana sake cika mata zuciya. Har tunani take yi me zata yi domin faranta zuciyarsa. Kallonsa tayi idanunta kamar tana shirin bacci.
"Ka kaini gida kada nayi abin kunya a gefen titi"
Jin haka ya ware idanunsa a kanta "abin kunya kuma?"
A kagauce ta kalle shi "mu tafi mana da gaske nake"
Tayar da motar yayi suna tafiya yana kallonta yana tsoron me zata yi. Suna zuwa gida ta fice ta barshi a tsaye da rikon baki.
Da saurinsa ya bita suka ci karo a bakin kofa ta cire mayafi da dankwali ga wani zanin a hannunta.
"Ina zuwa?"
Haki take yi saboda gudun da tayi na hawa saman ta durkusa a gabansa ta juya baya.
"Hau"
"Ina?"
"Goyaka zanyi Mijin Mawadda na kaika daki sai nayi abinda ba na kunya ba yanzu tunda mun dawo gida"
Sai da ya gama dariya ya ga ta sha kunu ita da gaske take.
"A wannan dan bayan? Na kagu dai naga abin kunyar nima na koya" ya dora hannunsa a tsakiya.
Murya na rawa tace "Na rasa me zanyi maka a duniya kasan cewa nagode da duka abubuwan da kake yi min."
Tayar da ita yayi ta soma kuka ya rungumeta.
"Abu daya zaki yi min"
Ta dago kai da sauri "me kake so?"
"Mu zamewa juna komai na rayuwa. Abokai, 'yan uwa, masoya da duk wani abu da kika san yana kara shakuwa. Banyi miki komai don kice kin gode ba. Allah ne Ya saka ki a nan" ya dora hannunta a saitin zuciyarsa.
Ga ido fal hawaye ta soma murmushi kuma kunyarsa tana saukar mata. Matseta yayi a jikinsa ya soma shagwabar da ta riga ta sallama masa "zaki goyani din muje ki nuna min abin da kika ce?"
Ta zille "a wane bayan?"
"Irin yadda muka yi a asibiti zaki yi min kinji Mawadda mana"
"Ya na iya tunda ka iya dadin baki"
Dakin suka shige suna yiwa juna dariya yana cewa sai tayi abinda ta fada tana cewa ta fasa.
*******
Abu kamar wasa bikin Qareeba da Bilya saura sati biyu. Dama wata uku aka saka gashi lokaci ya gabato. Dr Tani da mijinta harma da 'yan uwan Qareeba maza kowa ya nuna bajinta ajin farko. Sun kashe kudi sosai wurin kawata gidan da Bilya ya kama mata babu nisa da su Dahiru.
Bisa shawarar Nawal da amincewar Attahir tunda gida dai nasu ne su biyu Dahiru ya gyarawa Mawadda dakin da yake a matsayin na maigadi a gidan da dan karamin bandakinsa wurin ya koma bangaren gyaran jiki. Watanta guda da farawa yawancin costumers dinta na da da ma 'yan unguwar da suka fara ganeta suka soma zuwa kasuwa ta fara budewa.
Wanna satin ta rufe karbar kowa sai Anti Qareeba. Gyara take yi mata sosai su wuni suna hira harda Nawal.
Yau da wuri suka fara saboda Dahiru yace zai zo su fita. Wayarta ce ta soma kara tayi zaton ya taho ne ta ga ashe Nawal ce.
" 'Yar uwa yau naji shiru ko zazzabin ne? Na ga Dan uwanmu bai fita ba shiyasa ban shigo ba"
Attahir ne da kansa ashe hankalinsa daga ji a tashe yake "asibiti zan kaita ta dora girki ne don Allah ko zaki karasa"
Mayafinta ta yafa tana yiwa Qareeba bayani. Zamanta kenan ko kaya bata cire ba ta bita suka yi sallama. Gabadaya babu kwari jikin Nawal din Attahir ya rikota ta kasa tsayuwa.
Mawadda tana mata sannu itama a rude Qareeba tace
"Allah Yasa dai baki sha wasu magungunan zazzabin ba da alama ciki ne."
Duk da hankalinsa a tashe yake bai hana murmushi bayyana a fuskar a Attahir ba.
"Da gaske?"
Nawal ta rufe ido tana jin kunya saboda dama tayi tunanin hakan. Kallonta yayi yana murmushi "da gaske akwai babyna a nan...."
"Ehem ehemmm" Qareeba tace tana kamo hannun Mawadda itama kunya ta kamata.
"Ina ne kitchen din naji kauri"
Shigewa suka yi Attahir yana ganin sun shige ya daga Nawal yana murna.
"Ka bari ayi confirming mana"
"Ni nayi. Dama na kula sai wani cikowa kike yi ashe ashe yarinyar nan ta girma"
Mawadda ta kalli Qareeba tana dariyar shakiyanci don suna jin su Attahir har suka fita "ni dai idan ina da ciki kada wanda yazo ranar farko"
"Saboda me?"
"Daga ni har Mijin Mawadda nasan zamu taba abin kunya a gaban mutane"
Dama tsokana ce take yi ai kuwa Qareeba ta hau dariya kamar me tana cewa ya kamata ko kuda ne ta zama ranar don ganin kwaf.
"Da kallon wata saliha nake miki fa"
Mawadda tayi dariya "Antinmu bari dai mu kaiki gidan Yaya Bilya zaki bamu labari"
Qareeba tace "Allah ko? Wayyo ni kinsa naji kamar na matso da bikin"
Tsokanar juna suka shiga yi har suka karasa girkin da gyara kitchen din sannan aka fara aiki.
Dinkuna na gani na fada Mawadda tayi a kayan da Dahiru ya saya mata na fitar biki. Dasu ake komai don ma Nawal tana fama da laulayi mai wahala.
Ranar kamu wani tsadadden leshi ruwan madara da adon shudi Qareeba ta saka anyi mata dinkin buba. Zanin akan rigar ta daura sai ashoke blue da gold da takalmi da jaka suma gold.
Tayi kyau sosai ta fito a amaryarta. Murmushin farincikinta yaki buya saboda wannan ranar daban take a wurinta. Manyan kawayenta wanda kuma su kadai ne kawayen da suka dade tare Jameela da Fatima 'yan shagwaba irinta sune kan gaba wurin komai.
Zuwa yanzu sun zama tamkar 'yan uwa da su Ade shiyasa suka zo akayi komai tare dasu saboda yadda Dr Tani take shige musu duk don ta nuna nadamarta kuma ta samu 'yarta ta zauna lafiya.
Anyi bikin kwana hudu events kala kala an gama lafiya. Bayan an gama taron yini ango da kansa yazo daukar amarya bisa yarjewar mahaifinta don tun abinda ya sami Mawadda sun tsorata da kai amarya.
Dr Tani tana ta kuka ta kankame Qareeba ita kuwa ko gezau. Sai da ta sake rungumeta a kunne ta rada mata "to sarkin shirme ki dan matso kwalla mana"
"Kai Mummy kwalliyata sai ta baci ya ganni banyi kyau ba"
Dr Tani ta sake make murya "kinga kallonki ake yi. Ko dan yaya ne ki danyi kinji. Haka al'ada take"
Zumburo baki tayi sannan ta ja mayafi ta rufe fuskarta ta soma ihun kuka "yeeeeee"
Hakuri aka soma bata a ranta tace dama sun bar bata bakinsu yau ranar murna ce a gareta.
Bakin mota aka rakota Bilya ya kasa fitowa saboda kunyar jama'a. Bude mata yayi yana daga ciki ta shigo kamshin jikinta ya cika motar.
Kafin su bar layin ta soma kokarin bude fuska ya rike hannun. Wani abu yaji ya tsirga masa har kafa a tausashe yace
"Akwai mutane fa kada ki bude su gane min amaryata kafin na fara gani"
"Ade na kallonki dai hajiyar soyayya"
Tana dagowa suka hada ido da Ade kuwa ta rufe ido tana dariya. Sai dare suka bar gidan bayan doguwar nasiha daga Baba da kuma karin godiya ga Dahiru.
A wannan rana da hankulansu suke a kwance Dahiru da Mawadda sunyi kwanan farinciki da dimbin soyayya. Basa ji basa ganin kowa sai junansu.
Bayan kwana biyu suka wuce Tariwa harda su Baba gabadaya. Gabanta har faduwa ya rinka yi akan hanya saboda yadda take ji. Yara da manya tun a hanya suka yiwa motocin dafifi aka rakasu har kofar gidan Maigari dattijon arziki irin albarka.
Shima fitowa yayi yana zaune jamaa sun zagaye shi ta kowane bangare yayi musu nasiha da jankunne akan rayuwa. Mawadda da take sanye da kaya na alfarma kana ganinta kasan ta wuce sa'a ya nuna musu tare da tunatar dasu babban abinda ya kamata a hadu a yiwa mutane irinta wato tsayawa juna da kuma tausasawa.
Ita da su Yaya sun sha kuka mata suka yi ta rumgumarsu ana murna. Satinsu guda a garin suna zaga 'yan uwa sannan suka koma gida.
*****
Sati uku kenan da gama shari'arsu BB aka kira Dahiru da Mawadda kotu domin karbar kudin tarar da aka yankewa Haj Mara.
Alh Sule suka gani ya bada cheque na miliyan biyar. Dahiru ya duba da kyau yace ba haka Alkali tace ba.
Nannauyan numfashi Alh Sule ya saukar "na sani kuma kudin da na kara ba fansar mutumcin Mawadda bane da dana ya tozarta. Na bata ne domin tun shekarun baya naso haduwa da ita Allah bai nufa ba. Allah Ya gani ban goyi bayan abinda akayi miki ba amma bansan inda zan same ki ba. Wannan kudin duka harda na Marakisiyya ne. Shine abu na karshe da zan iya yi mata don nasan ko wuka zaa saka mata yanzu bata da inda zata fitar da wannan kudin. Idan da hali ko don rage nauyi da hakki kuji tausayina don Allah ku yafewa Babawo. Nasan zaku ce wannan tsoho da son kai yake. Sai dai kaddara idan ta hadu da son zuciya rayuwar mutum sai ta lalace. Babawo bashi da sauran gata sai yafiyarku a gareshi"
Fuskar kamala da dattako ta Alh Sule Chanji ita ta sanya Dahiru ya dubi Mawadda.
"Idan har na isa...."
"Ka isa Yayanmu" ta katse shi "Na yafe masa Alhaji"
Bata kara cewa komai ba bayan wannan ta fita daga wurin ta nufi motarsu. Dahiru ne ya karasa komai yazo ya sameta jingine da motar tana tunani. A gefenta ya tsaya.
"Kinsan me na tuna?"
Ta juyo ta kalle shi "me?"
"Ranar da na fara sake ganinki. Wallahi da kika fito ba karamar dauriya da jarumta nayi wurin kin fitowa na rungumeki ba. You looked so sweet lokacin"
"Yanzu fa?" Ta tsare shi da ido.
"Mawadda ce Dahiru, Dahiru kuma Mawadda..."
Kallon fuskarsa tayi suka hada ido a hankali tace "I love you"
Bude mata kofa yayi ta zauna ya rufe sannan ya zagaya ya zauna shima. Hannunta ya kamo ya sarke yatsunsu yana kallon yadda nata suka yi kyau sun sha jan lalle.
"Ina rokon Allah Ya kara min sonki da kaunarki kuma Ya bani ikon kulawa dake har karshen rayuwarmu."
Kwalla ce ta cika mata ido yana gani hawayen ya soma diga duk ya rude.
"Na bata miki rai ne?"
Ta girgiza kai da sauri sannan ta kwantar da kanta a jikin kujera soyayyar Dahiru tana sake cika mata zuciya. Har tunani take yi me zata yi domin faranta zuciyarsa. Kallonsa tayi idanunta kamar tana shirin bacci.
"Ka kaini gida kada nayi abin kunya a gefen titi"
Jin haka ya ware idanunsa a kanta "abin kunya kuma?"
A kagauce ta kalle shi "mu tafi mana da gaske nake"
Tayar da motar yayi suna tafiya yana kallonta yana tsoron me zata yi. Suna zuwa gida ta fice ta barshi a tsaye da rikon baki.
Da saurinsa ya bita suka ci karo a bakin kofa ta cire mayafi da dankwali ga wani zanin a hannunta.
"Ina zuwa?"
Haki take yi saboda gudun da tayi na hawa saman ta durkusa a gabansa ta juya baya.
"Hau"
"Ina?"
"Goyaka zanyi Mijin Mawadda na kaika daki sai nayi abinda ba na kunya ba yanzu tunda mun dawo gida"
Sai da ya gama dariya ya ga ta sha kunu ita da gaske take.
"A wannan dan bayan? Na kagu dai naga abin kunyar nima na koya" ya dora hannunsa a tsakiya.
Murya na rawa tace "Na rasa me zanyi maka a duniya kasan cewa nagode da duka abubuwan da kake yi min."
Tayar da ita yayi ta soma kuka ya rungumeta.
"Abu daya zaki yi min"
Ta dago kai da sauri "me kake so?"
"Mu zamewa juna komai na rayuwa. Abokai, 'yan uwa, masoya da duk wani abu da kika san yana kara shakuwa. Banyi miki komai don kice kin gode ba. Allah ne Ya saka ki a nan" ya dora hannunta a saitin zuciyarsa.
Ga ido fal hawaye ta soma murmushi kuma kunyarsa tana saukar mata. Matseta yayi a jikinsa ya soma shagwabar da ta riga ta sallama masa "zaki goyani din muje ki nuna min abin da kika ce?"
Ta zille "a wane bayan?"
"Irin yadda muka yi a asibiti zaki yi min kinji Mawadda mana"
"Ya na iya tunda ka iya dadin baki"
Dakin suka shige suna yiwa juna dariya yana cewa sai tayi abinda ta fada tana cewa ta fasa.
*******
Abu kamar wasa bikin Qareeba da Bilya saura sati biyu. Dama wata uku aka saka gashi lokaci ya gabato. Dr Tani da mijinta harma da 'yan uwan Qareeba maza kowa ya nuna bajinta ajin farko. Sun kashe kudi sosai wurin kawata gidan da Bilya ya kama mata babu nisa da su Dahiru.
Bisa shawarar Nawal da amincewar Attahir tunda gida dai nasu ne su biyu Dahiru ya gyarawa Mawadda dakin da yake a matsayin na maigadi a gidan da dan karamin bandakinsa wurin ya koma bangaren gyaran jiki. Watanta guda da farawa yawancin costumers dinta na da da ma 'yan unguwar da suka fara ganeta suka soma zuwa kasuwa ta fara budewa.
Wanna satin ta rufe karbar kowa sai Anti Qareeba. Gyara take yi mata sosai su wuni suna hira harda Nawal.
Yau da wuri suka fara saboda Dahiru yace zai zo su fita. Wayarta ce ta soma kara tayi zaton ya taho ne ta ga ashe Nawal ce.
" 'Yar uwa yau naji shiru ko zazzabin ne? Na ga Dan uwanmu bai fita ba shiyasa ban shigo ba"
Attahir ne da kansa ashe hankalinsa daga ji a tashe yake "asibiti zan kaita ta dora girki ne don Allah ko zaki karasa"
Mayafinta ta yafa tana yiwa Qareeba bayani. Zamanta kenan ko kaya bata cire ba ta bita suka yi sallama. Gabadaya babu kwari jikin Nawal din Attahir ya rikota ta kasa tsayuwa.
Mawadda tana mata sannu itama a rude Qareeba tace
"Allah Yasa dai baki sha wasu magungunan zazzabin ba da alama ciki ne."
Duk da hankalinsa a tashe yake bai hana murmushi bayyana a fuskar a Attahir ba.
"Da gaske?"
Nawal ta rufe ido tana jin kunya saboda dama tayi tunanin hakan. Kallonta yayi yana murmushi "da gaske akwai babyna a nan...."
"Ehem ehemmm" Qareeba tace tana kamo hannun Mawadda itama kunya ta kamata.
"Ina ne kitchen din naji kauri"
Shigewa suka yi Attahir yana ganin sun shige ya daga Nawal yana murna.
"Ka bari ayi confirming mana"
"Ni nayi. Dama na kula sai wani cikowa kike yi ashe ashe yarinyar nan ta girma"
Mawadda ta kalli Qareeba tana dariyar shakiyanci don suna jin su Attahir har suka fita "ni dai idan ina da ciki kada wanda yazo ranar farko"
"Saboda me?"
"Daga ni har Mijin Mawadda nasan zamu taba abin kunya a gaban mutane"
Dama tsokana ce take yi ai kuwa Qareeba ta hau dariya kamar me tana cewa ya kamata ko kuda ne ta zama ranar don ganin kwaf.
"Da kallon wata saliha nake miki fa"
Mawadda tayi dariya "Antinmu bari dai mu kaiki gidan Yaya Bilya zaki bamu labari"
Qareeba tace "Allah ko? Wayyo ni kinsa naji kamar na matso da bikin"
Tsokanar juna suka shiga yi har suka karasa girkin da gyara kitchen din sannan aka fara aiki.
Dinkuna na gani na fada Mawadda tayi a kayan da Dahiru ya saya mata na fitar biki. Dasu ake komai don ma Nawal tana fama da laulayi mai wahala.
Ranar kamu wani tsadadden leshi ruwan madara da adon shudi Qareeba ta saka anyi mata dinkin buba. Zanin akan rigar ta daura sai ashoke blue da gold da takalmi da jaka suma gold.
Tayi kyau sosai ta fito a amaryarta. Murmushin farincikinta yaki buya saboda wannan ranar daban take a wurinta. Manyan kawayenta wanda kuma su kadai ne kawayen da suka dade tare Jameela da Fatima 'yan shagwaba irinta sune kan gaba wurin komai.
Zuwa yanzu sun zama tamkar 'yan uwa da su Ade shiyasa suka zo akayi komai tare dasu saboda yadda Dr Tani take shige musu duk don ta nuna nadamarta kuma ta samu 'yarta ta zauna lafiya.
Anyi bikin kwana hudu events kala kala an gama lafiya. Bayan an gama taron yini ango da kansa yazo daukar amarya bisa yarjewar mahaifinta don tun abinda ya sami Mawadda sun tsorata da kai amarya.
Dr Tani tana ta kuka ta kankame Qareeba ita kuwa ko gezau. Sai da ta sake rungumeta a kunne ta rada mata "to sarkin shirme ki dan matso kwalla mana"
"Kai Mummy kwalliyata sai ta baci ya ganni banyi kyau ba"
Dr Tani ta sake make murya "kinga kallonki ake yi. Ko dan yaya ne ki danyi kinji. Haka al'ada take"
Zumburo baki tayi sannan ta ja mayafi ta rufe fuskarta ta soma ihun kuka "yeeeeee"
Hakuri aka soma bata a ranta tace dama sun bar bata bakinsu yau ranar murna ce a gareta.
Bakin mota aka rakota Bilya ya kasa fitowa saboda kunyar jama'a. Bude mata yayi yana daga ciki ta shigo kamshin jikinta ya cika motar.
Kafin su bar layin ta soma kokarin bude fuska ya rike hannun. Wani abu yaji ya tsirga masa har kafa a tausashe yace
"Akwai mutane fa kada ki bude su gane min amaryata kafin na fara gani"