Sashe 27
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idan an zo gyaran jiki tana yi Rafi'a na lalle Jamila na kitso. Mal Fatihu sai son barka don kuwa 'ya'ya matan da bai taba rainawa ba sun zame masa babban arziki. Hatta 'yan uwansu na kauye su Nana suna cin arzikinsu.
Shekaru biyar baya Malam kakansu ya rasu amma bai bar duniya ba sai da ya mayarda auren Ade da Baba. Itama ta dena aikatau yanzu sun hada kai da Yaya awara suke yi fin kwano biyar a rana. Marwanu da Saifullahi sun koma makaranta almajirai ke jigilar fita da awara mai sauce da ta sami karbuwa sosai.
Kanen Mawadda na wurin Ade suma bata barsu ba tana tura musu kudin makaranta. Gabadaya ta sauya ta koma Mawadda cikakkiyar mace mara tsoro wadda burinta daya yanzu a duniya shine tayi ido hudu da Haj Mara da rabin ranta BB.
Innar Fatihu da Iya sun kara tsufa amma duka gida daya suke. Gidan Mal Fatihu na kauye sunyi kakara da Maigari ya karba suka yi masa ciko suna biyansa a hankali yanzu gidan Tunga ya zama nasu.
******
Tun kafin ya fito daga motar yara sun yanyameta suna ta shafawa ana kiran sunansa. Wata leda ya dauko a gefensa cike da kayan kwalama na yara ya bude motar ya fito. Kamshin turarensa da sanyin ne suka biyo bayansa. Rufe motar yayi ya shiga rarraba musu suna karba ana murna.
Daga cikin gida Innarsa tana jinsu ta soma fara'a tasan ya iso. Shima sauri yayi ya shiga gidan wasu matasa biyu suka biyo shi da akwatinsa da wata katuwar jaka.
Inna ta tashi tana tafi farincikinta baya buya "marhabin lale lale da mutanen ya ma sunan kasar...?"
Dahiru yayi 'yar dariya yana durkusawa a gabanta "Inna na sameku lafiya?"
"Lafiya lau Dahiru....oh ni Indo tafiyar wata biyu shine ka sake cika haka duk ka zama wani basamuden kato."
Ai kuwa ta saka shi dariya sosai. Muryarsa ma ta kara zama ta manya baka ce Dahiru saurayin Mawadda bane mai aikin kubewa a gona.
Baffa ne ya shigo suna tsaye Inna tana ta yiwa Dahiru tsiya yace ta barshi ya huta mana.
Bayan Isha suna hira da iyayensa Inna ta soma mitar rashin aurensa.
"Sai dai kaci banza kaci wofi aje iyali ya gagara" cewar Baffa
Bangaren da aka gyara masa da sunan zama da Mawadda ya kurawa ido yana tunani. Inna ma wurin ta kalla wanda Danlami ne daga baya ya ajiye matarsa kafin su koma cikin gari suma.
"To....to an tabo inda yake masa kaikayi ya lula duniyar tunani" Inna tace tana nunawa Baffa yanayinsa.
Tashi yayi bai kara magana ba ya shige dakin da ya sauka zuciyarsa duk babu dadi. Ina Mawadda take? Ina zai kara ganinta? Kuma a wane yanayi.
Bayan tashinsa Baffa yayi ajiyar zuciya. Tsahon shekarun nan basu taba sanar dashi Maigari ne ya basu gida ba saboda haka za'a iya gano inda suka koma. Hana karya lokacin rasuwar Malam ance masa Mal Fatihu yazo jana'izar mahaifinsa amma ko kwana baiyi a kauyen ba. Shi kuma lokacin baya gari sunje Kano daurin auren 'yar Baba Prof ne.
Rayuwar Dahiru ta dade da sauyawa tun bayar hduwarsa da Prof Abdulhadi. Mutumin ya amsa sunansa mutum ta kowace sigar kwatancen halin kwarai. Bayan ya daukarwa kansa biyan kudin makarantar Dahiru yakan taimaka masa da ihsani. Shi kuma Dahirun sai ya mayar da hankali sosai kada ya bashi kunya. Anyi sa'a kuwa sakamakonsa ya rinka kyau yana gama aji biyar ko bautar kasa bai tafi ba Prof ya samar masa tallafi wato scholarship aka tura shi Turkey karo ilimi. Yaje yayi masters dinsa ya gama cikin shekara daya da rabi. Wannan kudi da ya samu dasu ne ya rinka taimakon iyayensa. Gidansu yanzu idan ka dade baka garin sai yayi maka wuyar gamewa. Yayi masa gyara dan gaske don ma Baffa ya dage bazasu bar garin ba.
Bilya shima likkafa taci gaba yana da nasa garejin har 'yar mota ya saya. Danlami kuma sana'ar busasshen kifi yake wanda yake zuwa kudu ya saro kala kala ya kawo. Yana nan da teburinsa har wuri biyu a kasuwar sabon gari. Ummiyo tayi aure harda yara uku. 'Yan uwanta maza sune gatanta don bata rasa komai.
Dawowar Dahiru kasar ke da wuya ya sami aiki a kamfanin Etisalat. Abu ne da ba zato ba tsammani wani abokin karatunsa ya takura masa suka cike form online. Ashe kawunsa wani babba ne a kamfanin sai gasu suna isowa ba jimawa aka basu offer shi yana Kano abokin nasa yana Lagos.
Haka Allah Yake abinSa Ya baka a lokacin da baka zato bare tsammani. Yanzu haka wani aiki aka tura shi Qatar na wata biyu shine ya dawo jiya ya wuto Kano yau.
Da tunani kala kala ya kwana washegari lahadi da yamma yace zai koma saboda baije ofishinsu ya yi reporting ba. Inna dai tunin aure tayi masa da barazanar idan baiyi wasa ba watarana zai dawo ya tarar da mace an auro masa.
Jikinsa duk ba kwari tun jiya ya kasa samun sukuni da tunanin ko zai kuma ganin Mawadda. Shatara ta arziki yayi musu kamar yadda ya saba ya fita.
Da isarsa Kano gidan Baba Prof ya wuce. Dattijon arziki yayi matukar farincikin ganin Dahiru. Shima murnar yake har ya dauke hankalinsa daga damuwa da tunani.
Yana cin abinci suna hira Haj Mama matar Prof ta shigo.
"Tuzuru na daya...kodayake Attahir ya yiwa kansa fada magana tayi nisa yanzu kai kadai ka rage mana"
Prof yayi dariya don zancen da suke kenan ta damu da rashin aurensa. Ta zauna sun taba hira ya bata tata tsarabar tayi ta sa masa albarka. Da ta fita Prof yake masa fadan yaushe rabonsa da gidan Dr Auwal.
Mukulli yasa yana sosa kai hade da murmushi.
Prof yace "irin haka ko ban fada ba kasan ba dadi ko kazo ka wuce gidansu ka shigo nan. Shekaru sun ja ko kuwa riko ka fara ban sani ba" ya kare yana dariyar rigimar da ta hado Dahiru da uwar dakinsa Dr Tani.
Zaman gidan dena yiwa Dahiru dadi yayi tun bayan da Haj Mara ta samu ta yanke alakar dake tsakaninsu ta hanyar tura BB Dubai wai ya karo karatu. Ba kunya ta sharawa Dr Tani karyar babansa ne ya tura shi wai sai kura ta lafa akan case din Mawadda. A take Dr Tani ta nuna su a wurinsu babu komai ana iya auren ma a tura Qareeban. Son 'ya tayi aure yasa bata tunani yadda ya dace.
Qareeba bata da aiki sai koke-koke yayin da iyayen suka biye mata. Abu yayi gaba BB yafi shekara bai dawo ba. Tun suna bibiya har suka hakura. Albashin Dahiru tsabar kyashi yasa ta rage shi ya koma dubu biyar.
Haka yayi ta karatunsa har Prof ya gama cukucukun nema masa scholarship da admission. Sai da komai ya kankama yaje sanar da ita. Yana fada mata zaiyi tafiya bata tsaya taji me zaice ba ta tabe baki.
"An gaji da karyar bokon za'a koma gida kenan! Dama ido na zuba maka wai nan karatu kake kana mai shara da wanki ni ban taba jin ko alfarmar kudin registration ka roka ba. Ga kwadayi yana dawainiya da kai ka shigewa iyalin Prof Abdulhadi tun da suka dawo unguwar nan"
Takaici ya hana Dahiru magana suna haka Attahir ya shigo dama a bakin mota ya sameta. Hannu tasa ta yafito Attahir yazo ya gaisheta.
"Dama sanin hali na mutanenmu na kauye yasa nace kada yaron nan ya cuceku ya fake da mu wallahi iyakarsa shara da kuma wanki da guga. Idan ma wani abin yayi a gidanku kazo nemansa don yanzu haka ma zancen tafiya yake min to ka shaidawa iyayenka tun wuri maiaikinmu ne kawai"
Daga Dahirun har Attahir aka rasa me baki magana. Dama copy din admission letter dinsa Prof ya bayar yace ya bashi ya nuna musu.
Tun daga wannan ranar Dahiru bai sake shiga gidansu ba kuma duk zuwansa ko a hanya bai taba cin karo da wani dan gidan ba. Maigadin da ya sani ya dade da aka canza shi.
Alkawarin zuwa gidan yayi cikin sati a gaisa albarkan shekarun baya. Ya sami labarin duka mazan sunyi aure sai Hajiya Qareeba kadai ta rage. Duk abinda Dr Tani tayi dominta bukata bata biya ba.
Canja hirar yayi yace Prof yazo su ga sabuwar motarsa. Maimakon murna Haj Mama dai fadan aure ta sake dasawa wai bata ga amfanin kwalisa babu matar da za'a burge ba.
*****
Sati biyu kenan da Mawadda ta karbi sakamonta na makarantar yaki da jahilci da tayi. A daya bangaren kuma yau aka fara bikin Rafi'a.
Biki suka shirya daidai karfinsu na burgewa da kamun kai. Jamila ma ta dade da Ja'e ya mayar da ita da izinin babarsa yanzu gidan zai rage Mawadda kawai da 'yan maza.
Danlami sarkin shige shige ne Allah Ya kawowa katin daurin auren har kasuwa inda yake sana'arsa. Sai da ya nanata tambayar wanda ya bashi shima dan garinsu ne ya tabbatar masa da gaske kanwar Mawadda ce. Ranar da wuri ya tashi ya tafi ofishin Dahiru.
"Kai kuma daga ina haka kamar an jeho ka? Mutum da 'ya'ya biyu ya kasa girma"
Katin ya ajiye masa kafin ya mika hannu. Alkawari na yiwa kaina zan nemo maka Mawadda to ga katin auren kanwarta. Abu daya zaka bani ladan aiki shine ka ban mukullin motarka don Allah in zaga garin nan da iyalina muma mu kashe selfie.
Dahiru bai ce komai ba bayan karanta katin sai mukullin da ya jefa masa.
"Gobe da safe kafin na gama shiryawa ka dawo min da ita"
Danlami ya dauka yana ta murna yayi waje. Tabdi yau yasan Azima zata jidadi. Matarsa akwai saukin kai shiyasa yake son burgeta.
Dahiru kuma adaidaita sahu ya nema ya kaishi har layin gidan nasu ya tabbatar ba karya bane. Haka kawai yaji gabansa na faduwa wai cikin taron jama'ar dake waje ko cikin gidan nan Mawaddansa tana ciki.
Komawa yayi gidan da yake haya tare da wasu marasa auren na wurin aikinsu. Ranar yayi bacci mai dadi amma cike da zulumin ko tayi aure.
Washegari a daddafe ya kai karfe shida a office. Gida ya koma ya shirya yayi kyau sosai kamar ba Dahiru mai ahirin ba.
Shekaru biyar baya Malam kakansu ya rasu amma bai bar duniya ba sai da ya mayarda auren Ade da Baba. Itama ta dena aikatau yanzu sun hada kai da Yaya awara suke yi fin kwano biyar a rana. Marwanu da Saifullahi sun koma makaranta almajirai ke jigilar fita da awara mai sauce da ta sami karbuwa sosai.
Kanen Mawadda na wurin Ade suma bata barsu ba tana tura musu kudin makaranta. Gabadaya ta sauya ta koma Mawadda cikakkiyar mace mara tsoro wadda burinta daya yanzu a duniya shine tayi ido hudu da Haj Mara da rabin ranta BB.
Innar Fatihu da Iya sun kara tsufa amma duka gida daya suke. Gidan Mal Fatihu na kauye sunyi kakara da Maigari ya karba suka yi masa ciko suna biyansa a hankali yanzu gidan Tunga ya zama nasu.
******
Tun kafin ya fito daga motar yara sun yanyameta suna ta shafawa ana kiran sunansa. Wata leda ya dauko a gefensa cike da kayan kwalama na yara ya bude motar ya fito. Kamshin turarensa da sanyin ne suka biyo bayansa. Rufe motar yayi ya shiga rarraba musu suna karba ana murna.
Daga cikin gida Innarsa tana jinsu ta soma fara'a tasan ya iso. Shima sauri yayi ya shiga gidan wasu matasa biyu suka biyo shi da akwatinsa da wata katuwar jaka.
Inna ta tashi tana tafi farincikinta baya buya "marhabin lale lale da mutanen ya ma sunan kasar...?"
Dahiru yayi 'yar dariya yana durkusawa a gabanta "Inna na sameku lafiya?"
"Lafiya lau Dahiru....oh ni Indo tafiyar wata biyu shine ka sake cika haka duk ka zama wani basamuden kato."
Ai kuwa ta saka shi dariya sosai. Muryarsa ma ta kara zama ta manya baka ce Dahiru saurayin Mawadda bane mai aikin kubewa a gona.
Baffa ne ya shigo suna tsaye Inna tana ta yiwa Dahiru tsiya yace ta barshi ya huta mana.
Bayan Isha suna hira da iyayensa Inna ta soma mitar rashin aurensa.
"Sai dai kaci banza kaci wofi aje iyali ya gagara" cewar Baffa
Bangaren da aka gyara masa da sunan zama da Mawadda ya kurawa ido yana tunani. Inna ma wurin ta kalla wanda Danlami ne daga baya ya ajiye matarsa kafin su koma cikin gari suma.
"To....to an tabo inda yake masa kaikayi ya lula duniyar tunani" Inna tace tana nunawa Baffa yanayinsa.
Tashi yayi bai kara magana ba ya shige dakin da ya sauka zuciyarsa duk babu dadi. Ina Mawadda take? Ina zai kara ganinta? Kuma a wane yanayi.
Bayan tashinsa Baffa yayi ajiyar zuciya. Tsahon shekarun nan basu taba sanar dashi Maigari ne ya basu gida ba saboda haka za'a iya gano inda suka koma. Hana karya lokacin rasuwar Malam ance masa Mal Fatihu yazo jana'izar mahaifinsa amma ko kwana baiyi a kauyen ba. Shi kuma lokacin baya gari sunje Kano daurin auren 'yar Baba Prof ne.
Rayuwar Dahiru ta dade da sauyawa tun bayar hduwarsa da Prof Abdulhadi. Mutumin ya amsa sunansa mutum ta kowace sigar kwatancen halin kwarai. Bayan ya daukarwa kansa biyan kudin makarantar Dahiru yakan taimaka masa da ihsani. Shi kuma Dahirun sai ya mayar da hankali sosai kada ya bashi kunya. Anyi sa'a kuwa sakamakonsa ya rinka kyau yana gama aji biyar ko bautar kasa bai tafi ba Prof ya samar masa tallafi wato scholarship aka tura shi Turkey karo ilimi. Yaje yayi masters dinsa ya gama cikin shekara daya da rabi. Wannan kudi da ya samu dasu ne ya rinka taimakon iyayensa. Gidansu yanzu idan ka dade baka garin sai yayi maka wuyar gamewa. Yayi masa gyara dan gaske don ma Baffa ya dage bazasu bar garin ba.
Bilya shima likkafa taci gaba yana da nasa garejin har 'yar mota ya saya. Danlami kuma sana'ar busasshen kifi yake wanda yake zuwa kudu ya saro kala kala ya kawo. Yana nan da teburinsa har wuri biyu a kasuwar sabon gari. Ummiyo tayi aure harda yara uku. 'Yan uwanta maza sune gatanta don bata rasa komai.
Dawowar Dahiru kasar ke da wuya ya sami aiki a kamfanin Etisalat. Abu ne da ba zato ba tsammani wani abokin karatunsa ya takura masa suka cike form online. Ashe kawunsa wani babba ne a kamfanin sai gasu suna isowa ba jimawa aka basu offer shi yana Kano abokin nasa yana Lagos.
Haka Allah Yake abinSa Ya baka a lokacin da baka zato bare tsammani. Yanzu haka wani aiki aka tura shi Qatar na wata biyu shine ya dawo jiya ya wuto Kano yau.
Da tunani kala kala ya kwana washegari lahadi da yamma yace zai koma saboda baije ofishinsu ya yi reporting ba. Inna dai tunin aure tayi masa da barazanar idan baiyi wasa ba watarana zai dawo ya tarar da mace an auro masa.
Jikinsa duk ba kwari tun jiya ya kasa samun sukuni da tunanin ko zai kuma ganin Mawadda. Shatara ta arziki yayi musu kamar yadda ya saba ya fita.
Da isarsa Kano gidan Baba Prof ya wuce. Dattijon arziki yayi matukar farincikin ganin Dahiru. Shima murnar yake har ya dauke hankalinsa daga damuwa da tunani.
Yana cin abinci suna hira Haj Mama matar Prof ta shigo.
"Tuzuru na daya...kodayake Attahir ya yiwa kansa fada magana tayi nisa yanzu kai kadai ka rage mana"
Prof yayi dariya don zancen da suke kenan ta damu da rashin aurensa. Ta zauna sun taba hira ya bata tata tsarabar tayi ta sa masa albarka. Da ta fita Prof yake masa fadan yaushe rabonsa da gidan Dr Auwal.
Mukulli yasa yana sosa kai hade da murmushi.
Prof yace "irin haka ko ban fada ba kasan ba dadi ko kazo ka wuce gidansu ka shigo nan. Shekaru sun ja ko kuwa riko ka fara ban sani ba" ya kare yana dariyar rigimar da ta hado Dahiru da uwar dakinsa Dr Tani.
Zaman gidan dena yiwa Dahiru dadi yayi tun bayan da Haj Mara ta samu ta yanke alakar dake tsakaninsu ta hanyar tura BB Dubai wai ya karo karatu. Ba kunya ta sharawa Dr Tani karyar babansa ne ya tura shi wai sai kura ta lafa akan case din Mawadda. A take Dr Tani ta nuna su a wurinsu babu komai ana iya auren ma a tura Qareeban. Son 'ya tayi aure yasa bata tunani yadda ya dace.
Qareeba bata da aiki sai koke-koke yayin da iyayen suka biye mata. Abu yayi gaba BB yafi shekara bai dawo ba. Tun suna bibiya har suka hakura. Albashin Dahiru tsabar kyashi yasa ta rage shi ya koma dubu biyar.
Haka yayi ta karatunsa har Prof ya gama cukucukun nema masa scholarship da admission. Sai da komai ya kankama yaje sanar da ita. Yana fada mata zaiyi tafiya bata tsaya taji me zaice ba ta tabe baki.
"An gaji da karyar bokon za'a koma gida kenan! Dama ido na zuba maka wai nan karatu kake kana mai shara da wanki ni ban taba jin ko alfarmar kudin registration ka roka ba. Ga kwadayi yana dawainiya da kai ka shigewa iyalin Prof Abdulhadi tun da suka dawo unguwar nan"
Takaici ya hana Dahiru magana suna haka Attahir ya shigo dama a bakin mota ya sameta. Hannu tasa ta yafito Attahir yazo ya gaisheta.
"Dama sanin hali na mutanenmu na kauye yasa nace kada yaron nan ya cuceku ya fake da mu wallahi iyakarsa shara da kuma wanki da guga. Idan ma wani abin yayi a gidanku kazo nemansa don yanzu haka ma zancen tafiya yake min to ka shaidawa iyayenka tun wuri maiaikinmu ne kawai"
Daga Dahirun har Attahir aka rasa me baki magana. Dama copy din admission letter dinsa Prof ya bayar yace ya bashi ya nuna musu.
Tun daga wannan ranar Dahiru bai sake shiga gidansu ba kuma duk zuwansa ko a hanya bai taba cin karo da wani dan gidan ba. Maigadin da ya sani ya dade da aka canza shi.
Alkawarin zuwa gidan yayi cikin sati a gaisa albarkan shekarun baya. Ya sami labarin duka mazan sunyi aure sai Hajiya Qareeba kadai ta rage. Duk abinda Dr Tani tayi dominta bukata bata biya ba.
Canja hirar yayi yace Prof yazo su ga sabuwar motarsa. Maimakon murna Haj Mama dai fadan aure ta sake dasawa wai bata ga amfanin kwalisa babu matar da za'a burge ba.
*****
Sati biyu kenan da Mawadda ta karbi sakamonta na makarantar yaki da jahilci da tayi. A daya bangaren kuma yau aka fara bikin Rafi'a.
Biki suka shirya daidai karfinsu na burgewa da kamun kai. Jamila ma ta dade da Ja'e ya mayar da ita da izinin babarsa yanzu gidan zai rage Mawadda kawai da 'yan maza.
Danlami sarkin shige shige ne Allah Ya kawowa katin daurin auren har kasuwa inda yake sana'arsa. Sai da ya nanata tambayar wanda ya bashi shima dan garinsu ne ya tabbatar masa da gaske kanwar Mawadda ce. Ranar da wuri ya tashi ya tafi ofishin Dahiru.
"Kai kuma daga ina haka kamar an jeho ka? Mutum da 'ya'ya biyu ya kasa girma"
Katin ya ajiye masa kafin ya mika hannu. Alkawari na yiwa kaina zan nemo maka Mawadda to ga katin auren kanwarta. Abu daya zaka bani ladan aiki shine ka ban mukullin motarka don Allah in zaga garin nan da iyalina muma mu kashe selfie.
Dahiru bai ce komai ba bayan karanta katin sai mukullin da ya jefa masa.
"Gobe da safe kafin na gama shiryawa ka dawo min da ita"
Danlami ya dauka yana ta murna yayi waje. Tabdi yau yasan Azima zata jidadi. Matarsa akwai saukin kai shiyasa yake son burgeta.
Dahiru kuma adaidaita sahu ya nema ya kaishi har layin gidan nasu ya tabbatar ba karya bane. Haka kawai yaji gabansa na faduwa wai cikin taron jama'ar dake waje ko cikin gidan nan Mawaddansa tana ciki.
Komawa yayi gidan da yake haya tare da wasu marasa auren na wurin aikinsu. Ranar yayi bacci mai dadi amma cike da zulumin ko tayi aure.
Washegari a daddafe ya kai karfe shida a office. Gida ya koma ya shirya yayi kyau sosai kamar ba Dahiru mai ahirin ba.