Sashe 25
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Durkushewa tayi a wurin tana kuka Alkali yace 'yan sanda suyi waje da ita ko ya hukunta ta saboda dakatar da shari'a batare da izini ba. Suna kokarin kamata Iya da Innar Fatihu suka taso suma suka rikota kowa cikinsu na kuka suka fitar da ita waje. Mawadda kamar ta hadiye zuciya ba kuka sai ajiyar zuciya.
Barista Shafa'atu tace ta gama tambayoyinta domin tun da fari yarda da itan yasa ta dada nanatawa kotu cewa likita ce da ya kamata a kama maganarta saboda dadewarta a aiki da kwazo.
Barista Dalhatu ya taso yazo gabanta kana ganinsa yana cike da nishadi.
"Dr Tani da kika duba Mawadda baki ga wata alama ba kenan dake nuni da cewa anyi mata fyade?"
Tunawa tayi da raunukan jikin Mawadda ta dan runtse ido. Ta tabbatar Haj Mara bazata yi mata karya ba amintarsu tun kuruciya. Idan an gama case din ya kamata iyayen Mawadda su tsareta ta fadi gaskiya waye yayi mata fyade.
"Abu daya na gani shine yarinyar ba budurwa bace"
Yaya sai kuka ta rike hannun Mawadda tana matsawa.
"My lord ina fata kotu taji bayani mai gamsarwa daga bakin shaidar da masu kawo kara suka kawo. Ta yiwu da gaske fyade aka yiwa Mawadda amma ba BB bane saboda bayanin da suka yi shi da mahaifiyarsa da rashin wata shaida da zata karyata hakan. Haka zalika duk inda ake tunanin samun Na'ibi mai kiyos abu ya gagara mutane da dama sunce ko garinsu ba'a sani ba. Da wannan nake rokon kotu da ta taimaka ta yiwa Babawo Sule adalci" dan dukar da kai yayi ya koma ya zauna.
Alkali yace ko Barista Shafa'atu tana da karin bayani ta kalli Mawadda ta girgiza kai.
Ya duka yana kallon takardunsa yace ga hukuncin da kotu ta yanke bayan dan jawabi
"Duba da rashin kwararan shaidu daga bangaren masu korafi da kuma bayanan likita wannan kotu mai alfarma ta kori wannan kara, ta wanke Babawo Sule daga zargin da ake yi masa sannan ta ci Mawadda tarar naira dubu ashirin da biyar bisa dalilin bata masa suna. Wanda bai gamsu da wannan hukunci ba yana da damar daukaka kara."
Yana gamawa ya buga gudumarsa ya mike sannan kowa ya tashi ya fita ta baya.
Yaya tayi tayi ta daga Mawadda daga wurin da take zaune ta kasa saboda mutuwar zaune da tayi. Barista ta matso kusa dasu
"Kuyi hakuri zamu iya daukaka kara sai mu karo shaidu. Kunga tun da farko bakuyi min bayanin asibitin Bebeji da ta fara kwanciya ba da tuni munje har can saboda karin shaida "
Mal Fatihu ya tashi yana murmushin da yafi kuka ciwo yace "Barista mungode a haka ma."
Zata sake magana ya je gaban Mawadda ya tayar da ita har lokacin murmushi yake yi mata "Ni nasan wa na haifa kinji ko, idan duniya zata taru ta nuna miki yatsa maganarki kadai zan dauka. Shari'a kuma mu barta haka zuwa lokacin da zamu taru a gaban Sarkin da Ya halicci kowa da komai"
Da haka ya samu ta tashi zuciyarta tana wani irin bugu da sauri da sauri. Suna fitowa waje aka yanyamesu da tambayoyi ga mutane kowa na fadin abinda yazo bakinsa.
Su Iya sun taso da sauri su tarar dasu Baba yana kare Mawadda daga 'yan jarida. Yaja hannunta suyi gaba kawai ya yanke jiki ya fadi ita kuma tayi kansa saboda rashin kwarin jikinta a wannan lokacin da kuma rikon da yayi mata ta kwala ihu "BABA....!!!!"
[08/01 8:32 pm] : *GUMIN HALAK...*💰11
*Batul Mamman*💖
Yau su Mal.Fatihu zasu bar kauyensu, mahaifarsu kuma tushensu. Tuni sun gama hada kayansu da ba wani yawa garesu. Da wuri Yaya ta fita ta tafi sallama da 'yan uwanta wanda a gidanta suka yini a jiya.
Ade dasu Iya suka zo gidan domin tare zasu tafi har Innar Fatihu. Idan sun taimaka musu sun nutsu a gidan su dawo duk da Ade ma tasan zaman kauyen yanzu yafi karfinta. Aiki zata bazama nema ko don samun lafiyar Mawadda dake fama da digar fitsari har yanzu.
Kowa na can ana tarkata kaya Ade na zaune kan kujerar girki Baba yana daga kan tabarma yace mata
"Sa'ade ina fata zaki yafe min tura Mawadda aiki da nayi har hakan ta faru"
"Haba Yaya me ya kawo wannan zancen kuma? Ka barmu muji da bakincikin mutan garin nan na yanzu"
Gyara zama yaso yi hularsa ta fado. Dora masa ita Ade tayi akan hannunsa mai lafiya ya danyi murmushi
"Kinga fa naso shiga layin zaurawanki ashe ba rabo na koma rabin mutum"
Mawadda na fitowa daga daki taji abinda ya fada kunya ta kamata ta koma da sauri. Ade kuwa dariya tasa don ta kara kwantar masa da hankali tace "ko zaka fito ne?"
Shima yayi dariya "rufa min asiri kada Iya ta cinyeni danye."
Iya na jinsu ashe da ga dakin da Mawadda ta koma. Murmushi tayi sannan hawaye ya sauko mata duk kuwa da dakiya irin ta ta.
"Ehem, ehemmmm....gafarar ku dai masu yi da mutane da rana tsaka. Muna jinku daga ciki ana shuka a idon makwarwa"
Ade mikewa tayi da sauri ta bar wurin don kunya shi kuma Baba ya dauki hularsa ya rufe fuska. Iya tayi 'yar dariya ta wucesu.
Sai da suka yi sallar azahar aka fara batun nemo mota daga bakin titi. Nan fa sai koke-koke yawanci daga 'ya'yansu ne ma saboda Baba yace bai yarda su biyosu a yau ba. Baya so suyi abinda suma nasu auren zai gurgunce irin na Jamila. Sun hakura tare da alkawarin zuwa kafin suyi sati. A haka Malam kakansu yazo ya riskesu an soma fita da kaya waje. Baba na ganinsa yaji kwalla ta taho masa.
"Meye hakan Fatihu a gaban 'ya'ya da jikoki" cewar tsohon mai halin dattako cike da dauriya. Ba karamin tashin hankali ya shiga ba sakamakon abubuwan da ke faruwa da iyalin dan nasa amma ya yarda jarabawa ce mai wucewa.
"Malam ka yafe min duk wani abu da na taba yi maka da gangan ko bisa kuskure."
Malam ya dafa masa kafada "Allah Ya baka lafiya Fatihu Yasa wannan tafiya ta zama tamkar budewar wani *sabon shafi* na rayuwarku. Bansan lokacin da zamu sake haduwa ba ni ga tsufa ga lalurar kafa da ido. Kai kuma ga yadda Allah Yayi da kai sannan Maigari yace yafi son ka bawa garin nan iska har abin ya lafa"
Nasiha yayi ta musu akan rike mutumcinsu idan sunje birni kada son abin duniya ya rudesu.
*****
Danlami ya shigo gidansu da sauri ya tari Inna a kofar dakin Baffa yana faman haki.
"Inna tafiyar fa tazo har an samo a kori kura sun fara lodin kayansu"
Juyawa tayi ta sanar da Baffa sai ta ga har ya fito shima. Kwanansa uku yana son zuwa yiwa su Mal Fatihu sallama amma tsananin kunya ya hana. Inna ce tace ya kamata su ajiye komai suje kada ayi rabuwa ba ta arziki ba. Rashin yardarsu da auren yaran suna ganin ko wasu ne da wuya su amince.
Mayafi ta sako Baffa yasa hula suka je gidan. An fito da Baba kenan za'a saka shi a mota. Mukullin sabon gidan nasu Maigari ya bawa kanin Mal Fatihu dreba shine zaiyi musu jagora an nuna masa gidan.
Baffa yana jin nauyi haka ya matsa jikin motar suka gaisa da Baba. Inna ma haka yayi suka gaisa dasu Yaya kowa yana kokarin boye abinda ke ransa. Idan ka cire 'yan uwa na jini su Inna ne kadai suka zo yi musu sallama. Inna ta kawo wani madaidaicin buhu da Danlami ya biyota dashi tace gashi ba yawa. Ledoji uku ne a cikinsa daya shinkafa, daya wake dayan kuma waken soya. Sun rabu su Bilki suna ta kuka a gefe ma Inna sai da tayi nata na tausayin wannan iyali.
******
*KANO TA DABO TUMBIN GIWA*
Sati biyu kenan da dawowarsu Kano. Gidan ba laifi yana da fadi fiye da tsammaninsu. Kuma banda dakuna uku na ciki akwai wani a soro shi aka barwa Marwanu da Saifullahi 'ya'ya biyu maza da Mal Fatihu yake dasu 'yan kasa da shekara shabiyar. Jamila, Mawadda da kanwarsu mai binta Rafi'a an basu daki daya su ma. Dayan kuma na Baba ne yayin da Ade dasu Iya suke cikin na Yaya.
Iya da Inna kwanansu biyar suka koma sai dai Malam ya matsa Iya ta dawo saboda hankalinsa bai kwanta ba. Ga bakunta ga maigida a kwance suna bukatar sa ido na babba. To dayake abubuwa da dama sun faru ko kadan da ta dawo babu wannan rigimar ta matsawa Yaya. Ita kanta tasan Yaya mai kaunar jininta ce shiyasa yanzu take kokarin rike girmanta. Ade kuma ta sami aiki gidan wani tsohon minista a rijiyar zaki da gudu ta karba don tasan banda 'ya'yanta da take biyawa kudin makaranta dole ta nemi kudi saboda Mawadda.
Wata rana suna zaune ana cin dumame Mawadda tace "Yaya wai bazamu fara sana'a bane?"
"Nima tunanin da nake kwana dashi kenan amma na rasa me zamuyi"
Jamila da take gwanar kitso tace anjima idan sun shiga gaisawa da sauran makotan da basu sami damar shigarwa ba zasu sanar dasu ana kitso a gidan.
Da wannan shawarar suka fita. Gidaje uku suka shiga. Dayan da yake da 'yar tazara dasu harda gate mai kyau dashi. Sun shiga sun sami matar tana hada garwashi a bayan gidan da danta ya kaisu. Gefe ga mace ta lullube da bargo fuskarta tayi yelo. Tana aikin suna gaisawa tace suyi hakuri bata shigo ba aikin amaryar nan ne ya tsayar da ita. Hankalin Mawadda kacokan yana gareta tana kallo ta zuba wani turare a kasko wurin ya bade da kamshi ta daga bargon ta tura kaskon sannan ta sake lullube yarinyar.
Mawadda ta kasa hakuri ta tambayeta me take yi haka.
Murmushi tayi "gyaran jiki ne na amare da matan aure ko kina so?"
A kunyace Mawadda tace a'a sai dai fa da kyar ta tashi suka bar gidan. Komai ta ga matar tayi burgeta yake. A kwaba wannan a kwaba wancan ance duk amarya za'a shafawa jikinta yayi kyau. Matar kanta mai suna Zahra ta kula da yadda Mawadda ke kallonta ita kuwa ba gajiyawa kome tayi sai tayi mata bayani.
Barista Shafa'atu tace ta gama tambayoyinta domin tun da fari yarda da itan yasa ta dada nanatawa kotu cewa likita ce da ya kamata a kama maganarta saboda dadewarta a aiki da kwazo.
Barista Dalhatu ya taso yazo gabanta kana ganinsa yana cike da nishadi.
"Dr Tani da kika duba Mawadda baki ga wata alama ba kenan dake nuni da cewa anyi mata fyade?"
Tunawa tayi da raunukan jikin Mawadda ta dan runtse ido. Ta tabbatar Haj Mara bazata yi mata karya ba amintarsu tun kuruciya. Idan an gama case din ya kamata iyayen Mawadda su tsareta ta fadi gaskiya waye yayi mata fyade.
"Abu daya na gani shine yarinyar ba budurwa bace"
Yaya sai kuka ta rike hannun Mawadda tana matsawa.
"My lord ina fata kotu taji bayani mai gamsarwa daga bakin shaidar da masu kawo kara suka kawo. Ta yiwu da gaske fyade aka yiwa Mawadda amma ba BB bane saboda bayanin da suka yi shi da mahaifiyarsa da rashin wata shaida da zata karyata hakan. Haka zalika duk inda ake tunanin samun Na'ibi mai kiyos abu ya gagara mutane da dama sunce ko garinsu ba'a sani ba. Da wannan nake rokon kotu da ta taimaka ta yiwa Babawo Sule adalci" dan dukar da kai yayi ya koma ya zauna.
Alkali yace ko Barista Shafa'atu tana da karin bayani ta kalli Mawadda ta girgiza kai.
Ya duka yana kallon takardunsa yace ga hukuncin da kotu ta yanke bayan dan jawabi
"Duba da rashin kwararan shaidu daga bangaren masu korafi da kuma bayanan likita wannan kotu mai alfarma ta kori wannan kara, ta wanke Babawo Sule daga zargin da ake yi masa sannan ta ci Mawadda tarar naira dubu ashirin da biyar bisa dalilin bata masa suna. Wanda bai gamsu da wannan hukunci ba yana da damar daukaka kara."
Yana gamawa ya buga gudumarsa ya mike sannan kowa ya tashi ya fita ta baya.
Yaya tayi tayi ta daga Mawadda daga wurin da take zaune ta kasa saboda mutuwar zaune da tayi. Barista ta matso kusa dasu
"Kuyi hakuri zamu iya daukaka kara sai mu karo shaidu. Kunga tun da farko bakuyi min bayanin asibitin Bebeji da ta fara kwanciya ba da tuni munje har can saboda karin shaida "
Mal Fatihu ya tashi yana murmushin da yafi kuka ciwo yace "Barista mungode a haka ma."
Zata sake magana ya je gaban Mawadda ya tayar da ita har lokacin murmushi yake yi mata "Ni nasan wa na haifa kinji ko, idan duniya zata taru ta nuna miki yatsa maganarki kadai zan dauka. Shari'a kuma mu barta haka zuwa lokacin da zamu taru a gaban Sarkin da Ya halicci kowa da komai"
Da haka ya samu ta tashi zuciyarta tana wani irin bugu da sauri da sauri. Suna fitowa waje aka yanyamesu da tambayoyi ga mutane kowa na fadin abinda yazo bakinsa.
Su Iya sun taso da sauri su tarar dasu Baba yana kare Mawadda daga 'yan jarida. Yaja hannunta suyi gaba kawai ya yanke jiki ya fadi ita kuma tayi kansa saboda rashin kwarin jikinta a wannan lokacin da kuma rikon da yayi mata ta kwala ihu "BABA....!!!!"
[08/01 8:32 pm] : *GUMIN HALAK...*💰11
*Batul Mamman*💖
Yau su Mal.Fatihu zasu bar kauyensu, mahaifarsu kuma tushensu. Tuni sun gama hada kayansu da ba wani yawa garesu. Da wuri Yaya ta fita ta tafi sallama da 'yan uwanta wanda a gidanta suka yini a jiya.
Ade dasu Iya suka zo gidan domin tare zasu tafi har Innar Fatihu. Idan sun taimaka musu sun nutsu a gidan su dawo duk da Ade ma tasan zaman kauyen yanzu yafi karfinta. Aiki zata bazama nema ko don samun lafiyar Mawadda dake fama da digar fitsari har yanzu.
Kowa na can ana tarkata kaya Ade na zaune kan kujerar girki Baba yana daga kan tabarma yace mata
"Sa'ade ina fata zaki yafe min tura Mawadda aiki da nayi har hakan ta faru"
"Haba Yaya me ya kawo wannan zancen kuma? Ka barmu muji da bakincikin mutan garin nan na yanzu"
Gyara zama yaso yi hularsa ta fado. Dora masa ita Ade tayi akan hannunsa mai lafiya ya danyi murmushi
"Kinga fa naso shiga layin zaurawanki ashe ba rabo na koma rabin mutum"
Mawadda na fitowa daga daki taji abinda ya fada kunya ta kamata ta koma da sauri. Ade kuwa dariya tasa don ta kara kwantar masa da hankali tace "ko zaka fito ne?"
Shima yayi dariya "rufa min asiri kada Iya ta cinyeni danye."
Iya na jinsu ashe da ga dakin da Mawadda ta koma. Murmushi tayi sannan hawaye ya sauko mata duk kuwa da dakiya irin ta ta.
"Ehem, ehemmmm....gafarar ku dai masu yi da mutane da rana tsaka. Muna jinku daga ciki ana shuka a idon makwarwa"
Ade mikewa tayi da sauri ta bar wurin don kunya shi kuma Baba ya dauki hularsa ya rufe fuska. Iya tayi 'yar dariya ta wucesu.
Sai da suka yi sallar azahar aka fara batun nemo mota daga bakin titi. Nan fa sai koke-koke yawanci daga 'ya'yansu ne ma saboda Baba yace bai yarda su biyosu a yau ba. Baya so suyi abinda suma nasu auren zai gurgunce irin na Jamila. Sun hakura tare da alkawarin zuwa kafin suyi sati. A haka Malam kakansu yazo ya riskesu an soma fita da kaya waje. Baba na ganinsa yaji kwalla ta taho masa.
"Meye hakan Fatihu a gaban 'ya'ya da jikoki" cewar tsohon mai halin dattako cike da dauriya. Ba karamin tashin hankali ya shiga ba sakamakon abubuwan da ke faruwa da iyalin dan nasa amma ya yarda jarabawa ce mai wucewa.
"Malam ka yafe min duk wani abu da na taba yi maka da gangan ko bisa kuskure."
Malam ya dafa masa kafada "Allah Ya baka lafiya Fatihu Yasa wannan tafiya ta zama tamkar budewar wani *sabon shafi* na rayuwarku. Bansan lokacin da zamu sake haduwa ba ni ga tsufa ga lalurar kafa da ido. Kai kuma ga yadda Allah Yayi da kai sannan Maigari yace yafi son ka bawa garin nan iska har abin ya lafa"
Nasiha yayi ta musu akan rike mutumcinsu idan sunje birni kada son abin duniya ya rudesu.
*****
Danlami ya shigo gidansu da sauri ya tari Inna a kofar dakin Baffa yana faman haki.
"Inna tafiyar fa tazo har an samo a kori kura sun fara lodin kayansu"
Juyawa tayi ta sanar da Baffa sai ta ga har ya fito shima. Kwanansa uku yana son zuwa yiwa su Mal Fatihu sallama amma tsananin kunya ya hana. Inna ce tace ya kamata su ajiye komai suje kada ayi rabuwa ba ta arziki ba. Rashin yardarsu da auren yaran suna ganin ko wasu ne da wuya su amince.
Mayafi ta sako Baffa yasa hula suka je gidan. An fito da Baba kenan za'a saka shi a mota. Mukullin sabon gidan nasu Maigari ya bawa kanin Mal Fatihu dreba shine zaiyi musu jagora an nuna masa gidan.
Baffa yana jin nauyi haka ya matsa jikin motar suka gaisa da Baba. Inna ma haka yayi suka gaisa dasu Yaya kowa yana kokarin boye abinda ke ransa. Idan ka cire 'yan uwa na jini su Inna ne kadai suka zo yi musu sallama. Inna ta kawo wani madaidaicin buhu da Danlami ya biyota dashi tace gashi ba yawa. Ledoji uku ne a cikinsa daya shinkafa, daya wake dayan kuma waken soya. Sun rabu su Bilki suna ta kuka a gefe ma Inna sai da tayi nata na tausayin wannan iyali.
******
*KANO TA DABO TUMBIN GIWA*
Sati biyu kenan da dawowarsu Kano. Gidan ba laifi yana da fadi fiye da tsammaninsu. Kuma banda dakuna uku na ciki akwai wani a soro shi aka barwa Marwanu da Saifullahi 'ya'ya biyu maza da Mal Fatihu yake dasu 'yan kasa da shekara shabiyar. Jamila, Mawadda da kanwarsu mai binta Rafi'a an basu daki daya su ma. Dayan kuma na Baba ne yayin da Ade dasu Iya suke cikin na Yaya.
Iya da Inna kwanansu biyar suka koma sai dai Malam ya matsa Iya ta dawo saboda hankalinsa bai kwanta ba. Ga bakunta ga maigida a kwance suna bukatar sa ido na babba. To dayake abubuwa da dama sun faru ko kadan da ta dawo babu wannan rigimar ta matsawa Yaya. Ita kanta tasan Yaya mai kaunar jininta ce shiyasa yanzu take kokarin rike girmanta. Ade kuma ta sami aiki gidan wani tsohon minista a rijiyar zaki da gudu ta karba don tasan banda 'ya'yanta da take biyawa kudin makaranta dole ta nemi kudi saboda Mawadda.
Wata rana suna zaune ana cin dumame Mawadda tace "Yaya wai bazamu fara sana'a bane?"
"Nima tunanin da nake kwana dashi kenan amma na rasa me zamuyi"
Jamila da take gwanar kitso tace anjima idan sun shiga gaisawa da sauran makotan da basu sami damar shigarwa ba zasu sanar dasu ana kitso a gidan.
Da wannan shawarar suka fita. Gidaje uku suka shiga. Dayan da yake da 'yar tazara dasu harda gate mai kyau dashi. Sun shiga sun sami matar tana hada garwashi a bayan gidan da danta ya kaisu. Gefe ga mace ta lullube da bargo fuskarta tayi yelo. Tana aikin suna gaisawa tace suyi hakuri bata shigo ba aikin amaryar nan ne ya tsayar da ita. Hankalin Mawadda kacokan yana gareta tana kallo ta zuba wani turare a kasko wurin ya bade da kamshi ta daga bargon ta tura kaskon sannan ta sake lullube yarinyar.
Mawadda ta kasa hakuri ta tambayeta me take yi haka.
Murmushi tayi "gyaran jiki ne na amare da matan aure ko kina so?"
A kunyace Mawadda tace a'a sai dai fa da kyar ta tashi suka bar gidan. Komai ta ga matar tayi burgeta yake. A kwaba wannan a kwaba wancan ance duk amarya za'a shafawa jikinta yayi kyau. Matar kanta mai suna Zahra ta kula da yadda Mawadda ke kallonta ita kuwa ba gajiyawa kome tayi sai tayi mata bayani.