Sashe 42
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fuskar Baffa ta nuna rashin jindadi "nasan bamu kyauta ba kuma bazan gaji da baka hakuri ba. Amma rashin amincewarka yanzu tamkar baka mayar da komai ya wuce din bane kamar yadda ka fada min"
Dariya yayi
"Kada ka daureni Mal Isiyaku. Ai shi ya gani da idanunsa yarinyar nan har yanzu fa bata gama dawowa daidai ba. Abu kadan yake zaburar da ita ta firgita. Karin nauyi kawai zamu bashi idan aka aura masa ita"
"Sauki na Allah ne. Ni dai zuwan yau na zumunci ne amma zamu dawo ayi magana ta gemu da gemu" yace yana dariya.
Baba ya rasa amsar da zai bashi yace bari ya kirawota ta gaishe shi sai ta yiwa Inna magana ta fito.
Cike da ladabi tazo ta gaishe shi sannan su Ade suka rako Inna yayin da ta koma ciki.
*****
Kwanakin da suka gabata Dahiru ya yisu cikin neman amincewar Mawadda a bangaren su Baffa shima sau biyu yana kiran Baba akan zancen. Iyayensa biyu da zaiyi shawara dasu duka suna gidan ya tara matansa a gabansu yace ga yadda suka yi da Mal Isiyaku.
"Anya baka ganin wannan wata dama ce Allah Ya bamu domin samarwa Mawadda farinciki?" Cewar Innarsa.
Iya tace "kuma ina tsammanin mun daukaki abin nan da girma sosai muma mun bada gudunmawa wurin dakushe mata tunanin aure. Mace take gama yawon bariki ma tayi aure balle wadda aka yiwa fin karfi? Mutanen nan ba mune muke binsu ba kazalika babu abinda basu sani ba su da dansu suka kawo kansu saboda haka ni dai tawa shawarar shine a basu dama"
Har kasan zuciyar Ade godiya take ga Allah da Iyanta ta kawo wannan shawara. Tana son Mawadda tayi aure kuma bata ga wanda ya dace da ita ba sama da Dahiru.
Yaya ma dari bisa dari ta goyi bayan shawarar Iya
"mu gwada Malam kada nan gaba muzo muna dana sani. Yarinyar nan tayi kokari kuma tana kan yi wurin nuna maka komai ya wuce kuma ta amince da hukuncinka gareta. Sai dai wallahi tana da rauni sosai. Sai dare yayi kaji tana kuka ita kadai gari ya waye ta shiga aiki kamar babu komai a ranta."
Ade Baba ya kalla yana jiran jin ta bakinta sai tayi murmushi kawai sannan tace duk shawarar da aka tsayar tayi mata.
*****
Mal Isiyaku ya nemi 'yan uwansa akan maganar tunda dole dasu za'a nemi aure babu wanda ya goyi bayansa. Daga me cewa tun farkon karuwanci tayi sai masu cewa yanzu ma da jikinta take ciyar da iyayenta. Rigingimu dai daban daban Inna har ta soma tunanin ko su fada masa ya hakura kawai. Don abin yafi zafi daga bangaren 'yan uwan da suka so ya auri 'ya'yansu bayan sun fara masa kallon Alhaji.
*****
"Alhaji kasa baki mana" Haj Mara tace cikin bacin rai. Gani take ita kadai ce ta damu da rayuwar danta. Yanzu ma maganar zuwa Kano tayi masa yace ba inda zashi.
Kallon BB yayi wanda yake tsaye a gefen dinning table yaki ma yazo gabansu.
"Babawo wannan karon na goyi bayan mamanka. Ka shirya ranar Juma'a kaje ku gaisa mu kuma zamuyi abinda ya dace game da sa rana da sauran shirye shirye"
Kankance idanu yayi "Alhaji zanyi aure fa ku dena damuwa. Akwai information da nake jira akan yarinyar ku zan fara sanarwa idan magana ta kankama"
"Babawo wallahi zanci mutumcinka akan maganar Qareeba. Kai wane irin yaro ne mara jin magana? Dole ne sai yadda kake so za'ayi?" Ta taso tayi kansa kamar ta mare shi sai ta kasa. Yanzu fa makotansu ma kowa zancen BB yake ana cewa yaje turai ya zama dan iska. Kitson kansa yafi komai kona mata rai.
"Wai da marina zakiyi. Hahahahhh abin dariya"
Hanyar dakinsa yayi ta dafe kirjinta da hannu daya ta rike kujera.
Alh Sule ya taso yazo gabanta "Marakisiyya duk wanda yace gyara kayanka ba yana nufin sauke mu raba bane. Ni da dana kika koya masa yaki jin maganata wai bana sonsa. Ki duba ki gani yadda yake neman haddasa miki ciwon zuciya. Yarinyar nan da ya taba nema ki fada min garinsu idan da rabo sai mu nema masa ita ko zai kintsu"
"Allah Ya kiyaye wallahi. Ni na hada zuri'a da masu aiki makiyana su sami abin fada. Idan wadancan 'ya'yan so dinne ai bazaka taba fadin haka ba." Cike da takaici ta buga tsaki ta bar wurin.
Alh Sule ya dade a tsaye shima nasa ran a bace. Haj Mara ta lalata Babawo da soyayyar da take ikirari ta kai shi matakin da addu'a kawai ta rage masa.
*****
Dahiru duk ya matsu yaji amsawar Baba saboda ya ma dena zuwa gidan yana jiran amincewarsa. Da ya sake tuntubar Baffa da zancen ce masa yayi dole su bi a sannu domin ko waye zaiji tsoron saurin sake amincewa a koma 'yar gidan jiya.
Ana haka ne bayan duka su Inna sun amince Baba da kansa ya kira Baffa ya sanar dashi cewa ya baiwa Dahiru Mawadda. Baffa yayi murna sosai da godiya yace in Allah Ya yarda babu zancen bata lokaci da wuri zasu zo a daidaita magana. Suna gamawa ya kira Dahiru ya sanar dashi.
Mawadda bata san me ake ciki ba tana fama da gyaran wata mai jego tayi arbain za ta koma gidan mijinta. Aikin nasu har magariba don na kwana uku suka yi washegari zata koma. Almajiri ne ya shigo daga soron Mawadda tana ce masa ya dakata daga waje za'a karbi kwanonsa.
Yace mata "Ba bara nazo ba sallama ake da wata wai Mawadda"
Iya ta sa dariya dan karami dashi ya iya rashin kunya. Kodayake ba laifinsa bane. Iyaye sun sake shi da malamin da aka bawa amanarsa.
"Jeka kace waye yake sallama da ita" inji Yaya.
"Yaya ko wanka banyi ba ki ko waye ya tafi kawai bari na gyara tsakar gidan"
Yaro ya koma waje abinsa ya tsaya gaban Dahiru kerere.
"To tace ko waye ya tafi bata yi wanka ba kuma zata gyara tsakar gida"
Rike baki yayi yana kallon yaron shima. Ya kira wayarta yafi sau goma bata dauka ba lokacin tana aiki. Shi kuma murnar bashi ita da akayi tasa bazai iya hakuri ba. Sunfi sati uku basu hadu ba.
"Koma kace mata Dahiru ne" ya sake tura yaron ba don yaso ba.
Yaro ya koma ya isar da sako. Mamaki tayi don rabonsa da gidan tun zuwansu da su Baffa. Inna ce tace tayi sauri taje su gaisa karshenta ya sami labarin bashi ita da akayi ne.
Tsintsiyar hannunta ce ta fadi ta tsaya tana kallon Inna.
Yaya tayi murmushi ko ba'a fada ba banda mamaki akwai farinciki bayyane a fuskarta "jeki ki kimtsa da sauri kin bar shi a waje"
Daki ta shiga ta dauko wayarta. Missed calls rututu biyu daga amarya Rafi'a sauran kuwa duka na Dahiru ne. Allah ne Ya kawo Saifullahi shima yazo gida aka sa shi shiga da Dahiru ciki ya zauna jiranta.
Cikin minti ashiri tayi wanka da shiryawa duk cikin sauri. A kunyace ta wuce su Ade taje ta same shi.
Maimakon ta ga gajiyawa da fushin zaman jira a tattare dashi da ta shiga sai ta ga yana ta mata murmushi.
Langabe kai tayi "Yayanmu kayi hakuri aiki nake wayar tana daki"
Shima ya langabe nashi "kinji nayi korafi?"
"A'a"
"To zauna mu gaisa matata Mawaddatan wa Rahma"
Ja da baya tayi tana sunne kai.
"Kunya?"
Ta gyada kai a karo na farko kuma tana zama a kujerar da tafi kusa da kofa. Yaji dadi sosai da yaga wannan chanji a tare da ita.
Gani yayi tana ta boye fuska cikin mayafi shima ya cire hularsa ya dora akan fuskarsa yace "nima fa kunyar nan nake ji"
"Sai kace mace?"
"Ba mace bane amma na macen ne." Ya bata amsa yana kallonta.
Ya sake cewa "ko ba haka bane? An bani ke an baki ni"
Murmushin nan ne dai a fuskarta mai shiga ransa tace "Ni fa yanzun nan na sani"
"Are you happy?"
"Kai Yayanmu...." ji tayi kamar ta tashi ta gudu.
"Allah sai kin amsa min"
Duk yadda taso zillewa kin yarda yayi dole ta amsa masa ta hanyar daga kanta.
"Na fiki farinciki amma bazaki san haka ba sai nan gaba kadan. Kinga ma dai ki fara shiri bikin nan ba zai dade ba"
"Da sauri haka?"
Yayi dariya "nima irin abin nan zaki min ince ba kya doki? Duk kukan da ki ka gama yi da rashin bacci an fada miki ban sani bane zaki wayance"
Kallonsa tayi da mamaki sosai tace da karamar murya "Yayanmu ka fara bani tsoro fa. Waye ya fada maka?"
Dahiru ya rinka dariya "assha Mawadda ashe ba zan sha wuyar yi miki wayo ba"
Cije lebenta tayi tana cewa sai ta rama abin da ya kula sararta ne shi kuma yake matukar bashi sha'awa game da ita. Dena kallonta yayi ba shiri.
"Alkawarinmu yana nan har yanzu?"
"Wanne? Ni ban san wani alkawari ba"
"Ni na sani ai kuma dakin nan ma shaida ne. Da bakinki ki ka ce idan na sami mata zaki yi mata gyaran jiki kyauta. To don Allah ina so ki fara da wuri kiyi irin wanda baki taba yiwa kowa ba"
Cewa tayi bata yarda ba wannan wayo ne yace shi kuma sai ta cika alkawarin. Haka suka yi ta hira cikin nishadi da farinciki.
Cikin lokaci kankani sun sake shakuwa ga wata soyayya da suke yiwa juna mai karfi. Anzo neman aure wanda harda Baba Prof a ciki. Dama tun kafin su zo ya sanar da Baffa gara a hada lokaci daya da na Attahir. Baffa yace bai sani ba ko zasu amince tunda baifi wata biyu ba ya rage.
Sunyi sa'a Baba yace shima baya son a ja lokacin saboda haka sun amince.
Dahiru ya dage shiri komai tare da Attahir suke yi. Wata rana ya dawo daga wurin aiki Baba Prof ya kira shi. Yana zuwa ya tarar da Attahir. Nan ya zube musu mukullai biyu yace suje wani gida ne a rijiyar zaki sama da kasa iri daya sababbi. Kowa ya gwada inda mukullinka ya bude nan ne naka. Gudunmawarsa kenan ya biya musu kudin haya na shekara.
Dariya yayi
"Kada ka daureni Mal Isiyaku. Ai shi ya gani da idanunsa yarinyar nan har yanzu fa bata gama dawowa daidai ba. Abu kadan yake zaburar da ita ta firgita. Karin nauyi kawai zamu bashi idan aka aura masa ita"
"Sauki na Allah ne. Ni dai zuwan yau na zumunci ne amma zamu dawo ayi magana ta gemu da gemu" yace yana dariya.
Baba ya rasa amsar da zai bashi yace bari ya kirawota ta gaishe shi sai ta yiwa Inna magana ta fito.
Cike da ladabi tazo ta gaishe shi sannan su Ade suka rako Inna yayin da ta koma ciki.
*****
Kwanakin da suka gabata Dahiru ya yisu cikin neman amincewar Mawadda a bangaren su Baffa shima sau biyu yana kiran Baba akan zancen. Iyayensa biyu da zaiyi shawara dasu duka suna gidan ya tara matansa a gabansu yace ga yadda suka yi da Mal Isiyaku.
"Anya baka ganin wannan wata dama ce Allah Ya bamu domin samarwa Mawadda farinciki?" Cewar Innarsa.
Iya tace "kuma ina tsammanin mun daukaki abin nan da girma sosai muma mun bada gudunmawa wurin dakushe mata tunanin aure. Mace take gama yawon bariki ma tayi aure balle wadda aka yiwa fin karfi? Mutanen nan ba mune muke binsu ba kazalika babu abinda basu sani ba su da dansu suka kawo kansu saboda haka ni dai tawa shawarar shine a basu dama"
Har kasan zuciyar Ade godiya take ga Allah da Iyanta ta kawo wannan shawara. Tana son Mawadda tayi aure kuma bata ga wanda ya dace da ita ba sama da Dahiru.
Yaya ma dari bisa dari ta goyi bayan shawarar Iya
"mu gwada Malam kada nan gaba muzo muna dana sani. Yarinyar nan tayi kokari kuma tana kan yi wurin nuna maka komai ya wuce kuma ta amince da hukuncinka gareta. Sai dai wallahi tana da rauni sosai. Sai dare yayi kaji tana kuka ita kadai gari ya waye ta shiga aiki kamar babu komai a ranta."
Ade Baba ya kalla yana jiran jin ta bakinta sai tayi murmushi kawai sannan tace duk shawarar da aka tsayar tayi mata.
*****
Mal Isiyaku ya nemi 'yan uwansa akan maganar tunda dole dasu za'a nemi aure babu wanda ya goyi bayansa. Daga me cewa tun farkon karuwanci tayi sai masu cewa yanzu ma da jikinta take ciyar da iyayenta. Rigingimu dai daban daban Inna har ta soma tunanin ko su fada masa ya hakura kawai. Don abin yafi zafi daga bangaren 'yan uwan da suka so ya auri 'ya'yansu bayan sun fara masa kallon Alhaji.
*****
"Alhaji kasa baki mana" Haj Mara tace cikin bacin rai. Gani take ita kadai ce ta damu da rayuwar danta. Yanzu ma maganar zuwa Kano tayi masa yace ba inda zashi.
Kallon BB yayi wanda yake tsaye a gefen dinning table yaki ma yazo gabansu.
"Babawo wannan karon na goyi bayan mamanka. Ka shirya ranar Juma'a kaje ku gaisa mu kuma zamuyi abinda ya dace game da sa rana da sauran shirye shirye"
Kankance idanu yayi "Alhaji zanyi aure fa ku dena damuwa. Akwai information da nake jira akan yarinyar ku zan fara sanarwa idan magana ta kankama"
"Babawo wallahi zanci mutumcinka akan maganar Qareeba. Kai wane irin yaro ne mara jin magana? Dole ne sai yadda kake so za'ayi?" Ta taso tayi kansa kamar ta mare shi sai ta kasa. Yanzu fa makotansu ma kowa zancen BB yake ana cewa yaje turai ya zama dan iska. Kitson kansa yafi komai kona mata rai.
"Wai da marina zakiyi. Hahahahhh abin dariya"
Hanyar dakinsa yayi ta dafe kirjinta da hannu daya ta rike kujera.
Alh Sule ya taso yazo gabanta "Marakisiyya duk wanda yace gyara kayanka ba yana nufin sauke mu raba bane. Ni da dana kika koya masa yaki jin maganata wai bana sonsa. Ki duba ki gani yadda yake neman haddasa miki ciwon zuciya. Yarinyar nan da ya taba nema ki fada min garinsu idan da rabo sai mu nema masa ita ko zai kintsu"
"Allah Ya kiyaye wallahi. Ni na hada zuri'a da masu aiki makiyana su sami abin fada. Idan wadancan 'ya'yan so dinne ai bazaka taba fadin haka ba." Cike da takaici ta buga tsaki ta bar wurin.
Alh Sule ya dade a tsaye shima nasa ran a bace. Haj Mara ta lalata Babawo da soyayyar da take ikirari ta kai shi matakin da addu'a kawai ta rage masa.
*****
Dahiru duk ya matsu yaji amsawar Baba saboda ya ma dena zuwa gidan yana jiran amincewarsa. Da ya sake tuntubar Baffa da zancen ce masa yayi dole su bi a sannu domin ko waye zaiji tsoron saurin sake amincewa a koma 'yar gidan jiya.
Ana haka ne bayan duka su Inna sun amince Baba da kansa ya kira Baffa ya sanar dashi cewa ya baiwa Dahiru Mawadda. Baffa yayi murna sosai da godiya yace in Allah Ya yarda babu zancen bata lokaci da wuri zasu zo a daidaita magana. Suna gamawa ya kira Dahiru ya sanar dashi.
Mawadda bata san me ake ciki ba tana fama da gyaran wata mai jego tayi arbain za ta koma gidan mijinta. Aikin nasu har magariba don na kwana uku suka yi washegari zata koma. Almajiri ne ya shigo daga soron Mawadda tana ce masa ya dakata daga waje za'a karbi kwanonsa.
Yace mata "Ba bara nazo ba sallama ake da wata wai Mawadda"
Iya ta sa dariya dan karami dashi ya iya rashin kunya. Kodayake ba laifinsa bane. Iyaye sun sake shi da malamin da aka bawa amanarsa.
"Jeka kace waye yake sallama da ita" inji Yaya.
"Yaya ko wanka banyi ba ki ko waye ya tafi kawai bari na gyara tsakar gidan"
Yaro ya koma waje abinsa ya tsaya gaban Dahiru kerere.
"To tace ko waye ya tafi bata yi wanka ba kuma zata gyara tsakar gida"
Rike baki yayi yana kallon yaron shima. Ya kira wayarta yafi sau goma bata dauka ba lokacin tana aiki. Shi kuma murnar bashi ita da akayi tasa bazai iya hakuri ba. Sunfi sati uku basu hadu ba.
"Koma kace mata Dahiru ne" ya sake tura yaron ba don yaso ba.
Yaro ya koma ya isar da sako. Mamaki tayi don rabonsa da gidan tun zuwansu da su Baffa. Inna ce tace tayi sauri taje su gaisa karshenta ya sami labarin bashi ita da akayi ne.
Tsintsiyar hannunta ce ta fadi ta tsaya tana kallon Inna.
Yaya tayi murmushi ko ba'a fada ba banda mamaki akwai farinciki bayyane a fuskarta "jeki ki kimtsa da sauri kin bar shi a waje"
Daki ta shiga ta dauko wayarta. Missed calls rututu biyu daga amarya Rafi'a sauran kuwa duka na Dahiru ne. Allah ne Ya kawo Saifullahi shima yazo gida aka sa shi shiga da Dahiru ciki ya zauna jiranta.
Cikin minti ashiri tayi wanka da shiryawa duk cikin sauri. A kunyace ta wuce su Ade taje ta same shi.
Maimakon ta ga gajiyawa da fushin zaman jira a tattare dashi da ta shiga sai ta ga yana ta mata murmushi.
Langabe kai tayi "Yayanmu kayi hakuri aiki nake wayar tana daki"
Shima ya langabe nashi "kinji nayi korafi?"
"A'a"
"To zauna mu gaisa matata Mawaddatan wa Rahma"
Ja da baya tayi tana sunne kai.
"Kunya?"
Ta gyada kai a karo na farko kuma tana zama a kujerar da tafi kusa da kofa. Yaji dadi sosai da yaga wannan chanji a tare da ita.
Gani yayi tana ta boye fuska cikin mayafi shima ya cire hularsa ya dora akan fuskarsa yace "nima fa kunyar nan nake ji"
"Sai kace mace?"
"Ba mace bane amma na macen ne." Ya bata amsa yana kallonta.
Ya sake cewa "ko ba haka bane? An bani ke an baki ni"
Murmushin nan ne dai a fuskarta mai shiga ransa tace "Ni fa yanzun nan na sani"
"Are you happy?"
"Kai Yayanmu...." ji tayi kamar ta tashi ta gudu.
"Allah sai kin amsa min"
Duk yadda taso zillewa kin yarda yayi dole ta amsa masa ta hanyar daga kanta.
"Na fiki farinciki amma bazaki san haka ba sai nan gaba kadan. Kinga ma dai ki fara shiri bikin nan ba zai dade ba"
"Da sauri haka?"
Yayi dariya "nima irin abin nan zaki min ince ba kya doki? Duk kukan da ki ka gama yi da rashin bacci an fada miki ban sani bane zaki wayance"
Kallonsa tayi da mamaki sosai tace da karamar murya "Yayanmu ka fara bani tsoro fa. Waye ya fada maka?"
Dahiru ya rinka dariya "assha Mawadda ashe ba zan sha wuyar yi miki wayo ba"
Cije lebenta tayi tana cewa sai ta rama abin da ya kula sararta ne shi kuma yake matukar bashi sha'awa game da ita. Dena kallonta yayi ba shiri.
"Alkawarinmu yana nan har yanzu?"
"Wanne? Ni ban san wani alkawari ba"
"Ni na sani ai kuma dakin nan ma shaida ne. Da bakinki ki ka ce idan na sami mata zaki yi mata gyaran jiki kyauta. To don Allah ina so ki fara da wuri kiyi irin wanda baki taba yiwa kowa ba"
Cewa tayi bata yarda ba wannan wayo ne yace shi kuma sai ta cika alkawarin. Haka suka yi ta hira cikin nishadi da farinciki.
Cikin lokaci kankani sun sake shakuwa ga wata soyayya da suke yiwa juna mai karfi. Anzo neman aure wanda harda Baba Prof a ciki. Dama tun kafin su zo ya sanar da Baffa gara a hada lokaci daya da na Attahir. Baffa yace bai sani ba ko zasu amince tunda baifi wata biyu ba ya rage.
Sunyi sa'a Baba yace shima baya son a ja lokacin saboda haka sun amince.
Dahiru ya dage shiri komai tare da Attahir suke yi. Wata rana ya dawo daga wurin aiki Baba Prof ya kira shi. Yana zuwa ya tarar da Attahir. Nan ya zube musu mukullai biyu yace suje wani gida ne a rijiyar zaki sama da kasa iri daya sababbi. Kowa ya gwada inda mukullinka ya bude nan ne naka. Gudunmawarsa kenan ya biya musu kudin haya na shekara.