Sashe 58
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Attahir ya fita shigo dashi. Dahiru kuma yace da Dr Tani yana son magana da ita.
Qareeba na zumbura baki ta tashi ta basu wuri.
Hankalinta a dan tashe tace "lafiya dai ko?
"Akan Anti Qareeba ne"
"Dahiru zaka aureta ne?"
"A'a" yace da sauri.
Jikinta a sanyaye tace to me ya faru.
"Hajiya duk abubuwan rashin jindadin da suka faru tsakaninmu basu sa na dena tausayin Anti Qareeba ba. Ni da ke da mutane da dama kowa yasan tana son tayi aure"
Kwalla ce ta ciko a idanun Dr Tani "wallahi Dahiru ko waye yanzu yazo nemanta idan yana da sana'a zan bashi ko don kallon da ake yi mata na wadda aka yiwa fyade. Yar uwarka bata jin kunyar fada min tana son auren nan kaga idan bata yi ba sai mu sami matsala"
"Ko da dan uwana ne kuma makanike?"
Yawu ta hadiya ta kalli idanun Dahiru wanda suka matukar tsorata ta ranar da yace zai kona mata asibiti.
Bakinta yana rawa a hankali tace "makanike?"
Ya dage gira yana jiran ya gani ko zata fadi magana mara dadi su tattara su bar gidan. Duk halin shirmen Qareeba yana ganinta da wani dan mutumci tun bayan abinda BB yayi mata kuma ba don tozarci yake son hadata da dan uwan da bashi da kamarsa ba. Don ko me ya zama yau Bilya ne mafari.
"Eh makanike mai mace daya da 'ya'ya biyar. Yana da kirki fiye da zatonki kuma mutum ne mai tsananin hakuri....and yes yana da garejin kansa yanzu da mota ba yaron kowa bane"
Ga tsananin mamakinsa hawaye ne suke saukowa hadaddiya kuma rikakkiyar 'yar boko Dr Tani.
"Ko a cikin 'ya'ya Dahiru ka fita daban. Nagode kuma in sha Allahu zan baku mamaki a kotu. A shirye nake na rasa komai don ganin bayan Haj Mara da BB. Allah Yasa tayi masa yayan naka"
Murmushi Dahiru yayi wanda ya karawa fuskarsa kwarjini da kyau.
"Kada ki damu da wannan in sha Allah"
Tare suka koma falon lokacin Attahir ya shigo da Bilya. Kana ganinsa ka ga jinin Dahiru saboda kama da suke yi. Dukkansu suna da tsayi musamman Bilya da Danlami da suka rankwafa kadan. Shiga yayi ta kamala yayi kyau kallo daya zaka gane mutum ne mai sanyin hali.
Tunda suka shigo Qareeba ta kasa dauke ido daga kansa don sai da Dr Tani ta zauna a gefenta ta dan daki gefen kafarta tayi firgigit ta dago.
Sun gaisa da Dr Tani a take ya kwanta mata. To ita wane sauran zabe zata zauna bayan duka isharar da tayi ta gani a kwanakin nan.
Dahiru ne ya fara mikewa "Hajiya zamu je wurin Baba Prof mu dawo sai mu wuce gida"
Qareeba ta dago da sauri "dukkanku Ahirin?"
"Yayanmu Bilya zai jiramu a nan ba jimawa zamuyi ba"
Tayi wani fari da ido "no take your time fa sai na zauna dashi kada a barshi shi daya"
Bilya yana jin haka ya daga ya kalli Dahiru. Anya zai iya da wannan tunda yazo dama ta kafe shi da idanu.
Cikin sanyinsa da ya janyo masa raini a wurin Furera yace "ko dai na biku ne"
Qareeba taji kamar ya mareta daga zuwa sai tafiya "don Allah ka tsaya mu sake gaisawa sai na raka ka gidan. Ba nisa daga nan"
Attahir ya kunshe baki yayi waje Dahiru ya biyo bayansa "ba fa nason iskanci matar Yayana zata zama."
Attahir ya fashe da dariya "solidarity sak dan uwa ai nima yayana ne. Muje mu basu wuri. Amma wallahi kamar tsoronta yake yi. Allah Sarki Yayanmu Bilya"
******
Shiru falon daga Qareeba har Bilya an rasa wanda zai fara magana. Shi bai san ta ina zai fara ba ita kuma nan ta kame ne kada tayi abinda ta saba ake cewa bata da kan gado. Gajiya tayi ta danyi gyaran murya.
"Ehemmmm"
Bilya ya zubo ruwa da sauri ya miko mata "sannu karbi ki sha"
Fari take tana juya idanu kafin ta karba ta dan kurba kadan.
Bilya ya kalli yadda tayi da idanu ya zuba hannuwansa a aljihun riga "me ya sami idanun ko zaki shiga ciki ki wanke?"
Kasa hakuri tayi cikin muryarta ta sangarta tace "wai kai baka taba zuwa wurin mace bane?"
Sai da ya koma ya zauna ya amsa mata "ni da nake da aure da 'ya'ya ma"
"Duk abuna nasan wurina Ahirin ya kawoka ko ba haka ba"
Bilya a ransa yace toohh wannan gaba gadi take sannan ya gyada kai.
"Ina ganin sun fita na gane. Shine kazo babu wani tambayoyi irin wanda ake yiwa mace farkon zuwa kayi shiru abinka."
Murmushi yayi saboda yadda take tuttura baki da gani an saba yi mata yadda take so amma kuma tsoronta yake ji don yadda take magana yasan kila ana jinsu kada azo ace ya yi mata wani abu.
"Yi hakuri gani nayi kamar kinfi karfina shiyasa nayi shiru"
Sunkuyar da kai tayi tana jin kamar kwalla muryarta tana rawa tace "kai dai ka fadi gaskiya ko kaima banyi maka bane? Its ok an saba haka bazan ji haushi ba"
Jikinsa ne yayi mugun sanyi ta bashi tausayi. Mace har mace bai hango wata makusa ba amma Allah bai nufeta da aure ba. Aure babu ruwansa da arziki ko kyau. Idan lokaci yayi ne kawai sai anyi.
"Qareeba ni talaka ne, makanike mai mata da yara kuma dan kauye wanda karatunsa ya tsaya a JSS 3. Ina zan kaiki?"
"Inda ake kai mata"
Hannu biyu tasa ta rufe bakinta bayan maganar ta subutu ta fito ta shige kunnuwansa suka hada ido. Mayafinta da yake a kafada ta dauko ta rufe fuska karo na farko a rayuwarta da taji kunyar wani da namiji.
Wani murmushin ya sake yi "indai zaki iya aurena a haka to wannan talakan yayi alkawarin kaiki inda ake kai matan...dakin aure ne a killace su a basu kulawa"
Tashin hankali mamakin kansa ne ya kama shi. Daga ina yake zaro wadannan zantuka shi kuwa. Qareeba tsabar kunya balle da yace zai aureta ta shiga tattaba wuya ta tabbatar kalau take ba zazzabi bane yasa ta kasa magana.
Yana lura da ita yace "baki da lafiya ne?"
"Ina jin dai ba kalau ba. Kaga na kasa dago kai na kalleka abin mamaki" tace da gaske cikin mamakin.
"Bayan kin gama yi min kirikiri da ido meye baki gama gani ba" ya zolayeta.
Ta sake rufe fuska "ban taba jin haka ba tunda nake akan kowa"
"Me kike ji Qareeba?" Bilya ya sami kansa da tambayarta. Sosai yake jindadin magana da ita.
"Farinciki"
Karamar dariya yayi ta dago da kai "don Allah kada ka samin rai kaima naji shiru. Nasan Ahirin ya fada maka komai a kaina amma wallahi ba'ayi raping dina ba"
Bilya ji yayi ko gobe akace yazo a daura musu aure zai yarda saboda yadda Qareeba ta shiga zuciyarsa musamman saboda tausayi.
"Ki bari nayi zuwa uku sai mu tabbatar da zamu iya zama da juna. Sai dai matsala daya wallahi Dahiru baya son sunan nan Ahirin"
Bude mayafin tayi ta sa dariya "ai wallahi sai dai yayi hakuri sunansa kenan a wurina"
******
Dahiru da Attahir a kafa suka fita tunda ba nisa bane titi kawai zasu tsallaka suyi tafiyar kasa da minti biyar.
Fitowarsu a idon BB da Bobo ya tabbatar Mawadda bata bayansu yace "Bobo dawo nan da sauri"
Chanjin seat suka yi ya tada mota da sauri ya bata wuta. Attahir ya haye dan tudun gefen titi inda zai sada shi da gidansu shi kuma Dahiru yana daga bayansa. Daga kafarsa ke da wuya basu san daga ina ba sai ganinsa suka yi yayi sama saboda wani mugun bugu da BB yayi masa ya dawo ya daki kan bonnet dinta ya fadi kasa ko motsi kwakkwara baya yi.
Attahir mutuwar tsaye yayi har maigadin gidan Dr Auwal da wasu maza suka taho suna kokarin daga Dahiru. Jikinsa gabadaya ji yake kamar an sara masa guduma. Bai tashi gane me yake yi ba sai da suka yi ido da ido da BB Sule Chanji yayin da ya fizgi motar a guje kamar zai tashi sama.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰23
*Batul Mamman*💖
Kwanaki shadaya da auren su Dahiru wanda yayi daidai da kwana goma da tarewar Mawadda. A dan tsukin lokacin nan shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu. Duk abinda Dahiru zaiyi domin ya cire mata tsoro kuma ta saki jiki dashi yana yi. Shiyasa bata da wata damuwa sai ta kokarin kyautata masa.
Zamansu gwanin sha'awa kana ganinsu kaga masoyan da suka yi nisa cikin soyayyar juna. Tsakaninsu dasu Attahir ma sai son barka. Matan suna matukar kokari su hada kai domin jindadin mazansu. Nawal bata da matsala. Yadda ta rungumi Mawadda babu kyama ko nuna ta fita domin ita a yanzu bautar kasa zata fara sabanin Mawadda da Adult education tayi.
Yau da sassafe matan suka tashi saboda aikin da yake gabansu. Gidan Baba Prof zasu je daga can kuma kowanne zai tafi da matarsa gidan iyayenta. Washegari kuma Dahiru da Mawadda su tafi Tariwa su kwana biyu.
Mawadda ta gama tuwon shinkafa da miyar agushi tun daga falo kamshin miyar sai yasa yawu tsinkewa. A kasa kuma Nawal ta kusa gama suyar samosa da doughnut da zasu hada su kai musu.
Shadaya da rabi ta gama komai harda breakfast ta gyara gida ta koma daki domin tashin Dahiru sannan tayi wanka. Filon da take sawa tsakaninsu dogo shi ta gani a kasa shi kuma yana amsa waya.
Wardrobe ta bude inda ta jera musu kayansu ta tsaya tana karewa kayanta kallo.
Bayan Dahiru ya gama wayar taji yace "Matar Dahiru yau ba gaisuwa?"
"Ina zuwa gaisheka na ga ka jefar min da dan amana a kasa"
Dariya ya soma yi yayi rub da ciki ya rike fuskarsa da hannuwansa.
"Kin jawo masa yau zan jefa shi ta taga ma. Haka kawai kullum yana tsakiyar mata da miji shi ko tsoron daukan alhaki baya yi ma"
Sai da tayi dariya tace "babu wani hakki, tunda hannunka ya warke ko zaka koma kasa? Idan ka sauka da kaina zan jefar da filon"
"Haka ma zaki ce? Kwana kike makale da shi fa ga bawan Allah a gefe" ya nuna kansa yana bata rai.
Qareeba na zumbura baki ta tashi ta basu wuri.
Hankalinta a dan tashe tace "lafiya dai ko?
"Akan Anti Qareeba ne"
"Dahiru zaka aureta ne?"
"A'a" yace da sauri.
Jikinta a sanyaye tace to me ya faru.
"Hajiya duk abubuwan rashin jindadin da suka faru tsakaninmu basu sa na dena tausayin Anti Qareeba ba. Ni da ke da mutane da dama kowa yasan tana son tayi aure"
Kwalla ce ta ciko a idanun Dr Tani "wallahi Dahiru ko waye yanzu yazo nemanta idan yana da sana'a zan bashi ko don kallon da ake yi mata na wadda aka yiwa fyade. Yar uwarka bata jin kunyar fada min tana son auren nan kaga idan bata yi ba sai mu sami matsala"
"Ko da dan uwana ne kuma makanike?"
Yawu ta hadiya ta kalli idanun Dahiru wanda suka matukar tsorata ta ranar da yace zai kona mata asibiti.
Bakinta yana rawa a hankali tace "makanike?"
Ya dage gira yana jiran ya gani ko zata fadi magana mara dadi su tattara su bar gidan. Duk halin shirmen Qareeba yana ganinta da wani dan mutumci tun bayan abinda BB yayi mata kuma ba don tozarci yake son hadata da dan uwan da bashi da kamarsa ba. Don ko me ya zama yau Bilya ne mafari.
"Eh makanike mai mace daya da 'ya'ya biyar. Yana da kirki fiye da zatonki kuma mutum ne mai tsananin hakuri....and yes yana da garejin kansa yanzu da mota ba yaron kowa bane"
Ga tsananin mamakinsa hawaye ne suke saukowa hadaddiya kuma rikakkiyar 'yar boko Dr Tani.
"Ko a cikin 'ya'ya Dahiru ka fita daban. Nagode kuma in sha Allahu zan baku mamaki a kotu. A shirye nake na rasa komai don ganin bayan Haj Mara da BB. Allah Yasa tayi masa yayan naka"
Murmushi Dahiru yayi wanda ya karawa fuskarsa kwarjini da kyau.
"Kada ki damu da wannan in sha Allah"
Tare suka koma falon lokacin Attahir ya shigo da Bilya. Kana ganinsa ka ga jinin Dahiru saboda kama da suke yi. Dukkansu suna da tsayi musamman Bilya da Danlami da suka rankwafa kadan. Shiga yayi ta kamala yayi kyau kallo daya zaka gane mutum ne mai sanyin hali.
Tunda suka shigo Qareeba ta kasa dauke ido daga kansa don sai da Dr Tani ta zauna a gefenta ta dan daki gefen kafarta tayi firgigit ta dago.
Sun gaisa da Dr Tani a take ya kwanta mata. To ita wane sauran zabe zata zauna bayan duka isharar da tayi ta gani a kwanakin nan.
Dahiru ne ya fara mikewa "Hajiya zamu je wurin Baba Prof mu dawo sai mu wuce gida"
Qareeba ta dago da sauri "dukkanku Ahirin?"
"Yayanmu Bilya zai jiramu a nan ba jimawa zamuyi ba"
Tayi wani fari da ido "no take your time fa sai na zauna dashi kada a barshi shi daya"
Bilya yana jin haka ya daga ya kalli Dahiru. Anya zai iya da wannan tunda yazo dama ta kafe shi da idanu.
Cikin sanyinsa da ya janyo masa raini a wurin Furera yace "ko dai na biku ne"
Qareeba taji kamar ya mareta daga zuwa sai tafiya "don Allah ka tsaya mu sake gaisawa sai na raka ka gidan. Ba nisa daga nan"
Attahir ya kunshe baki yayi waje Dahiru ya biyo bayansa "ba fa nason iskanci matar Yayana zata zama."
Attahir ya fashe da dariya "solidarity sak dan uwa ai nima yayana ne. Muje mu basu wuri. Amma wallahi kamar tsoronta yake yi. Allah Sarki Yayanmu Bilya"
******
Shiru falon daga Qareeba har Bilya an rasa wanda zai fara magana. Shi bai san ta ina zai fara ba ita kuma nan ta kame ne kada tayi abinda ta saba ake cewa bata da kan gado. Gajiya tayi ta danyi gyaran murya.
"Ehemmmm"
Bilya ya zubo ruwa da sauri ya miko mata "sannu karbi ki sha"
Fari take tana juya idanu kafin ta karba ta dan kurba kadan.
Bilya ya kalli yadda tayi da idanu ya zuba hannuwansa a aljihun riga "me ya sami idanun ko zaki shiga ciki ki wanke?"
Kasa hakuri tayi cikin muryarta ta sangarta tace "wai kai baka taba zuwa wurin mace bane?"
Sai da ya koma ya zauna ya amsa mata "ni da nake da aure da 'ya'ya ma"
"Duk abuna nasan wurina Ahirin ya kawoka ko ba haka ba"
Bilya a ransa yace toohh wannan gaba gadi take sannan ya gyada kai.
"Ina ganin sun fita na gane. Shine kazo babu wani tambayoyi irin wanda ake yiwa mace farkon zuwa kayi shiru abinka."
Murmushi yayi saboda yadda take tuttura baki da gani an saba yi mata yadda take so amma kuma tsoronta yake ji don yadda take magana yasan kila ana jinsu kada azo ace ya yi mata wani abu.
"Yi hakuri gani nayi kamar kinfi karfina shiyasa nayi shiru"
Sunkuyar da kai tayi tana jin kamar kwalla muryarta tana rawa tace "kai dai ka fadi gaskiya ko kaima banyi maka bane? Its ok an saba haka bazan ji haushi ba"
Jikinsa ne yayi mugun sanyi ta bashi tausayi. Mace har mace bai hango wata makusa ba amma Allah bai nufeta da aure ba. Aure babu ruwansa da arziki ko kyau. Idan lokaci yayi ne kawai sai anyi.
"Qareeba ni talaka ne, makanike mai mata da yara kuma dan kauye wanda karatunsa ya tsaya a JSS 3. Ina zan kaiki?"
"Inda ake kai mata"
Hannu biyu tasa ta rufe bakinta bayan maganar ta subutu ta fito ta shige kunnuwansa suka hada ido. Mayafinta da yake a kafada ta dauko ta rufe fuska karo na farko a rayuwarta da taji kunyar wani da namiji.
Wani murmushin ya sake yi "indai zaki iya aurena a haka to wannan talakan yayi alkawarin kaiki inda ake kai matan...dakin aure ne a killace su a basu kulawa"
Tashin hankali mamakin kansa ne ya kama shi. Daga ina yake zaro wadannan zantuka shi kuwa. Qareeba tsabar kunya balle da yace zai aureta ta shiga tattaba wuya ta tabbatar kalau take ba zazzabi bane yasa ta kasa magana.
Yana lura da ita yace "baki da lafiya ne?"
"Ina jin dai ba kalau ba. Kaga na kasa dago kai na kalleka abin mamaki" tace da gaske cikin mamakin.
"Bayan kin gama yi min kirikiri da ido meye baki gama gani ba" ya zolayeta.
Ta sake rufe fuska "ban taba jin haka ba tunda nake akan kowa"
"Me kike ji Qareeba?" Bilya ya sami kansa da tambayarta. Sosai yake jindadin magana da ita.
"Farinciki"
Karamar dariya yayi ta dago da kai "don Allah kada ka samin rai kaima naji shiru. Nasan Ahirin ya fada maka komai a kaina amma wallahi ba'ayi raping dina ba"
Bilya ji yayi ko gobe akace yazo a daura musu aure zai yarda saboda yadda Qareeba ta shiga zuciyarsa musamman saboda tausayi.
"Ki bari nayi zuwa uku sai mu tabbatar da zamu iya zama da juna. Sai dai matsala daya wallahi Dahiru baya son sunan nan Ahirin"
Bude mayafin tayi ta sa dariya "ai wallahi sai dai yayi hakuri sunansa kenan a wurina"
******
Dahiru da Attahir a kafa suka fita tunda ba nisa bane titi kawai zasu tsallaka suyi tafiyar kasa da minti biyar.
Fitowarsu a idon BB da Bobo ya tabbatar Mawadda bata bayansu yace "Bobo dawo nan da sauri"
Chanjin seat suka yi ya tada mota da sauri ya bata wuta. Attahir ya haye dan tudun gefen titi inda zai sada shi da gidansu shi kuma Dahiru yana daga bayansa. Daga kafarsa ke da wuya basu san daga ina ba sai ganinsa suka yi yayi sama saboda wani mugun bugu da BB yayi masa ya dawo ya daki kan bonnet dinta ya fadi kasa ko motsi kwakkwara baya yi.
Attahir mutuwar tsaye yayi har maigadin gidan Dr Auwal da wasu maza suka taho suna kokarin daga Dahiru. Jikinsa gabadaya ji yake kamar an sara masa guduma. Bai tashi gane me yake yi ba sai da suka yi ido da ido da BB Sule Chanji yayin da ya fizgi motar a guje kamar zai tashi sama.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰23
*Batul Mamman*💖
Kwanaki shadaya da auren su Dahiru wanda yayi daidai da kwana goma da tarewar Mawadda. A dan tsukin lokacin nan shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu. Duk abinda Dahiru zaiyi domin ya cire mata tsoro kuma ta saki jiki dashi yana yi. Shiyasa bata da wata damuwa sai ta kokarin kyautata masa.
Zamansu gwanin sha'awa kana ganinsu kaga masoyan da suka yi nisa cikin soyayyar juna. Tsakaninsu dasu Attahir ma sai son barka. Matan suna matukar kokari su hada kai domin jindadin mazansu. Nawal bata da matsala. Yadda ta rungumi Mawadda babu kyama ko nuna ta fita domin ita a yanzu bautar kasa zata fara sabanin Mawadda da Adult education tayi.
Yau da sassafe matan suka tashi saboda aikin da yake gabansu. Gidan Baba Prof zasu je daga can kuma kowanne zai tafi da matarsa gidan iyayenta. Washegari kuma Dahiru da Mawadda su tafi Tariwa su kwana biyu.
Mawadda ta gama tuwon shinkafa da miyar agushi tun daga falo kamshin miyar sai yasa yawu tsinkewa. A kasa kuma Nawal ta kusa gama suyar samosa da doughnut da zasu hada su kai musu.
Shadaya da rabi ta gama komai harda breakfast ta gyara gida ta koma daki domin tashin Dahiru sannan tayi wanka. Filon da take sawa tsakaninsu dogo shi ta gani a kasa shi kuma yana amsa waya.
Wardrobe ta bude inda ta jera musu kayansu ta tsaya tana karewa kayanta kallo.
Bayan Dahiru ya gama wayar taji yace "Matar Dahiru yau ba gaisuwa?"
"Ina zuwa gaisheka na ga ka jefar min da dan amana a kasa"
Dariya ya soma yi yayi rub da ciki ya rike fuskarsa da hannuwansa.
"Kin jawo masa yau zan jefa shi ta taga ma. Haka kawai kullum yana tsakiyar mata da miji shi ko tsoron daukan alhaki baya yi ma"
Sai da tayi dariya tace "babu wani hakki, tunda hannunka ya warke ko zaka koma kasa? Idan ka sauka da kaina zan jefar da filon"
"Haka ma zaki ce? Kwana kike makale da shi fa ga bawan Allah a gefe" ya nuna kansa yana bata rai.