Sashe 4
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tashi muje dakina ki kwanta nan zaki takura"
"Yaya ki barni a nan tsoro zanji ni kadai"
"Zan tayaki kwanan tashi mu tafi"
Ba musu ta tashi suna shiga Yaya ta tura kyauren ta hade rai sosai tare da daga wukar yadda Mawadda zata gani.
"Tambayarki zanyi kuma kika sake kika min kuka sai na lahira ya fiki jindadi kin sanni sarai. Me ya sameki???"
Kuka zata fara bakinta ya soma rawa Yaya ta dora yatsanta akan baki "wallahi Mawadda zanci mutumcinki idan kika min karya. Ki bude baki ki fada min uban me kike boyewa? Sata kika yi a gidan suka miki duka ko kuwa?" Har ranta bata son fadin abinda take zargi.
Ta yaya zata fada bayan kashedin da akayi mata? Banda ita duka gidan fa Haj Mara tace zata sa a harbe.
Wukar Yaya ta dago "ko ki fada min ko na yankaki a dakin nan babu wanda ya isa ya kwaceki....kin bude bakin nan ko sai jikinki ya fara jini?"
A raunane Mawadda ta durkushe a kasa "tace harbemu duka harda ku zata sa ayi idan na fada"
"Ita wa kenan?"
"Hajiyan da ta kawoni dazu wadda nake yiwa aiki"
Jikin Yaya duka yayi sanyi hannunta yana rawa ta riko Mawadda.
"Babu wanda ya isa ya cutar da wani sai Allah Yaso. Ki fada min me ya faru"
Kuka mai sauti Mawadda ta soma da kyar ta iya cewa "BB ne"
"Wa kika ce?"
"Dan Hajiyar ne, shine...shine.." kuka ya hanata cigaba
Yaya tuni zarginta ya kara tabbata. Wukar ta yar tayi kan Mawadda ta kwantar da ita tare da janye zanin jikinta. Abinda idonta ya gani yasa tayi baya a gigice tana salati. Tana kaiwa jikin bango ta sulale a kasa kawai sai ta fashe da kuka.
Mawadda ta rarrafo ta fada kanta itama tana yi.
"Yaya wallahi fin karfi yayi min...ya zaneni, ya fasa min baki sannan....kuma nayi ta rokon Hajiyar ta maidoni gida tunda ya fara bina taki. Ciwon da nake ji Yaya gara na mutu na huta"
Yaya bata iya cewa komai ba sai kukan da take bilhakki.
Mal Fatihu wanda tun fitar Yaya ya taso shima musamman da yaga ta dauko wuka yana jingine a jikin kofar dakin yaji jiri na dibarsa bayan ya gama jin komai. Duk tunaninsa bai taba hasashen zai ji wannan bakin labari ba.
Kofar dakin ya dan buga a hankali "Haule bude min kofar nan"
Da saurinta ta tashi ta bude yana shigowa ta nuna masa Mawadda wadda ta gama tsurewa saboda yanayin fuskarsa duk da rashin wadatar haske babu annuri.
"Malam fyade akayi mata...mun shiga uku Malam....na gani da idona wallahi aikin karfi ne da ganin wannan rashin imani"
Hannun 'yarsa ya kama ya tayar da ita tsaye.
"Ki dubi girman Allah ki fada min gaskiya karfi aka saka miki ko kwadayi ne yasa kika kai kanki?"
Tana kuka ta rinka basu labarin abinda BB yayi mata. Ba komai bakinta ya iya maimaitawa ba tana kuka iyayenta suna yi.
Baba yana rike da ita ya share mata hawaye "Allah Ya isanmu Mawadda, Allah zai bi mana hakkinmu zaiyi miki sakayya kinji"
A fusace Yaya ta mike tana kuke ido "Malam kada kace min a iya nan zaka bar maganar nan? Shegiyar mata don rashin kunya ta shigo har gidan nan tace wai tafiya ce ta kamasu. Mu zata wulakanta saboda suna da arziki. Yanzu mutumcin 'yar tamu da aka kwata ta karfi shine aka fanshe shi a dubu ashirin din da ta bayar dazu. Kudinsu na banza to Yasin bazamu lamunta ba"
Baba yace tayi a hankali dare ne fa "banda abinki me zaki iya yi musu? Ya riga ya cucemu sai dai mu barsu da Allah"
"Shikenan mu talakawa ba mutane bane Malam? Hawayenmu ruwane? Bakinciki, damuwa da ciwonmu duka ba ababen dubawa bane saboda bamu da kudi?" Yaya ta fada tana sake rushewa da kuka.
Daren ranar babu wanda ya rintsa cikinsu daga kuka sai kuka. Baba ne yayi karfin halin dauro alwala ya tayar da nafila domin neman sassauci.
******
Kwanuka ne jibge a gabanta tana wankewa ga rana ta take har ruwa idanunta suke yi. Kofi aka jeho ya sameta a tsakiyar baya sai da ta gantsare. A haka ma wai don na roba ne. Bata bukatar karin bayani tasan ko waye da wannan aikin. Duk gidan babu wanda ya rainata a matsayinta na mai aiki kamarsa.
"Ke Ade Umma tana kiranki tace kiyi sauri"
Fara'ar dole ta nemo ta yaba a fuskarta kafin ta bashi amsa.
"Abbati kace mata ina zuwa kaji, kuma don Allah ka dena jifa ka tuna na fada maka babu kyau" ta kare da sassauta murya. Indai zai kawo wani abu wurinta to sai dai ya jefa mata saboda baya son ta taba shi ma balle ta rabi jikinsa tunda dai sunanta mai aiki.
Ko kallonta baiyi ba da tayi maganar ya juya yana buga game a wayar babarsa. Gumi ne sharkaf a jikin Ade haka ta tashi ta dauraye hannunta sannan ta shiga cikin katon gidan ta kofar kitchen dake baya.
Sanyi ne mai ratsa jiki ya marabceta a falon matar gidan ta durkusa daga can gefe
Yaronta karami dan shekara uku da rabi ta nuna mata yana tsaye a jikin labule.
"Fa'iz ne yayi kashi kije kiyi masa tsarki. Idan kin gama ki gyara min wurin sosai kinsanni da jin wari. Kin karasa wanke wanken ne?"
Ade har tayi gaba tana kokarin daga dirkeken yaron mai uwar kiba tace saura kadan.
"Ni kuwa bana son nawa Ade gashi na kula kamar halinki ne. Kinsan sarai duk laraba sai kin wanke komai na kitchen saboda bana son ganin kwanukana da kura amma sai ki wuni abu daya" tana magana tana hade rai
Dan murmushi Ade tayi. A lalace tasan ko yaya zata baiwa matar nan shekara goma. Tasan ita ce a kasa dole ta bi ta amma wani wulakancin ko darajar shekaru ai a raga maka.
Wucewa tayi ta gabatar da aikin da aka sakata. Bayan ta gama ta koma wurin wanke-wanken a tsakar rana. Gida ne babba mai kyau don kuwa maigidan dan kwangila ne da ya shahara. Uwardakinta Sakina ce matarsa ta uku kuma kowace gidanta daban. 'Ya'yanta hudu duk maza shiyasa take fankama ita a dole ta kama gida saboda sauran yaransu maza bibbiyu ne.
Wurin ajiye motoci an kebe shi daban anyi rumfa. Haka wurin wasan yaran da ma wurin da maigidan yakan zauna shan iska a lambun gidan. Sai dai kash, wurin da Ade tafi wuni tana aikin wanke-wanke babu koda langa langa. Komai rana haka take yi, idan kuma ana ruwa ta koma ciki yana daukewa ta dawo, ba'a taba tunanin gyarawa ba tamkar ba mutum ke aiki a wurin ba. Uwardakin nata tamkar mai aljanu ko ruwa aka sha da kofi to ya zama kayan wanke wanke kuma. Ita gadara yaranta fitsara.
Sai da ta gama komai ta koma falon can inda aka ce ta rinka dakatawa saboda ba'a taka kafet indai ba maisharar cikin gidan ba ta durkusa.
"Dama akan maganar da na soma yi miki ce rannan na zuwa gida naga baki ce komai ba"
Tsaki Sakina ta buga ta ajiye remote din hannunta.
"Bala'i! wato na lura Ade ke fa da mayya ce idan kika kama mutum sai buzunsu. Kin tado maganar nan yafi sau biyar saboda bana son ji nake katseki amma kinki hakura. Ku wai baku da aiki sai son zuwa gida? Kwanaki kince kaciya akayiwa autanki na barki kinje har kwana biyu yanzu kuma kina son sake zuwa wani wurin..wane uzurin gareki kuma?"
Duk da ranta ya baci haka ta danne "Yarinyata ce bikinta ya matso watan cika ciki"
"Yarinyarki kuma? Yaranki duka ba maza bane su hudu kuma dai ai suna yawan zuwa gidan nan ganinki tunda suma a cikin Kanon suke"
"Ita babbar a kauyenmu take wurin nata mahaifin"
Sakina ta sake jan tsaki. Wannan abu yana matukar konawa Ade rai don bata son ayi mata tsaki amma ya ta iya.
"Gaskiya bana son yawo Ade idan aikin kika gaji dashi sai na nemi wata"
Hankali a tashe tace "Hajiya me ya kawo neman wata? Wallahi bikin 'yata ne baifi wata biyu ya rage ba. Shine nace bari na sanar dake da wuri don nasan ba kya son titsiye"
Shiru Sakina tayi tana tunanin muddin Ade ta tafi zasu wahala. Ita take wanke wanke da kula da yara. Mai shara namiji ne dama sai mai girki wata bayerabiya duk rashin mutumcinta bata iya yi mata saboda tsoronta ma take ji. Matar bata daukar raini don da iliminta. Ade kuwa marainiyar wayonta ko waya zata kira sai ta bata ta roki ta nemo mata sunan da take son kira.
Da gangan tasha kunu "Ni dai bangane wani watan cika ciki ba. Bayan sallah da kusan sati biyar za'ayi bikin babban dan Alhaji kuma baki da yawa zasu sauka a gidana. Idan kin bincika watan bikin yar taki a na bature sai ki fada min. Satin bikin ki tafi talata ki dawo lahadi. Nasan halin mutanenmu uwar amarya bata wani abin kirki a bikin 'yarta akwai 'yan uwa da abokan arziki."
Ade tayi shiru tana tunani. Wato bikin dan Alhaji shine biki na 'yarta kuma ko oho. Dan kudin da take samu a gidan ba karamin tallafi yake mata ba. Ga yara hudu a gidan mijin data baro ga babbar a kauye tare da nata uban da aurensu ya dade da mutuwa. Bazata so rasa aikin nata ba shiyasa ta amince da sharadin Sakina ba don taso ba.
Murmushi tayi wai Mawaddanta ta isa aure. Da aikin nan ta hada ya kusa dubu dari da zata fito da tilon diyarta wadda kaddara ta rabasu.
*****
"Yaya ki barni a nan tsoro zanji ni kadai"
"Zan tayaki kwanan tashi mu tafi"
Ba musu ta tashi suna shiga Yaya ta tura kyauren ta hade rai sosai tare da daga wukar yadda Mawadda zata gani.
"Tambayarki zanyi kuma kika sake kika min kuka sai na lahira ya fiki jindadi kin sanni sarai. Me ya sameki???"
Kuka zata fara bakinta ya soma rawa Yaya ta dora yatsanta akan baki "wallahi Mawadda zanci mutumcinki idan kika min karya. Ki bude baki ki fada min uban me kike boyewa? Sata kika yi a gidan suka miki duka ko kuwa?" Har ranta bata son fadin abinda take zargi.
Ta yaya zata fada bayan kashedin da akayi mata? Banda ita duka gidan fa Haj Mara tace zata sa a harbe.
Wukar Yaya ta dago "ko ki fada min ko na yankaki a dakin nan babu wanda ya isa ya kwaceki....kin bude bakin nan ko sai jikinki ya fara jini?"
A raunane Mawadda ta durkushe a kasa "tace harbemu duka harda ku zata sa ayi idan na fada"
"Ita wa kenan?"
"Hajiyan da ta kawoni dazu wadda nake yiwa aiki"
Jikin Yaya duka yayi sanyi hannunta yana rawa ta riko Mawadda.
"Babu wanda ya isa ya cutar da wani sai Allah Yaso. Ki fada min me ya faru"
Kuka mai sauti Mawadda ta soma da kyar ta iya cewa "BB ne"
"Wa kika ce?"
"Dan Hajiyar ne, shine...shine.." kuka ya hanata cigaba
Yaya tuni zarginta ya kara tabbata. Wukar ta yar tayi kan Mawadda ta kwantar da ita tare da janye zanin jikinta. Abinda idonta ya gani yasa tayi baya a gigice tana salati. Tana kaiwa jikin bango ta sulale a kasa kawai sai ta fashe da kuka.
Mawadda ta rarrafo ta fada kanta itama tana yi.
"Yaya wallahi fin karfi yayi min...ya zaneni, ya fasa min baki sannan....kuma nayi ta rokon Hajiyar ta maidoni gida tunda ya fara bina taki. Ciwon da nake ji Yaya gara na mutu na huta"
Yaya bata iya cewa komai ba sai kukan da take bilhakki.
Mal Fatihu wanda tun fitar Yaya ya taso shima musamman da yaga ta dauko wuka yana jingine a jikin kofar dakin yaji jiri na dibarsa bayan ya gama jin komai. Duk tunaninsa bai taba hasashen zai ji wannan bakin labari ba.
Kofar dakin ya dan buga a hankali "Haule bude min kofar nan"
Da saurinta ta tashi ta bude yana shigowa ta nuna masa Mawadda wadda ta gama tsurewa saboda yanayin fuskarsa duk da rashin wadatar haske babu annuri.
"Malam fyade akayi mata...mun shiga uku Malam....na gani da idona wallahi aikin karfi ne da ganin wannan rashin imani"
Hannun 'yarsa ya kama ya tayar da ita tsaye.
"Ki dubi girman Allah ki fada min gaskiya karfi aka saka miki ko kwadayi ne yasa kika kai kanki?"
Tana kuka ta rinka basu labarin abinda BB yayi mata. Ba komai bakinta ya iya maimaitawa ba tana kuka iyayenta suna yi.
Baba yana rike da ita ya share mata hawaye "Allah Ya isanmu Mawadda, Allah zai bi mana hakkinmu zaiyi miki sakayya kinji"
A fusace Yaya ta mike tana kuke ido "Malam kada kace min a iya nan zaka bar maganar nan? Shegiyar mata don rashin kunya ta shigo har gidan nan tace wai tafiya ce ta kamasu. Mu zata wulakanta saboda suna da arziki. Yanzu mutumcin 'yar tamu da aka kwata ta karfi shine aka fanshe shi a dubu ashirin din da ta bayar dazu. Kudinsu na banza to Yasin bazamu lamunta ba"
Baba yace tayi a hankali dare ne fa "banda abinki me zaki iya yi musu? Ya riga ya cucemu sai dai mu barsu da Allah"
"Shikenan mu talakawa ba mutane bane Malam? Hawayenmu ruwane? Bakinciki, damuwa da ciwonmu duka ba ababen dubawa bane saboda bamu da kudi?" Yaya ta fada tana sake rushewa da kuka.
Daren ranar babu wanda ya rintsa cikinsu daga kuka sai kuka. Baba ne yayi karfin halin dauro alwala ya tayar da nafila domin neman sassauci.
******
Kwanuka ne jibge a gabanta tana wankewa ga rana ta take har ruwa idanunta suke yi. Kofi aka jeho ya sameta a tsakiyar baya sai da ta gantsare. A haka ma wai don na roba ne. Bata bukatar karin bayani tasan ko waye da wannan aikin. Duk gidan babu wanda ya rainata a matsayinta na mai aiki kamarsa.
"Ke Ade Umma tana kiranki tace kiyi sauri"
Fara'ar dole ta nemo ta yaba a fuskarta kafin ta bashi amsa.
"Abbati kace mata ina zuwa kaji, kuma don Allah ka dena jifa ka tuna na fada maka babu kyau" ta kare da sassauta murya. Indai zai kawo wani abu wurinta to sai dai ya jefa mata saboda baya son ta taba shi ma balle ta rabi jikinsa tunda dai sunanta mai aiki.
Ko kallonta baiyi ba da tayi maganar ya juya yana buga game a wayar babarsa. Gumi ne sharkaf a jikin Ade haka ta tashi ta dauraye hannunta sannan ta shiga cikin katon gidan ta kofar kitchen dake baya.
Sanyi ne mai ratsa jiki ya marabceta a falon matar gidan ta durkusa daga can gefe
Yaronta karami dan shekara uku da rabi ta nuna mata yana tsaye a jikin labule.
"Fa'iz ne yayi kashi kije kiyi masa tsarki. Idan kin gama ki gyara min wurin sosai kinsanni da jin wari. Kin karasa wanke wanken ne?"
Ade har tayi gaba tana kokarin daga dirkeken yaron mai uwar kiba tace saura kadan.
"Ni kuwa bana son nawa Ade gashi na kula kamar halinki ne. Kinsan sarai duk laraba sai kin wanke komai na kitchen saboda bana son ganin kwanukana da kura amma sai ki wuni abu daya" tana magana tana hade rai
Dan murmushi Ade tayi. A lalace tasan ko yaya zata baiwa matar nan shekara goma. Tasan ita ce a kasa dole ta bi ta amma wani wulakancin ko darajar shekaru ai a raga maka.
Wucewa tayi ta gabatar da aikin da aka sakata. Bayan ta gama ta koma wurin wanke-wanken a tsakar rana. Gida ne babba mai kyau don kuwa maigidan dan kwangila ne da ya shahara. Uwardakinta Sakina ce matarsa ta uku kuma kowace gidanta daban. 'Ya'yanta hudu duk maza shiyasa take fankama ita a dole ta kama gida saboda sauran yaransu maza bibbiyu ne.
Wurin ajiye motoci an kebe shi daban anyi rumfa. Haka wurin wasan yaran da ma wurin da maigidan yakan zauna shan iska a lambun gidan. Sai dai kash, wurin da Ade tafi wuni tana aikin wanke-wanke babu koda langa langa. Komai rana haka take yi, idan kuma ana ruwa ta koma ciki yana daukewa ta dawo, ba'a taba tunanin gyarawa ba tamkar ba mutum ke aiki a wurin ba. Uwardakin nata tamkar mai aljanu ko ruwa aka sha da kofi to ya zama kayan wanke wanke kuma. Ita gadara yaranta fitsara.
Sai da ta gama komai ta koma falon can inda aka ce ta rinka dakatawa saboda ba'a taka kafet indai ba maisharar cikin gidan ba ta durkusa.
"Dama akan maganar da na soma yi miki ce rannan na zuwa gida naga baki ce komai ba"
Tsaki Sakina ta buga ta ajiye remote din hannunta.
"Bala'i! wato na lura Ade ke fa da mayya ce idan kika kama mutum sai buzunsu. Kin tado maganar nan yafi sau biyar saboda bana son ji nake katseki amma kinki hakura. Ku wai baku da aiki sai son zuwa gida? Kwanaki kince kaciya akayiwa autanki na barki kinje har kwana biyu yanzu kuma kina son sake zuwa wani wurin..wane uzurin gareki kuma?"
Duk da ranta ya baci haka ta danne "Yarinyata ce bikinta ya matso watan cika ciki"
"Yarinyarki kuma? Yaranki duka ba maza bane su hudu kuma dai ai suna yawan zuwa gidan nan ganinki tunda suma a cikin Kanon suke"
"Ita babbar a kauyenmu take wurin nata mahaifin"
Sakina ta sake jan tsaki. Wannan abu yana matukar konawa Ade rai don bata son ayi mata tsaki amma ya ta iya.
"Gaskiya bana son yawo Ade idan aikin kika gaji dashi sai na nemi wata"
Hankali a tashe tace "Hajiya me ya kawo neman wata? Wallahi bikin 'yata ne baifi wata biyu ya rage ba. Shine nace bari na sanar dake da wuri don nasan ba kya son titsiye"
Shiru Sakina tayi tana tunanin muddin Ade ta tafi zasu wahala. Ita take wanke wanke da kula da yara. Mai shara namiji ne dama sai mai girki wata bayerabiya duk rashin mutumcinta bata iya yi mata saboda tsoronta ma take ji. Matar bata daukar raini don da iliminta. Ade kuwa marainiyar wayonta ko waya zata kira sai ta bata ta roki ta nemo mata sunan da take son kira.
Da gangan tasha kunu "Ni dai bangane wani watan cika ciki ba. Bayan sallah da kusan sati biyar za'ayi bikin babban dan Alhaji kuma baki da yawa zasu sauka a gidana. Idan kin bincika watan bikin yar taki a na bature sai ki fada min. Satin bikin ki tafi talata ki dawo lahadi. Nasan halin mutanenmu uwar amarya bata wani abin kirki a bikin 'yarta akwai 'yan uwa da abokan arziki."
Ade tayi shiru tana tunani. Wato bikin dan Alhaji shine biki na 'yarta kuma ko oho. Dan kudin da take samu a gidan ba karamin tallafi yake mata ba. Ga yara hudu a gidan mijin data baro ga babbar a kauye tare da nata uban da aurensu ya dade da mutuwa. Bazata so rasa aikin nata ba shiyasa ta amince da sharadin Sakina ba don taso ba.
Murmushi tayi wai Mawaddanta ta isa aure. Da aikin nan ta hada ya kusa dubu dari da zata fito da tilon diyarta wadda kaddara ta rabasu.
*****