← Book details Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 68

Sashe 15

Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Sakamakon urinalysis da aka yi mata ya nuna bata kamu da wata kwayar cuta ba irin wadanda suke kama mafitsara. Saboda haka zan dorata akan magunguna sannan akwai abubuwan da nake bukatar ta kiyaye. Ku dan bamu wuri zanyi mata bayani"

Su Iya ne akan gaba wurin fita. Dr Tani ta kalli Mawadda tana dan murmushi. Yarinyar ta bata tausayi sosai har labarin abinda ya sameta ta bawa iyalinta.

"Kina jin saukin jikinki yanzu?"

"Eh" ta amsa murya can kasa.

"Abinda nake so dake shine na farko bana so kina zama da fitsarin nan duk da na kula ana chanja miki zani akai akai. Ga auduga nan za'a baki sai ki rinka sakawa ko da ya digo bazai taba miki kaya ba. Abu na biyu ina so duk lokacin da kika ji fitsari kiyi kokarin rikonsa na kamar minti biyar....ke security! kirawo min mahaifiyar yarinyar nan dai"

Yaya ce ta shigo Dr ta cigaba da bayanin yadda take so a kula da Mawadda. Idan taji fitsari su rinka dubawa da agogo sai bayan minti biyar da soma jinsa zuwa goma zata je tayi. Kuma ta dage sosai wurin rikonsa kada ya digo. Abu na biyu idan sun je tayi ta tabbatar ta gama sai ta sake dagewa ta kuma matso duk wanda yayi saura. Kada ta tashi sai ta tabbatar a karo na biyun ta sake yin wani komai kankantarsa. Tana so suyi haka na kwana uku domin horar da jijiyoyin wurin. Idan ta gamsu da cewa Mawadda tana yin yadda aka umarceta zasu sallameta sai ta dawo bayan sati daya a dubata amma dole zata cigaba da yin yadda tace din.

"Sai lamari ya baci ake yin aiki wanda bana fata muzo haka dake. Saboda haka ki dage sosai ki bi abubuwan da nace. Magunguna kuma za'a bawa babanta takarda ya siyo da wuri domin a fara amfani dasu."

Wasu cikin magungunan babu a pharmacy din asibitin aka kwatantawa Baba wani a waje. Ya samesu duka amma an kashe kudi kusan dubu hamsin. Yau ba don Iya da Ade ba da kila ko bara ce ta kama yayi zaiyi. Me za'ayi da talauci. Sai yayi huluna suyi sati yanzu ko tayawa ba'ayi balle kuma a saya. Gonar da yake dan nomawa yanzu amfanin da ake samu ba kamar da ba ita ma.

Da nannauyar zuciya ya koma ya kai magungunan. Suna ta fatan Allah Yasa a dace.

Abubuwan da Dr. Tani tace ta kula dasu na yanayin fitsari kuwa ta fara gwadawa iyayenta suna karfafa mata gwiwa.

******

Maigadi ne ya fito jin ana ta buga gate din. Yasan fuskar matar da ya gani duk da bai san sunanta ba amma yasan tana zuwa wurin Haj Mara.

Bude mata yayi suka gaisa ta tambayi Hajiyar yace tana ciki. Da sallama ta shiga. Da Haj Mara taji muryarta wani mugun tsoro ne ya kamata. Murmushi ta kakalo na dole gabanta na faduwa.

"Hajiya Gambo kece a gidan namu?"

Gambo dillaliyar masu aiki tayi dariya "ai ku ne hajiyoyi. Yaya gida da kujiba-kujibar yau da gobe? "

"Lafiya kalau"

Shiru Haj Mara bata sake magana ba tana jira taji me ya kawo Gambo. Ita kuma jira take Hajiyan ta turo mata Mawadda kamar yadda ta saba. Gajiya tayi da jiran tace

"Hajiya ina Mawadda ne? Yarinya na kawo nan Malali shine nace bari na leko mu gaisa."

Haj Mara ta hadiyi wani mugun yawu saboda yadda ta tsorata.

"Mawadda ai ta tsufa a gida"

"Ban fahimta ba"

"Rana daya kawai tasa min kuka tana son tafiya. Tun ina bata hakuri na gaji da kaina na mayar da ita"

Gambo tace "Mawaddan? Ni duk cikin yaran da nake kawowa ma ai tafi sauran hankali. Tasan cewa zan dawo na tafi da ita da kaina. Dama yau karfin zuwan nawa zanyi miki maganar bikinta ne da ya matso. Shine nace gara na fada ko zaki nemi wata. Ita idan nazo na kaita hutun sallah bazata dawo ba"

"Ni na hakura ma da masu aiki hakanan Gambo. Aikin nawa yake gida sai mu uku"

"Haba Hajiya da kanki"

"Ai dole, Gambo bazan boye miki ba Mawadda ta bani mamaki. Ta difga min sata ta ban mamaki shiyasa ta dage zata tafi"

Ran Gambo kuwa ya baci. Ta saba da ace ta kawo yarinya tayi sata amma batayi zaton haka daga Mawadda ba.

"Hajiya kada ki damu nawa ta satar miki? Wallahi da kaina zan dawo miki da kudinki don gidansu zani. Wannan sai su kashe min kasuwa azo ana ganin kamar hadin baki muke dasu"

BB yana kitchen yazo shan ruwa yaji Hajiyarsa tana karya don ta rufa masa asiri. Wata dariyar shakiyanci yayi ya fito falon.
"Hajiyata kenan, Allah Ya barmin ke muci karenmu ba babbaka"

Gambo ta bisu da kallo Haj Mara ta wayance tace ta bar maganar satar ita ta hakura.

Gambo na fita wayar Baba ta kira tunda tana da ita. Duk lokacin da tazo karbar kudin Mawadda da layin take kiransa ta hadasu su gaisa. Ko tasha bata karasa ba ya dauka ta soma fada masa abinda Haj Mara tace.

"Ince ko Kano zaki sauka idan kin taho."

"Eh dama gobe nayi niyar zuwa Tariwa din"

"To ki daure ki shigo asibitin Malam sai ki kirani"

Daga haka ya kashe wayar ya barta da mamaki. A tashar unguwa uku ta sauka ta wuce gidanta da niyar gobe zata je asibitin tunda dare yayi.
******

Haj Mara tun zuwan Gambo hankalinta ya kasa kwanciya. Matar nan dai tasan gidanta. Idan ta dawo tare da iyayen Mawadda fa yaya zata yi?

Alh Sule har ya fuskanci tana cikin damuwa yayi kwafa.

"Tun ba'aje ko ina ba kin fara zurfafa a tunani akan barnar da yaron nan yake yi ko? To kadan ma kika gani. Ina me tabbatar miki idan bazaki kaini gidan iyayenta mu gyara lamarin nan ba to ki tanadi abin tarar hawaye nan gaba"

Ya gaji da magiya harda barazanar saki duka a banza tace bazata kaishi gidansu Mawadda ba.

Tsoron dawowar Gambo yasa ta dauki waya bayan ya fita daga dakin ta kira kawarta.

Saita muryarta tayi tamkar babu komai kafin ta soma magana da aka dauka
" 'yar boko matar dan boko"

Dr Tani tayi dariya
" 'yar kasuwa matar dan kasuwa jiya ina ta nemanki waya a kashe. Ya ya mutan gida"

Dan barkwanci da tsokanar juna suka taba irin na kawayen da suka tashi tare. Sai kuma Haj Mara ta tattaro nutsuwarta.

"Tani kwana biyu ina ta tunani nace bari dai na fada miki naji ra'ayinki. Cewa nayi me zai hana in turo Babawo yazo su daidaita da kanwarsa Qareeba?"

A zahirin gaskiya Dr. Tani bata da burin 'yarta tayi auren nesa saboda zaman su Haj Mara a Kaduna. To amma ta gaji da gorin dangin miji gashi Qareeban duk gayunta samari basa dadewa ta rasa dalili. Shekara ashirin da biyar gara tayi aure ko zata huta da surutu.

"Amma kinyi tunani mai kyau Marakisiyya na amince. Zanyi magana da Daddynsu sai na fada miki yadda muka yi"

Ajiyar zuciya Haj Mara tayi. Gara Babawo yayi aure kila zata sami saukin wannan bibiyar matan da yake yi.
******

Da kwatancen da Baba yake mata Gambo ta iso dakin da aka kwantar da Mawadda. Kafin tayi tambayar me suke a nan Yaya ta labarta mata komai. Idanunta jazur saboda kuka da takaicin rainin wayon da Haj Mara tayi mata jiya tace da zasu bata hadin kai da an kaisu kotu.

Iya tayi dariya "Allah nagode maKa na sami mai goya min baya. Mun yarda mun amince don ko wadannan basa so..." ta nuna su Baba "ni bazan yafe ba."

Sake kallon Mawadda tayi taji kamar ita ta jawo mata da bata tsananta bincike akan gidan ba. Ji yadda ya sabauta musu yarinya ta fada kumatu ba tsoka sai hakwara gayau da idanu.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰7

*Batul Mamman*💖

Bayan Sati Daya

Aikin Dahiru a gidan Dr. Tani ya kankama kuma Alhamdulillah komai yana tafiya daidai. Matsalarsa daya ce a gidan Qareeba wadda ta zame masa tamkar horror. Ta matsa masa sosai duk wani motsinsa abin tsokana ne a wurinta. Ta kai ta kawo idan yaji muryarta gabansa har faduwa yake saboda bai san me zata ce masa ba.

Yau ta kama litinin dama tun jiya ya sanar cewa yana da uzurin da zai sa bazai sami damar zuwa da wuri ba. Asibitin makaranta suka je inda akayi masa gwaje-gwaje na sanin yanayin lafiyarsa kamar yadda makarantu suke bukata. Yana gamawa ya wuce wurin aikinsa ko gidan Bilya bai koma ba. Ga rana ga yunwa don bai ci komai ba ya fita.

Sanye yake da koriyar t-shirt da dogon wandonsa ruwan dorawa mai duhu sai farin canbas din da yake ji dashi. Yayi kyau abinsa daidai da kwalliyarsa.

Tunda ya fara aikin maigadi ya bashi shawarar ya ware kaya daya da zai rinka amfani dasu kada ya kashe suturunsa a bawa filawa ruwa da su shara. Kafin ya tafi jiya ya wanke su ya shanya a bayan gidan inda igiyoyin shanyar suke. Yana isowa hanyar bayan yayi domin dauko su.

Ta cikin falo Qareeba ta hango shi yana tafiya da sauri ta dawo bakin taga inda zata ganshi sosai.

Dariya yaji an saka ya dan cije lebe. Yau ya shiga uku kuma ko da me tazo.

Kayansa ne suka bata dariya yaji ta ce

"Ahirin irin wannan gayu haka. Gaskiya ka burge maza enyee."

Ta zuge labulen tana kallonsa sosai bayan ta bude tagar. Shi kuwa kamar ya kwadeta. Cigaba yayi da tafiya kawai sai ta fara masa waka harda tafi.

" Gayu, gayu Ahirin on top, gayu, gayu Dashiru on top"

Abin ya sosa masa rai fiye da zato saboda dariya akwai cin rai ga yunwa. Karasawa yayi ya kwaso kayansa tana ta shirmen wakarta. Sai da yazo daidai tagar zai wuce ya daga hannu ya yi mata dakuwa.

Zaro idanu tayi ta nuna kanta "Ni?"

Ya gyada kai tare da harararta ya wuce. Bai ko karasa gaban gidan ba yaji Dr. Tani tana kiransa. Hankali kwance ya nufi bakin kofar shiga gidan don a tunaninsa aiki zata saka shi. Yana tsaye a gefe ta fito. Ko gaisuwar da yake mata bata amsa ba ta soma fada.
Chapter 15 · 0% Book details