Sashe 26
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna komawa gida Mawadda ta hau hirar gyaran jiki tana bawa su Yaya labari abinda ba halinta ba. Kowa yana mata dariya ko a jikinta.
Bayan kwana biyu Iya tace waken soyan da Innar Dahiru ta basu suyi awara dashi mana suci. Ai kuwa anyi awara Mawadda da Rafi'a suka tsiri jajjagen attaruhu da albasa suka soya yana ta kamshi suka ci dashi. Abu yayi musu dadi suka fara tunanin ko zasu fara awarar siyarwa. Kamar da wasa suka yi ta mai kyau da dadi maimakon yaji sai wannan jajjagen na attaruhu da albasa. Makota suka shiga suna sanarwar sun fara awara amma har dare ko kaza bata shigo saya ba. Allah Yasa ba yawa suka yi suka cinye abinsu.
Bayan wasu kwanaki Marwanu da Saifullahi suka ce sun gano masu kayan sayarwa a gefen titi a sake suyar awara zasu kai can. Batare da gajiyawa ba sukayi ta rabin kwano kada ta sake kwantai.
'Yar roba suka samu Mawadda ta yanka kabeji, tattasai da albasa kananu tace idan sun zubawa mutum sai su dan diba a watsa a kai.
'Yan samarin ba girman kai suka tafi shiru babu wanda ya tsaya siyan tasu. Haka sukayi ta yi har sau hudu. A karo na biyar Saifullahi zaman ya ishe shi sai ya soma waka yana cewa
"tamu ba irin tasu bace...awarmu ba irin tasu bace" haka nan ya kirkiri kayarsa yana yi Marwana ya hau buga cokali akan kwanon da ake zuba mahadin awarar. Mutane suna ta kallonsu wani mutum yace bari dai a bashi yaji irin tasu.
Da rawar jiki Marwanu ya zuba masa Saifullahi yana cewa "kasan shi yaji iska na kadawa sai ido mutum yazo ya kasa gane hanyar gida. Mu kuwa namu a soye yake ga gishiri ga mai tauraro, wani abin sai kaci dai"
Mutane suna ta dariya mutumin nan yaci ya hau santi. Kan kace kwabo an siyeta tas kowa yana cewa an ga sabon salo.
Awarsu uku da fita Yaya taji sallama.
"Oh ni Haule sai mu hakura da awarar nan kuma a nemi wata sana'ar. Kitson ma shiru babu wadda ta leko"
Baba yace tayi hakuri komai lokaci ne sai ga su Marwanu da kwanuka kwalam. Dadi ya kama mutan gidan kar ma Baba yaji labari. Yana zaune bashi da wani abu da zai iya domin tallafin gidansa.
A ranar suka fara tsarin yadda kasuwar awara zata cigaba. Cikin dan kankanin lokaci ta sami karbuwa har a cikin unguwa. Da rana tsaka sai mace taki girki a tura gidan awara a siyo. Kitson Jamila shima lokacin aka gane masa ya zamana gidan basa rasa abin batarwa.
Ana haka Zahra mai gyaran jiki tazo. Bayan 'yar hira dayake tana da mutumci take cewa Mawadda idan bata komai ta rinka zuwa tayata aiki don lokacin bukukuwa ya gabato saboda karshen shekara ne. Abu kamar wasa Mawadda ta fara don yanzu ta saki ranta ba kamar da ba. Matsalarta kuma ta ragu sosai yanzu sai idan tayi tari, zabura, ko wani aikin da zaisa jikinta motsawa ba shiri shine fitsarin yakan digo. Duk da haka kuma Ade tana dan tarin kudadenta idan anyi albashi ta kaiwa masu kemis ta siyo mata magani da kuma na Baba na hawan jini.
******
Karshen zangon farko na karatu yayi inda Dahiru yayu matukar dagewa ya sami G.P.A 2.34, ranar harda hawaye yayi saboda Prof yace masa so yake yayi kokari sosai sai gashi duk da babu darasin da zai sake maimaitawa amma bai sami yadda yaso ba. Rashin turancin nan da kuma rashin wadatar lokacin karatu yasa abubuwan nasa sai a hankali.
Yanzu sunyi sabo sosai da Baba Prof yana zuwa gidansa lokaci lokaci. Ranar da ya sanar dashi sakamakonsa duk kuwa da Prof Abdulhadi ya ma riga shi sani ya nuna masa farincikinsa sosai. Babu abinda ya bashi mamaki sai dauke masa nauyin kudin makaranta da yayi kamar yadda yayi masa alkawarin yi masa wani abun mamaki tun baya. Baffa da Bilya har gida suka je yi masa godiya yace da na kowa ne. Burinsa kawai Dahiru yayi karatu idan Allah Ya bashi iko shima ya zama inuwar da wani zai raba a gaba.
Har suka koma gida suna yabon kyaun hali irin na wannan bawan Allah. Ya hada Dahiru da dansa Attahir wanda shi yanzu yake shirin shiga jami'ar abota shiyasa zumuncinsu ya karu sosai.
******
"Kin sake magana da kawarki kuwa akan zancen yaran nan? Shirun yayi yawa" cewar Daddyn su Qareeba yana kallon Dr Tani fuska ba fara'a.
Tasan za'a rina yanzu kusan kullum sai ya tado zancen. Sun gama bazawa 'yan uwansu cewa biki ya matso komai lokaci guda za'ayi amma har yanzu wata kusan biyar ba amo ba labari. Sai ta jera sati tana kiran Haj Mara bata daukar wayar. Idan ta dauka a dakila take amsawa tana mata karyar aiki ne yake rike Babawo ita kuma tun zaman kotun nan lafiya tayi mata karanci.
Dr Tani dai ta shiga muguwar damuwa yayin da Qareeba soyayyar Babawo ta hanata sukuni.
A can Kaduna kuma Haj Mara ta rasa yadda zatayi don Alh Sule tun wannan tafiyar tasa China har yanzu bata sake saka shi a ido ba. Kamar kullum bashi da zancen da ya wuce zama ne baya yi sosai shiyasa taji shiru.
Tana zaune ta rafka tagumi bayan sun gama waya BB ya shigo yana tangadi. Tashi tayi hankali a tashe ta soma masa fada. Shima ya daga hannu yana nunata da yatsa yana fada cikin muryar maye.
"Hajjaju wal Makkatu ina matata Mawadda?
Tsaki taja "Babawo ka shiga taitayinka fa. An baka aiki kaki tafiya har sun cike gurbin da wani. Baka da abin yi sai kokarin lalata rayuwarka ko"
Ya zauna kamar kayan wanki a kujera "to kiyi min aure mana ki gani idan ban shiryu ba"
"Za ka auri Qareeba din ne? Dazu ma nayi ta ganin wayar Dr din ai"
"Dangin dolayen??? Gaskiya kin ma cuceni Hajjaju. Ai ni duniya babu wata mace a idona sai Mawadda. Duk sauran mata sunansu majajjawa"
Duka ta kai masa "dan ubanka harda ni?"
Ya dago yatsansa yana dariya "kece lamba one....hahahahhh"
'Yan uwansa mata tayi niyar kira to amma dukkansu ta kula wani zukewa suke daga gareta. Ga miji baya nan ji tayi komai ya soma kwance mata. Hanyar hawa sama ta nufa kakarin aman BB ya tsayar da ita. A nan kan tsadadden kafet dinta ya kwara abinsa ya damalmale ciki. Kamar tayi kuka amma babu wanda zata ce yazo ya gyara ko da dattijuwar dake mata aiki ce kada a sami na bada labari haka ta dawo tana gyarawa yana ta zage zage.
"Hajjaju ni dake nace kada ki sola ni akan maganar Mawadda ki ka ki. Ki nemo min ita miyi aure a ragargaji soyayya ko kuma wallahi na ragargazo miki ta'asa a gidan nan"
Dena abinda takeyi tayi tana kallonsa shima ya kafeta da ido. Shi fa banda tsoron shiga kurkuku da tuni a kotun nan ya fadi gaskiya.
Duk wani tunaninta ya kulle mafita daya ta hango idan ba haka ba yaron nan a gaba sai ya hanata shiga taro.
*****
*SHEKARA KWANA: 2018*
Wata macece mai cike da kamala da haiba ta shiga ofishin likita bayan an kira sunanta. Sanye take da doguwar rigar atampa ta daura dankwalinta ta yane kanta da mayafi mai kyau wanda ya dace da kayan. Ko kadan shigarta babu bayyana tsiraici don indai zata sa mayafi to fa sai wanda ta tabbatar ba shara-shara bane. Duk da ba kwalliya tayi ba da ta wuce kwalli, hoda da man lebe amma kallo daya zaka yi mata kasan cewa mace ce da tasan me take yi.
Da sallama ta shiga ofishin ta sami likitan zaune akan kujerar marasa lafiya yayin da yake nuna mata tasa da hannu nufinsa ta zauna.
Cogewa tayi a tsaye "Ni dai zan roki a canja min likita gaskiya idan haka zaka rinka yi min"
Mikewa yayi yana dariya ya koma mazauninsa "abin bai kai haka ba zo ki zauna ranki ya dade"
Zama tayi suka gaisa tayi masa bayanin yadda take ji yanzu kusan ta gama warkewa daga lalurarta ta rashin rikon fitsari. Ya ji dadi sosai yace zata yi wata batare da wani magani ba domin su tabbatar da samun lafiyarta.
"Alhamdulillah Mawadda wannan sauki daga Allah ne da kuma dagewarki wurin shan magunguna da yin kegel exercise yadda ya kamata. To sauki ya samu sai maganar aurenmu ko?" Ya daga mata gira.
Kai ta girgiza tana murmushi "kayi ka gama. Tare muke da Baba yana wurin karbar magani na barka lafiya"
"Mawadda meyasa kike min haka ne?" Ya fada a sanyaye.
Dan hade fuska tayi "saboda kasan komai game da ni Dr Imran. Babu wani dalili da zaisa kai ko wani yayi sha'awar aurena. Sannan....kasan burina na rayuwa har yau bai cika ba"
Cewa yayi zai kirata kawai don idan suka fara wannan muhawarar zancen baya taba karewa. Kafiya ce da ita sai kace irin mutanen farkon nan. Akwai ranar da ya zolaye ta ma yace da a wancan zamanin tazo irinsu ne suke yin riko da manyan gumaka a kasa chanja musu ra'ayi. Baya mantawa ranar ne ta fara sakin jiki dashi saboda dariyar da ya sakata sai dai gashi har sun bawa shekara baya babu wani cigaba.
Wurin Baba taje ya gama karbar magani da Saifullahi suka fito suka tafi.
Mawadda Fatihu kenan matashiya yar kimanin shekaru ashirin da biyar. Taga rayuwa ita da gabadaya ahalin gidansu a dalilin fyade da akayi mata a gidan da take aiki.
Bayan dawowarsu Kano sunyi ta fadi tashi har Allah Ya buda musu da taimakon Anti Zahra mai gyaran jiki. Matar nan ta riketa da zuciya daya ta koya mata sana'ar gyaran jiki sosai. Da ita take biyanta idan sunyi aiki daga baya cikin ikon Allah ta kware Anti Zahra tace lokaci yayi taci gashin kanta. Sannan ita sun dade da barin unguwar ta koma tudun yola da zama. Suna zumunci sosai har yanzu. A lalace a wata Mawadda bata sami kudi ba ta rike dubu talatin. Budi suka samu na ban mamaki da tasbihi ga Allah. Matan manya da 'yan uwa bata taba rainawa har kasuwarta ta bude haka.
Bayan kwana biyu Iya tace waken soyan da Innar Dahiru ta basu suyi awara dashi mana suci. Ai kuwa anyi awara Mawadda da Rafi'a suka tsiri jajjagen attaruhu da albasa suka soya yana ta kamshi suka ci dashi. Abu yayi musu dadi suka fara tunanin ko zasu fara awarar siyarwa. Kamar da wasa suka yi ta mai kyau da dadi maimakon yaji sai wannan jajjagen na attaruhu da albasa. Makota suka shiga suna sanarwar sun fara awara amma har dare ko kaza bata shigo saya ba. Allah Yasa ba yawa suka yi suka cinye abinsu.
Bayan wasu kwanaki Marwanu da Saifullahi suka ce sun gano masu kayan sayarwa a gefen titi a sake suyar awara zasu kai can. Batare da gajiyawa ba sukayi ta rabin kwano kada ta sake kwantai.
'Yar roba suka samu Mawadda ta yanka kabeji, tattasai da albasa kananu tace idan sun zubawa mutum sai su dan diba a watsa a kai.
'Yan samarin ba girman kai suka tafi shiru babu wanda ya tsaya siyan tasu. Haka sukayi ta yi har sau hudu. A karo na biyar Saifullahi zaman ya ishe shi sai ya soma waka yana cewa
"tamu ba irin tasu bace...awarmu ba irin tasu bace" haka nan ya kirkiri kayarsa yana yi Marwana ya hau buga cokali akan kwanon da ake zuba mahadin awarar. Mutane suna ta kallonsu wani mutum yace bari dai a bashi yaji irin tasu.
Da rawar jiki Marwanu ya zuba masa Saifullahi yana cewa "kasan shi yaji iska na kadawa sai ido mutum yazo ya kasa gane hanyar gida. Mu kuwa namu a soye yake ga gishiri ga mai tauraro, wani abin sai kaci dai"
Mutane suna ta dariya mutumin nan yaci ya hau santi. Kan kace kwabo an siyeta tas kowa yana cewa an ga sabon salo.
Awarsu uku da fita Yaya taji sallama.
"Oh ni Haule sai mu hakura da awarar nan kuma a nemi wata sana'ar. Kitson ma shiru babu wadda ta leko"
Baba yace tayi hakuri komai lokaci ne sai ga su Marwanu da kwanuka kwalam. Dadi ya kama mutan gidan kar ma Baba yaji labari. Yana zaune bashi da wani abu da zai iya domin tallafin gidansa.
A ranar suka fara tsarin yadda kasuwar awara zata cigaba. Cikin dan kankanin lokaci ta sami karbuwa har a cikin unguwa. Da rana tsaka sai mace taki girki a tura gidan awara a siyo. Kitson Jamila shima lokacin aka gane masa ya zamana gidan basa rasa abin batarwa.
Ana haka Zahra mai gyaran jiki tazo. Bayan 'yar hira dayake tana da mutumci take cewa Mawadda idan bata komai ta rinka zuwa tayata aiki don lokacin bukukuwa ya gabato saboda karshen shekara ne. Abu kamar wasa Mawadda ta fara don yanzu ta saki ranta ba kamar da ba. Matsalarta kuma ta ragu sosai yanzu sai idan tayi tari, zabura, ko wani aikin da zaisa jikinta motsawa ba shiri shine fitsarin yakan digo. Duk da haka kuma Ade tana dan tarin kudadenta idan anyi albashi ta kaiwa masu kemis ta siyo mata magani da kuma na Baba na hawan jini.
******
Karshen zangon farko na karatu yayi inda Dahiru yayu matukar dagewa ya sami G.P.A 2.34, ranar harda hawaye yayi saboda Prof yace masa so yake yayi kokari sosai sai gashi duk da babu darasin da zai sake maimaitawa amma bai sami yadda yaso ba. Rashin turancin nan da kuma rashin wadatar lokacin karatu yasa abubuwan nasa sai a hankali.
Yanzu sunyi sabo sosai da Baba Prof yana zuwa gidansa lokaci lokaci. Ranar da ya sanar dashi sakamakonsa duk kuwa da Prof Abdulhadi ya ma riga shi sani ya nuna masa farincikinsa sosai. Babu abinda ya bashi mamaki sai dauke masa nauyin kudin makaranta da yayi kamar yadda yayi masa alkawarin yi masa wani abun mamaki tun baya. Baffa da Bilya har gida suka je yi masa godiya yace da na kowa ne. Burinsa kawai Dahiru yayi karatu idan Allah Ya bashi iko shima ya zama inuwar da wani zai raba a gaba.
Har suka koma gida suna yabon kyaun hali irin na wannan bawan Allah. Ya hada Dahiru da dansa Attahir wanda shi yanzu yake shirin shiga jami'ar abota shiyasa zumuncinsu ya karu sosai.
******
"Kin sake magana da kawarki kuwa akan zancen yaran nan? Shirun yayi yawa" cewar Daddyn su Qareeba yana kallon Dr Tani fuska ba fara'a.
Tasan za'a rina yanzu kusan kullum sai ya tado zancen. Sun gama bazawa 'yan uwansu cewa biki ya matso komai lokaci guda za'ayi amma har yanzu wata kusan biyar ba amo ba labari. Sai ta jera sati tana kiran Haj Mara bata daukar wayar. Idan ta dauka a dakila take amsawa tana mata karyar aiki ne yake rike Babawo ita kuma tun zaman kotun nan lafiya tayi mata karanci.
Dr Tani dai ta shiga muguwar damuwa yayin da Qareeba soyayyar Babawo ta hanata sukuni.
A can Kaduna kuma Haj Mara ta rasa yadda zatayi don Alh Sule tun wannan tafiyar tasa China har yanzu bata sake saka shi a ido ba. Kamar kullum bashi da zancen da ya wuce zama ne baya yi sosai shiyasa taji shiru.
Tana zaune ta rafka tagumi bayan sun gama waya BB ya shigo yana tangadi. Tashi tayi hankali a tashe ta soma masa fada. Shima ya daga hannu yana nunata da yatsa yana fada cikin muryar maye.
"Hajjaju wal Makkatu ina matata Mawadda?
Tsaki taja "Babawo ka shiga taitayinka fa. An baka aiki kaki tafiya har sun cike gurbin da wani. Baka da abin yi sai kokarin lalata rayuwarka ko"
Ya zauna kamar kayan wanki a kujera "to kiyi min aure mana ki gani idan ban shiryu ba"
"Za ka auri Qareeba din ne? Dazu ma nayi ta ganin wayar Dr din ai"
"Dangin dolayen??? Gaskiya kin ma cuceni Hajjaju. Ai ni duniya babu wata mace a idona sai Mawadda. Duk sauran mata sunansu majajjawa"
Duka ta kai masa "dan ubanka harda ni?"
Ya dago yatsansa yana dariya "kece lamba one....hahahahhh"
'Yan uwansa mata tayi niyar kira to amma dukkansu ta kula wani zukewa suke daga gareta. Ga miji baya nan ji tayi komai ya soma kwance mata. Hanyar hawa sama ta nufa kakarin aman BB ya tsayar da ita. A nan kan tsadadden kafet dinta ya kwara abinsa ya damalmale ciki. Kamar tayi kuka amma babu wanda zata ce yazo ya gyara ko da dattijuwar dake mata aiki ce kada a sami na bada labari haka ta dawo tana gyarawa yana ta zage zage.
"Hajjaju ni dake nace kada ki sola ni akan maganar Mawadda ki ka ki. Ki nemo min ita miyi aure a ragargaji soyayya ko kuma wallahi na ragargazo miki ta'asa a gidan nan"
Dena abinda takeyi tayi tana kallonsa shima ya kafeta da ido. Shi fa banda tsoron shiga kurkuku da tuni a kotun nan ya fadi gaskiya.
Duk wani tunaninta ya kulle mafita daya ta hango idan ba haka ba yaron nan a gaba sai ya hanata shiga taro.
*****
*SHEKARA KWANA: 2018*
Wata macece mai cike da kamala da haiba ta shiga ofishin likita bayan an kira sunanta. Sanye take da doguwar rigar atampa ta daura dankwalinta ta yane kanta da mayafi mai kyau wanda ya dace da kayan. Ko kadan shigarta babu bayyana tsiraici don indai zata sa mayafi to fa sai wanda ta tabbatar ba shara-shara bane. Duk da ba kwalliya tayi ba da ta wuce kwalli, hoda da man lebe amma kallo daya zaka yi mata kasan cewa mace ce da tasan me take yi.
Da sallama ta shiga ofishin ta sami likitan zaune akan kujerar marasa lafiya yayin da yake nuna mata tasa da hannu nufinsa ta zauna.
Cogewa tayi a tsaye "Ni dai zan roki a canja min likita gaskiya idan haka zaka rinka yi min"
Mikewa yayi yana dariya ya koma mazauninsa "abin bai kai haka ba zo ki zauna ranki ya dade"
Zama tayi suka gaisa tayi masa bayanin yadda take ji yanzu kusan ta gama warkewa daga lalurarta ta rashin rikon fitsari. Ya ji dadi sosai yace zata yi wata batare da wani magani ba domin su tabbatar da samun lafiyarta.
"Alhamdulillah Mawadda wannan sauki daga Allah ne da kuma dagewarki wurin shan magunguna da yin kegel exercise yadda ya kamata. To sauki ya samu sai maganar aurenmu ko?" Ya daga mata gira.
Kai ta girgiza tana murmushi "kayi ka gama. Tare muke da Baba yana wurin karbar magani na barka lafiya"
"Mawadda meyasa kike min haka ne?" Ya fada a sanyaye.
Dan hade fuska tayi "saboda kasan komai game da ni Dr Imran. Babu wani dalili da zaisa kai ko wani yayi sha'awar aurena. Sannan....kasan burina na rayuwa har yau bai cika ba"
Cewa yayi zai kirata kawai don idan suka fara wannan muhawarar zancen baya taba karewa. Kafiya ce da ita sai kace irin mutanen farkon nan. Akwai ranar da ya zolaye ta ma yace da a wancan zamanin tazo irinsu ne suke yin riko da manyan gumaka a kasa chanja musu ra'ayi. Baya mantawa ranar ne ta fara sakin jiki dashi saboda dariyar da ya sakata sai dai gashi har sun bawa shekara baya babu wani cigaba.
Wurin Baba taje ya gama karbar magani da Saifullahi suka fito suka tafi.
Mawadda Fatihu kenan matashiya yar kimanin shekaru ashirin da biyar. Taga rayuwa ita da gabadaya ahalin gidansu a dalilin fyade da akayi mata a gidan da take aiki.
Bayan dawowarsu Kano sunyi ta fadi tashi har Allah Ya buda musu da taimakon Anti Zahra mai gyaran jiki. Matar nan ta riketa da zuciya daya ta koya mata sana'ar gyaran jiki sosai. Da ita take biyanta idan sunyi aiki daga baya cikin ikon Allah ta kware Anti Zahra tace lokaci yayi taci gashin kanta. Sannan ita sun dade da barin unguwar ta koma tudun yola da zama. Suna zumunci sosai har yanzu. A lalace a wata Mawadda bata sami kudi ba ta rike dubu talatin. Budi suka samu na ban mamaki da tasbihi ga Allah. Matan manya da 'yan uwa bata taba rainawa har kasuwarta ta bude haka.