← Book details Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 68

Sashe 43

Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Rasa bakin magana Dahiru yayi tamkar yasa kuka haka yake ji. Me zaice da wadannan bayin Allah? Shiyasa shima ya dauki nauyin wani yaro dan garinsu yanzu yana aji hudu a Dawakin kudu. Ya ga amfanin kyauyayawa sosai ji inda rayuwa ta maida shi matsayin da bai taba zato ba.

Sunje gidan banda wani daki kamar na maigadi sai borehole da wurin parking na kusan motoci hudu sannan gidan. Dahiru ne a sama Attahir a kasa.

A gidan Mal Fatihu ma shiri suke yi sosai. Ade tayi tarin kudi da sa ran Allah zai kawowa Mawadda mijin aure. To gashi lokaci yayi. Itama Mawadda nata kudin sana'ar da take ta tari ta fitar. Baba ya kawo abinda yake dashi Yaya ma tayi rawar gani. Kawunnai da Gwaggoni babu wanda aka bari a baya. Yayyenta su Bilki kowa da tata bajintar. Ashe kowa jiran lokaci yake Mawadda ta sami miji gashi kuwa an samu. Kudin suka dunkule aka saya mata gado mai kyau da kujeru. Duk da gidan dakuna biyu ne da falo karamin dakin kafet da kayan turaren wuta za'a saka.
*****

Su Dr Tani suma shirye shirye suke yi baji ba gani. Sun kashe kudi ba kadan ba wurin kayan dakin Qareeba. Biki tsiransu sati biyu dana Dahiru.

Qareeba ce kadai a gida BB ya kirata yace zai zo suyi sallama kafin ya wuce Kaduna. Har yanzu idan an bata zabi Dahiru take so amma ba yadda ta iya dole ta karbi BB tunda tana son auren.

"To My Man sai ka iso" tace ta tashi ta shirya.

Da yazo shigarsa ta kamala yayi yasa manyan kaya harda hula. Kamar bashi ba don tun kafin zuwan farko yayi aski. Wani munafukin murmushi yake dauke dashi a fuskarsa sakamakon gidansu Mawadda da Garwashi yace masa ya samo. Yau dinnan zai yakice Qareeba ya huta itama kuma Haj Mara dolenta ta barshi ya auri wadda yake so ko ya debo abin kunya.

Falon saukar baki suka zauna yana ji mai aikinsu tace zata je kitso Qareeba tace sai ta dawo ya wani murmusa dama ta samu. Hira ya rinka janta dashi can yace

"My dear muje ki nuna min dakinki mana"

Qareeba ta yi masa wani irin kallo kafin tace "dakina fa kace Man"

Tasowa yayi ya dawo kujerar da take mai cin mutum daya ya zauna akan hannun ya sakalo hannunsa akan kafadarta. A hankali ya sauko da kansa yana shakar kamshin turarenta ta tashi da sauri ta chanja kujera.

Gabanta yazo ya durkusa ya kama mata hannuwa "kinsan ina sonki ko?"

Hadiyar yawu tayi da kyar tsoro ya fara kamata "uhmm"

"Kuma nasan kin matsu ayi aurenmu " yace da murmushi.

Itama murmushin ta kakalo "eh mana amma please koma ka zauna ka dena tabani an kusa a daura"

"Auren da kike so na kawo miki kyauta Qareeba. Muje ki nuna min dakinki ni kuma na nuna miki soyayya irin wadda ta dace dake"

Zuwa yanzu banda tsoro harda bacin rai. Ta yarda bazata karyata ba tana son aure amma ita ba mutuniyar banza bace.

"Man bana son irin wannan wasan idan ma kana min kallon wadda bata da kamun kai ne to ka dena don ban taba zubar da mutumcina ba"

Tafi yayi ya tashi tsaye "da kyau ashe dai dolancin naki wuri yake samu"

Maganarsa tayi mata zafi ta tashi zata bar wurin kawai ya kamo wuyanta yana kokarin sumbatarta ta karfin tsiya. Ture shi tayi tana cewa ita ba 'yar iska bace.

Wani wawan mari ya kai mata a take bakinta ya fashe "nine dan iskan kenan. Yarinya kinyi gaskiya kuma yau zan nuna miki waye BB"

Qareeba na jin haka ta fara ja da baya ya biyota. Kuka ta saka tana kiran Mummy. BB ya samu ya fizgota tana kokarin gudu ta fada kan centre table jug da kofunan suka fashe wasu suka suketa.

Jinin da take zubarwa bai sa BB ya kyaleta ba ya dagata akan kafadarsa ya hau sama. Dakin farko na Dr Tani ya shiga ya jefata akan gado. Hankalinta yayi mugun tashi tana kuka wiwi ta durkusa a gabansa ganin yana cire kaya.

"Kayi hakuri Babawo kada ka cutar dani. Indai aurene na hakura kuma wallahi zan rufa maka asiri ka tafi"

"Hahhhh shegs Qareeba ashe kinsan suna na. Naji kina Man- Man nace bari dai in nuna miki man dinnan yau"

"Na tuba kayi hakuri don Allah" tace tana hada hannuwa.

Belt dinsa ya zare ya shiga zuba mata banda ciwukan da taji a kasa. Tayi kuka har hawaye ya kafe mata sannan yayi kanta.

*****

BB bai dade da zuwa ba Dahiru yazo. Haka kawai yace bari ya kawo musu katin aurensa. Yana wurin Dr Tani ta dawo itama.

Ganinsa da tayi ta wani tabe baki. Bai damu ba ya gaisheta tare da mika mata katin bikin.

Budewa tayi ta karanta sannan ta mika masa abinsa "naga kamu da walima kawai zata yi amaryar taka ni kuma saboda yanayin aikina dinner kawai nake iya zuwa."

Sarai ya gane magana take son fada masa yayi dariya kawai ya jefa su mota ya bude zai shiga ta dawo.

"Kaga motar wanda zai auri Qareeba itama saura 3 weeks. Dan jira na kirawo shi ku gaisa ko"

"Allah Sarki Anti Qareeba ashe lokaci yayi bana zata tashi. Kai na tayaku murna zan jira shi sai ya fito"

Ran Dr Tani yayi baki da maganarsa ta shige fuu yayi dariya kawai.

Falon baki taje ta tarar da kaya baja baja a kasa ga dishi dishin jini. Sama tayi cikin sauri tana kiran Qareeba taji motsi daga dakinta da kukan Qareeban amma kofa a rufe. A guje ta fito ta kirawo Dahiru.

Shi tsoro ma ta bashi amma ya kula ba lafiya don da takalmi daya ta fito ma. Binta yayi da sauri tayi sama tana kiransa da ya taimaka. Suna jiyo kukan Qareeba yayin da BB yake dukanta.

Dahiru baiyi wata wata ba ya kaiwa kofar wani irin duka sai ta bude.

Abinda suka gani ne yasa Dr Tani sumewa shi kuwa Dahiru yayi kan BB kamar zaki ya ga nama.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰18

*Batul Mamman*💖

Haj Mara duniya tayi zafi ta rasa ina BB ya shiga. Ta kira wayarsa har ta gaji.

Bata sanshi da wasu abokai ba yanzu balle ta neme su. 'Ya'yanta mata ta fadawa halin da ake ciki kowacce ta zuke saboda sun gama gajiya da halinsa.

Ta san Dr Tani akan 'ya'yanta da kowa ma fada take balle an taba Qareeba.
*****

Kano kuma Dr Auwal ya debo 'yan sanda ya shigar da kara. Cikin gidansa suka shiga aka dauki hotuna da za'a gabatar shaida. Komai a ilimance don yasan me yake yi shiyasa ko tsinke bai yarda an taba ba. Bayan sauraron bayanan maigadi suka ce suna son ganin wanda ya kaisu asibitin wato Dahiru.

Basu jima da fita ba Dr Auwal ya kira Alh Sule. Yana ofishinsa dake Lagos. Yayi zaton magana zasu yi da ta shafi auren 'ya'yansu sai yaji sabanin haka. Fada Dr Auwal yake yi cikin kunar rai.

"Alh Sule ina Babawo yake?"

"Dakata Dacta meya faru ko gaisawa bamu yi ba"

"Gaisuwa? Gaisuwa ai a gidan mutumci ake yinta. Saboda ku nuna hali an fada muku abinda yaron nan yayi amma daga kai har iyalinka babu wanda yazo yau kwana uku. Wallahi duk inda Babawo yake ku fito dashi domin na riga na hada da 'yan sanda sai munyi shari'a da ku"

Kan Alh Sule ne ya daure ya dai ce masa yayi hakuri sannan ya katse kiran ya nemi Haj Mara.

Tana dauka yace mata "me yake faruwa da Babawo yanzu Dr Auwal ya kirani"

Kuka tasa masa "Na shiga ukuna Alhaji Babawo fyade ya yiwa 'yarsu na rasa yadda zanyi bansan inda yake ba shi kansa"

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Marakisiyya kin kasheni" ya harzuka matuka ya fita da kansa ya kira drebansa. Ko gida bai koma ba ya wuce airport. Jiran awa biyu yayi kafin ya sami jirgi zuwa Kaduna.

Kai kawo Haj Mara take yi ya shigo rai a bace.

Tasowa tayi tana ganinsa "Alhaji."

"Marakisiyya kinga abinda nake gudu ko? Banda lalacewa yarinyar da zai aura nan da 'yan kwanaki ace yayi mata fyade. Wannan wane irin bala'i ne."

"Alhaji ba ta wannan nake ba yanzu shi kanshi bansan inda yake ba. Na kira wayarsa kullum a kashe."

Cikin takaici ya rike kafadunta yana jijjigata "ina tsammanin Babawo mahaukaci ne kuma a jikinki ya tsotso haukan. Ya za'ayi ina fada miki yayiwa yarinya fyade kice ba"a ganshi ba shi allura ne? 'Yar mutane tana gadon asibiti kin kasa fada min gashi har iyayenta sun shigar da kara"

"Kara??? Na bani na lalace Babawo wace irin rayuwa ka zabarwa kanka" tace tana zama dabas akan kujera.

Alh Sule yace "irin wadda ki ka zabar masa mana. Da ace kin bari mun gyara waccan barakar da abubuwa sunyi mana sauki tunda da bakinsa yace yana son yarinyar zai gyara barnar da yayi"

Hararar Alh Sule tayi rai a bace "kai babu dama ayi zancen Babawo sai ka sako wannan yarinyar. Mawadda, Mawadda dai kamar autar mata. Ana maganar 'yar mutane kana kiran 'yar aiki kazama 'yar kauye"

Hade bakinsa da ya saki yayi cikin mamaki "wato Qareeba 'yar mutane tunda iyayenta suna da kudi. Waccan yarinya Mawadda kuma ba mutum bace saboda 'yar aiki ce? Gaskiya kina da matsala da ke da duk masu yiwa 'yan aiki kallon bayi. Bawa ma Marakisiyya akwai hakki tsakaninsa da ubangida ballantana wadda tazo neman halak da guminta"

"Maganar yarinyar nan ta riga ta wuce da wanne zanji kuma? Yaro ya bata ga kuma wata a asibiti ka tsaya kana dauko min wani zance mara tushe. Har yau bana nadamar kashe maganar Mawadda domin tayi tsararo rayuwar dana ta gurbace saboda ita"

"Da kyau matar Alh Sule Chanji" yace yana tafa hannuwa "sai dai ina son tuna miki dukiya da duk wani abu da kike tunkaho dashi nawa ne ba na uban kowa ba"

Juyowa tayi jiki a sanyaye "Alhaji zagina ka ke yi ko gori?"

"Duk wanda ki ka dauka a ciki daidai ne. Kinga Malama na baki minti shabiyar ki shirya Kano zamu tafi yanzu"

******
Chapter 43 · 0% Book details