Sashe 6
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BB ne ya rike mata hannu zata sake dukanta "Hajiya bata motsi fa. Ba dai kin kashe musu 'ya ba. Ni dai babu ruwana da ranta na barta"
Sai a lokacin ta kula bakin Mawadda a daure yake ta yaye bargon ba shiri ta kawar da kai.
"Auzubillah Babawo ka jawo min masifa. Fyade kayiwa 'yar mutane?"
Mawaddan ya kalla wadda azaba taci karfinta tsoro ya kamashi kada ta mutu.
"To ai kece Hajiya nasan da cewa nayi ina son aurenta bazaki yarda ba"
Tashi tayi tana kuka tayi kansa da duka "fita dan ubanka....na shiga uku na."
Da kyar ta tallafi Mawadda ta dagata zaune ta ma rasa me ya kamata tayi mata kuma. Hannunta da kyar ya iya zaro waya a jakarta ta kira maigidanta Alh Sule Chanji. Yana can Lagos inda harkokin nasa suka fi karfi. Ko da ta fara masa bayani ba karamin tashin hankali ya shiga ba. Fada ya soma yi mata kamar ita tayi sannan yace a kai yarinyar asibiti yana nan tafe ranar laraba.
Haj Mara ta amsa har ta sakawa Mawadda kaya wata zuciyar ta kwabeta akan tonawa kanta da gidanta asiri. Dammara taci da mayafinta dankwali kuwa bata san inda ya fadi ba ta tafi dakinta ta debo ruwan zafi bokiti uku. Ita kadai take ta hawa da sauka bene BB ya fice ma bata san inda yayi ba. Haka ta zage ta soma yi mata wanka sai dai tana soma jin kwari a sanyaye tace zata iya.
Fita Hajiyan tayi tana ta kai kawo a dakin har Mawadda ta fito tana bin bango. Sai a lokacin ta tuna yadda ta rinka rokonta akan zuwa gida. Data sani ta barta da haka bai faru ba.
Ganin Hajiya a dakin yasa ta saki wani irin kuka mai shiga rai. Haj Mara ta riko hannunta zata zaunar da ita akan katifar ta zabura ta fice daga dakin da sauri. Ko zata mutu babu ita ba wannam bakin daki da ya kafa mummunan tarihi a rayuwarta balle kuma katifar.
A korido Hajiya ta ganta ta kama hannunta batare da tayi magana ba ta kaita nata dakin a sama. Daga cikin kayanta ta dauko mata doguwar riga wadda fadin ne kawai yayi mata yawa saboda Haj Mara ba tsayi gareta ba. Bayan nan ta bata shayi da maganin ciwon jiki tasha bisa tursasawa. Sai da ta dan nutsu Haj Mara ta soma magana.
"Mawadda kiyi hakuri akan abinda Babawo yayi miki kuma don Allah ki rufa maganar nan kada kowa yaji "
Batayi mamakin furucin Hajiyar ba saboda ta dade da gane mutane suna da son kai.
"Hajiya ki kaini asibiti don Allah" kuka ne ya taso mata mai karfi.
"Idan muka je asibiti kama Babawo za'ayi a kulle ki taimaka kiyi hakuri zan baki magani" Dole ta lallabata kada ta janyo musu bacin suna.
"nasan aure zakiyi kwanannan shiyasa zan baki kudi sosai saboda hidimar bikin naki. Kina samun sauki ko zuwa jibi ne zan mayar dake gida. Maganar nake so ta mutu kawai. Babawo shi kadai ne dana namiji kuma ya sami aiki a babban kamfani bana son abinda zai shafi mutumcinsa"
Yanzu kam tayi mamaki tunda son kai yasa an nuna mata ita nata mutumcin ba abin dubawa bane. Wani irin kallo tabi Hajiyar dashi musamman da taji tana waya da mijinta tana sanar dashi ai suna asibiti har an basu gado. Ransa duk a bace yace kada ta bari Babawo ya sake fita don har garinsu yarinyar sai sunje ta bishi da to kamar gaske.
Ranar Mawadda a dakin ta kwana da mugun zazzabi da ciwon kai bacci ma kasawa tayi. Ko yaya ta rufe ido Babawo take gani ga ciwo ko tafiya bata iyawa sai ta dafa bango amma anki kaita asibiti.
Da safe data tashi fuskarta duk ta kumbura lebe yayi suntum saboda buguwa ashe ya fashe ta ciki. Hajiya da kanta tayi komai Mawadda tana jinsu da da BB tana masa fadan yana son bata musu suna. Haka ta wuni a daki tana kuka Hajiya na kawo mata abinci da panadol wai maganin rage ciwo ne.
Bayan kwana biyu ana gobe Alhaji zai dawo Hajiya ta shigo gidan da sassafe da kaya niki-niki cikin ghana must go biyu manya tasa Mawadda ta sakko daga sama da mayafinta.
Kayan ta nuna mata wai na yaranta ne mata biyu masu aure da na yaransu gashi nan ta kai gida tsaraba. Sai wata jaka ita kuma sababbin kaya ne atamfofi da shadda harda leshi wai tayi fitar biki. Sai kuma kudi dubu ashirin ta dora mata a hannu.
"Mawadda"
Idonta da baya rabo da hawaye yanzu ta dago tare da amsawa. Kana ganinta kasan a tsorace take gani take kamar BB zai shigo. A yanzu ko cokali ne ya fadi sai ta zabura. Ga tafiyarta gabadaya ta canja saboda ciwon da Hajiya taki kaita asibiti balle asan taimakon da ya kamata ayi mata.
Fuska a hade ta cigada da cewa "Yau zan mayar dake garinku. Wannan duk na baki ne ki kai gida magana kuma ta mutu. Wallahi duk ranar da wani naki yazo min da zancen abinda ya faru tsakaninki da Babawo zan sanar dasu bin maza kike yi shiyasa na gaji na dawo dake. Ke da duka garinku bana jin zaku iya rigima dani don bani da mutumci ke shaida ce. Ki kama bakinki sawunki a likkafa kiyi shiru kawai. Zan iya sawa azo har gida a harbeki da iyayenki kinsan kanina soja ne kin sha ganinsa a gidan nan da bindiga"
Zuciyar Mawadda ta tsinke da lamarin Hajiya sai tsoro da ya shigeta. Ita wa ma zata fadawa balle azo ayi yunkurin kashesu har gida. Don har ranta ta yarda Hajiyan zata iya. Ko a garinsu da aka taba yiwa wata irin haka kowa tsanarta yayi bata mantawa ga kyama ita da iyaye. Karshe ma dai barin garin sukayi cikin dare.
Haj Mara ta karance ta tsaf tasan ta dana mata dafi zata rufa musu asiri. Kawarta daya ta fadawa wadda ta bata shawarar ta tattara ta kaita gida kafin mijinta ya dawo don ba karamin aikinsa bane yace sai Babawo ya aureta.
Haka ta tashi suka fita tana ta kukan rashin sanin abinyi. Waye zai kwatar mata 'yanci? Yaya rayuwarta zata kasance? Shin laifi ne don mutum yazo neman halak da guminsa saboda talauci???
A hanya ma haka ta sakata ta rufe fuska da habar hijabin wai kada a gane me ya sameta. Idan an matsa mata da tambaya tace faduwa tayi. Bata ma iya tankawa ba saboda azabar ciwon kai da fargabar haduwa da iyayenta.
*******
Kauyen Tariwa-Bebeji LG
Zaune yake a karkashin katuwar bishiyar kukar da take kusan a tsakiyar gonar mahaifinsa yana shan farau-farau ya hango kaninsa Danlami a guje har yana tuntube da fatanya garin sauri.
"Assha Danlami meye haka kake gudu kamar kaga kura?" Cewar Dahiru bayan ya dangwarar da tasar hannunsa ya taimaka masa ya mike tsaye.
Sai da ya gama kade farar jamfarsa da ta rine zuwa ruwan kasa saboda wahala da gumi sannan ya dubi yayansa yana murmushi.
"Albishirinka, amma dai muyita da wajewa zaka bani aron wannan yadin naka ruwan kasa da ka dinka da sallah karama idan zamu je Kano dasu Samaila kallon hawa"
Dahiru ya girgiza
"Sannu shugaban 'yan son banza, cha nake tare akayi mana dinkin"
"Amma dai kala daban ne ka sani. Nawa dashi naje kallon da karamar sallah yanzu ma sai na sake zuwa dashi saboda nemawa kai raini"
Dahiru yasan halin kaninsa sosai. Tunda ya fara wannan rokon tabbas labari mai dadi ya kawo masa. Murmushi ne ya subuce masa da zuciyarsa ta harbo jirgin inda ya kwasa a guje har yana kifar da sauran farau-farau dinsa. Danlami a tsorace ya bishi shima don yayi zaton ko macizan da suka addabi gonar ne wani ya fito.
Sai da suka isa wurin mutane Dahiru ya dan nutsu sai farinciki bayyane a fuskarsa.
"Su Danlami sai a dau na damo wannan sallar ma da naka kayan zaka je kallo. Mawadda ce tazo ko ko ba haka ba?"
Danlami ya danyi sakato yana kallonsa kafin ya buga tsaki "yanzu fa sai ka nemi raina min wayo kace jikinka ne ya baka ko? Soyayya manya, to munji labarin Lela Majanu ma ehee. Kuma Qur'anin Allah sai ka bani ko yau na raka ka tadi muga tsiya"
Ko kula shi Dahiru bai sake yi ba ya kara sauri yana dokin ganin sahibarsa Mawadda. Sai dai kuma dole ya bada kayan idan ba haka ba baya jin akwai wanda ya isa ya hana Danlami rakashi tadi. Zuwa zaiyi yayi ta zuba karshe ko gaisuwar kirki bazasu sami damar yi ba. Gashi daga shi har ita ba masu magana bane sosai bare su kore shi. Ba karamin raina shi Danlami yayi ba duk da akwai mace tsakaninsu sai dai akwain shakuwa mai karfi tsakaninsu.
Suna isa gida Innarsu tace ko yunwa ce ta dawo dashi saboda bai karya ba ya fita gona sakamakon ruwan da aka kwana ana yi. Abincinsa tasa kanwarsa mai bin Danlami ta kawo masa ya daga hannu alamun ta barshi.
"Wanka zanyi na fita Inna idan na dawo sai naci"
"Da rana tsaka gagal Dahiru ina zuwa haka ka bari yamma tayi mana"
"Sahibar kokon zuciyarsa ce ta dawo" cewar Danlami yana buga masa harara har lokacin fushin kayan da baya tunanin samu yake ga sallah babba saura kwana goma sha biyar.
Inna ta hau fara'a yau tasan Dahiru zai kwana farinciki. Shi kuwa kunya tasa bai iya cewa komai ba ya shige ya watsa ruwa. Shirt da wando ya zaro a kasan akwati ya saka ya fito fes rike da kanbas din da babban wansu mai aikin kanikanci a cikin Kano ya kawo masa da zai zo.
Yana sakawa ya fito Inna ta washe baki jajayen hakoranta suka bayyana "ka gaishe min da 'yar tawa kaji ko"
"To Inna, ko zan dan sami turaren nan na Baffa ko feshi daya ne kiyi min dan Allah"
"Ai ba sai ka roka ba Danlami miko masa kuma idan ka fesa sai na hadaka da Baffan"
Sai a lokacin ta kula bakin Mawadda a daure yake ta yaye bargon ba shiri ta kawar da kai.
"Auzubillah Babawo ka jawo min masifa. Fyade kayiwa 'yar mutane?"
Mawaddan ya kalla wadda azaba taci karfinta tsoro ya kamashi kada ta mutu.
"To ai kece Hajiya nasan da cewa nayi ina son aurenta bazaki yarda ba"
Tashi tayi tana kuka tayi kansa da duka "fita dan ubanka....na shiga uku na."
Da kyar ta tallafi Mawadda ta dagata zaune ta ma rasa me ya kamata tayi mata kuma. Hannunta da kyar ya iya zaro waya a jakarta ta kira maigidanta Alh Sule Chanji. Yana can Lagos inda harkokin nasa suka fi karfi. Ko da ta fara masa bayani ba karamin tashin hankali ya shiga ba. Fada ya soma yi mata kamar ita tayi sannan yace a kai yarinyar asibiti yana nan tafe ranar laraba.
Haj Mara ta amsa har ta sakawa Mawadda kaya wata zuciyar ta kwabeta akan tonawa kanta da gidanta asiri. Dammara taci da mayafinta dankwali kuwa bata san inda ya fadi ba ta tafi dakinta ta debo ruwan zafi bokiti uku. Ita kadai take ta hawa da sauka bene BB ya fice ma bata san inda yayi ba. Haka ta zage ta soma yi mata wanka sai dai tana soma jin kwari a sanyaye tace zata iya.
Fita Hajiyan tayi tana ta kai kawo a dakin har Mawadda ta fito tana bin bango. Sai a lokacin ta tuna yadda ta rinka rokonta akan zuwa gida. Data sani ta barta da haka bai faru ba.
Ganin Hajiya a dakin yasa ta saki wani irin kuka mai shiga rai. Haj Mara ta riko hannunta zata zaunar da ita akan katifar ta zabura ta fice daga dakin da sauri. Ko zata mutu babu ita ba wannam bakin daki da ya kafa mummunan tarihi a rayuwarta balle kuma katifar.
A korido Hajiya ta ganta ta kama hannunta batare da tayi magana ba ta kaita nata dakin a sama. Daga cikin kayanta ta dauko mata doguwar riga wadda fadin ne kawai yayi mata yawa saboda Haj Mara ba tsayi gareta ba. Bayan nan ta bata shayi da maganin ciwon jiki tasha bisa tursasawa. Sai da ta dan nutsu Haj Mara ta soma magana.
"Mawadda kiyi hakuri akan abinda Babawo yayi miki kuma don Allah ki rufa maganar nan kada kowa yaji "
Batayi mamakin furucin Hajiyar ba saboda ta dade da gane mutane suna da son kai.
"Hajiya ki kaini asibiti don Allah" kuka ne ya taso mata mai karfi.
"Idan muka je asibiti kama Babawo za'ayi a kulle ki taimaka kiyi hakuri zan baki magani" Dole ta lallabata kada ta janyo musu bacin suna.
"nasan aure zakiyi kwanannan shiyasa zan baki kudi sosai saboda hidimar bikin naki. Kina samun sauki ko zuwa jibi ne zan mayar dake gida. Maganar nake so ta mutu kawai. Babawo shi kadai ne dana namiji kuma ya sami aiki a babban kamfani bana son abinda zai shafi mutumcinsa"
Yanzu kam tayi mamaki tunda son kai yasa an nuna mata ita nata mutumcin ba abin dubawa bane. Wani irin kallo tabi Hajiyar dashi musamman da taji tana waya da mijinta tana sanar dashi ai suna asibiti har an basu gado. Ransa duk a bace yace kada ta bari Babawo ya sake fita don har garinsu yarinyar sai sunje ta bishi da to kamar gaske.
Ranar Mawadda a dakin ta kwana da mugun zazzabi da ciwon kai bacci ma kasawa tayi. Ko yaya ta rufe ido Babawo take gani ga ciwo ko tafiya bata iyawa sai ta dafa bango amma anki kaita asibiti.
Da safe data tashi fuskarta duk ta kumbura lebe yayi suntum saboda buguwa ashe ya fashe ta ciki. Hajiya da kanta tayi komai Mawadda tana jinsu da da BB tana masa fadan yana son bata musu suna. Haka ta wuni a daki tana kuka Hajiya na kawo mata abinci da panadol wai maganin rage ciwo ne.
Bayan kwana biyu ana gobe Alhaji zai dawo Hajiya ta shigo gidan da sassafe da kaya niki-niki cikin ghana must go biyu manya tasa Mawadda ta sakko daga sama da mayafinta.
Kayan ta nuna mata wai na yaranta ne mata biyu masu aure da na yaransu gashi nan ta kai gida tsaraba. Sai wata jaka ita kuma sababbin kaya ne atamfofi da shadda harda leshi wai tayi fitar biki. Sai kuma kudi dubu ashirin ta dora mata a hannu.
"Mawadda"
Idonta da baya rabo da hawaye yanzu ta dago tare da amsawa. Kana ganinta kasan a tsorace take gani take kamar BB zai shigo. A yanzu ko cokali ne ya fadi sai ta zabura. Ga tafiyarta gabadaya ta canja saboda ciwon da Hajiya taki kaita asibiti balle asan taimakon da ya kamata ayi mata.
Fuska a hade ta cigada da cewa "Yau zan mayar dake garinku. Wannan duk na baki ne ki kai gida magana kuma ta mutu. Wallahi duk ranar da wani naki yazo min da zancen abinda ya faru tsakaninki da Babawo zan sanar dasu bin maza kike yi shiyasa na gaji na dawo dake. Ke da duka garinku bana jin zaku iya rigima dani don bani da mutumci ke shaida ce. Ki kama bakinki sawunki a likkafa kiyi shiru kawai. Zan iya sawa azo har gida a harbeki da iyayenki kinsan kanina soja ne kin sha ganinsa a gidan nan da bindiga"
Zuciyar Mawadda ta tsinke da lamarin Hajiya sai tsoro da ya shigeta. Ita wa ma zata fadawa balle azo ayi yunkurin kashesu har gida. Don har ranta ta yarda Hajiyan zata iya. Ko a garinsu da aka taba yiwa wata irin haka kowa tsanarta yayi bata mantawa ga kyama ita da iyaye. Karshe ma dai barin garin sukayi cikin dare.
Haj Mara ta karance ta tsaf tasan ta dana mata dafi zata rufa musu asiri. Kawarta daya ta fadawa wadda ta bata shawarar ta tattara ta kaita gida kafin mijinta ya dawo don ba karamin aikinsa bane yace sai Babawo ya aureta.
Haka ta tashi suka fita tana ta kukan rashin sanin abinyi. Waye zai kwatar mata 'yanci? Yaya rayuwarta zata kasance? Shin laifi ne don mutum yazo neman halak da guminsa saboda talauci???
A hanya ma haka ta sakata ta rufe fuska da habar hijabin wai kada a gane me ya sameta. Idan an matsa mata da tambaya tace faduwa tayi. Bata ma iya tankawa ba saboda azabar ciwon kai da fargabar haduwa da iyayenta.
*******
Kauyen Tariwa-Bebeji LG
Zaune yake a karkashin katuwar bishiyar kukar da take kusan a tsakiyar gonar mahaifinsa yana shan farau-farau ya hango kaninsa Danlami a guje har yana tuntube da fatanya garin sauri.
"Assha Danlami meye haka kake gudu kamar kaga kura?" Cewar Dahiru bayan ya dangwarar da tasar hannunsa ya taimaka masa ya mike tsaye.
Sai da ya gama kade farar jamfarsa da ta rine zuwa ruwan kasa saboda wahala da gumi sannan ya dubi yayansa yana murmushi.
"Albishirinka, amma dai muyita da wajewa zaka bani aron wannan yadin naka ruwan kasa da ka dinka da sallah karama idan zamu je Kano dasu Samaila kallon hawa"
Dahiru ya girgiza
"Sannu shugaban 'yan son banza, cha nake tare akayi mana dinkin"
"Amma dai kala daban ne ka sani. Nawa dashi naje kallon da karamar sallah yanzu ma sai na sake zuwa dashi saboda nemawa kai raini"
Dahiru yasan halin kaninsa sosai. Tunda ya fara wannan rokon tabbas labari mai dadi ya kawo masa. Murmushi ne ya subuce masa da zuciyarsa ta harbo jirgin inda ya kwasa a guje har yana kifar da sauran farau-farau dinsa. Danlami a tsorace ya bishi shima don yayi zaton ko macizan da suka addabi gonar ne wani ya fito.
Sai da suka isa wurin mutane Dahiru ya dan nutsu sai farinciki bayyane a fuskarsa.
"Su Danlami sai a dau na damo wannan sallar ma da naka kayan zaka je kallo. Mawadda ce tazo ko ko ba haka ba?"
Danlami ya danyi sakato yana kallonsa kafin ya buga tsaki "yanzu fa sai ka nemi raina min wayo kace jikinka ne ya baka ko? Soyayya manya, to munji labarin Lela Majanu ma ehee. Kuma Qur'anin Allah sai ka bani ko yau na raka ka tadi muga tsiya"
Ko kula shi Dahiru bai sake yi ba ya kara sauri yana dokin ganin sahibarsa Mawadda. Sai dai kuma dole ya bada kayan idan ba haka ba baya jin akwai wanda ya isa ya hana Danlami rakashi tadi. Zuwa zaiyi yayi ta zuba karshe ko gaisuwar kirki bazasu sami damar yi ba. Gashi daga shi har ita ba masu magana bane sosai bare su kore shi. Ba karamin raina shi Danlami yayi ba duk da akwai mace tsakaninsu sai dai akwain shakuwa mai karfi tsakaninsu.
Suna isa gida Innarsu tace ko yunwa ce ta dawo dashi saboda bai karya ba ya fita gona sakamakon ruwan da aka kwana ana yi. Abincinsa tasa kanwarsa mai bin Danlami ta kawo masa ya daga hannu alamun ta barshi.
"Wanka zanyi na fita Inna idan na dawo sai naci"
"Da rana tsaka gagal Dahiru ina zuwa haka ka bari yamma tayi mana"
"Sahibar kokon zuciyarsa ce ta dawo" cewar Danlami yana buga masa harara har lokacin fushin kayan da baya tunanin samu yake ga sallah babba saura kwana goma sha biyar.
Inna ta hau fara'a yau tasan Dahiru zai kwana farinciki. Shi kuwa kunya tasa bai iya cewa komai ba ya shige ya watsa ruwa. Shirt da wando ya zaro a kasan akwati ya saka ya fito fes rike da kanbas din da babban wansu mai aikin kanikanci a cikin Kano ya kawo masa da zai zo.
Yana sakawa ya fito Inna ta washe baki jajayen hakoranta suka bayyana "ka gaishe min da 'yar tawa kaji ko"
"To Inna, ko zan dan sami turaren nan na Baffa ko feshi daya ne kiyi min dan Allah"
"Ai ba sai ka roka ba Danlami miko masa kuma idan ka fesa sai na hadaka da Baffan"