Sashe 13
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gidansu Mawadda yaje abin mamaki tun kafin yayi sallama gabansa ke faduwa saboda kunyar ganin Baba. Lallai baki shi ke yanka wuya. A da shine abin girmamawa ko ba komai ya girmi Baba a shekaru haka zalika ya fishi rufin asiri. Amma yanzu da yake ganin kansa mai laifi gareshi duk sai yaji ya muzanta.
Yayi sa'a Mal Fatihu ya dawo daga kasuwa inda ya sayar da dabbobin Iya tun magariba domin kuwa lokacin tara saura na dare ne.
Da Baba ya fito suka kalli juna sai wani nauyi ya sake lullube shi.
Da kyar ya iya bude baki yace "Mal Fatihu do Allah do Annabi kayi hakuri. Kuruciya da tsabagen surutu yasa Ummiyo wannan barambarama"
"Babu komai kada ka damu"
Yadda Baba ya amsa Baffa yasan ko kadan bai kai zuci ba to amma baya son jan zancen.
"Ga wannan ka rike saboda kulawa da ita." Kudi ya mikawa Mal.Fatihu har naira dubu biyar.
Shi kuwa ya noke hannu "idan domin abinda ya faru ne Mal Isiyaku ka dena damun kanka dama ko ba dade ko ba jima ai gaskiya zata fito"
Duk yadda Baffa yaso Baba yaki karbar kudin har sai da yace ko dai ya rike shi a rai ne. Jin haka yasa ya karba suka yi sallama.
Washegari Baba ne ya jagoranci tafiyarsu Kano tare da Mawadda da Yaya. Iya ba yadda batayi ba akan Ade ta bisu tace kada a ga rashin kawaicinta tunda Yayan ta tsaya tsayin daka akan lamarin. Idan sun je Baba zai kira ya sanar dasu halin da ake ciki. Idan da bukatar su tafi sai su bi bayansu.
Dubu talatin yasa a aljihu banda kudin mota. Kanwar Yaya da take aure a sallari wata unguwa cikin Kano ita ce zata shige musu gaba zuwa asibitin Malam Aminu Kano. Da isarsu gidanta suka fara wucewa. Mawadda tana ta dararewa a baya saboda ko yaya aka kalleta sai ta tsargu.
Gani take kamar ana ganinta ake gane abinda BB yayi mata. Uwa uba ta kara shiga takura saboda fitsarin nan. Duk wani motsi a sannu take yinsa sannan tana bakin kokarinta wurin ganin ta rike fitsarin. Da aka kawo musu abinci baifi loma biyar tayi ba shima don an matsa mata ne. Suna gamawa kuwa suka wuce asibitin kai tsaye.
Ita Barira a iya saninta layi ake bi idan anje asibiti a karbi kati. Saboda haka wurin ta kaisu gashi shadaya saura. Sun jima a kan layin da basu tantance na menene ba sai daga baya wani ya sanar dasu na karbar sakamakon gwaji ne ba na karbar ko bude fayil ba. Haka suka sake komawa su ka bi layin da aka nuna musu. Sun sha matukar wahala kafin suyi sa'ar bude kati amma saboda makara da suka yi aka ce bazasu ga likita ba a ranar sai washegari su tabbatar sunyi sammako.
Baba yaso su ga likita a yau saboda baya son takurawa Barira da maigidanta. Ita ce autar su Yaya bata fi shekarun Bilki ba. Bisa lalura suka kwana a gidan inda aka bawa Baba wani daki a soro.
Duk yadda suka yi ya sanar da Ade ita kuma ta fadawa su Malam. Da safe kuwa waahegari bakwai akan layi tayi musu. Suna nan har rana ta gama budewa suka karbi kati aka ce su bi layin ganin likita. Har wata ajiyar zuciya Baba yayi don murnar suna gab da samun abinda ya kawosu. Da yake ko karyawa basuyi ba suka fito yace su jira shi ya samo musu wani abin da zasu ci.
Ya dan sha wahala kafin ya sami wurin masu abinci don shi gabadaya kansa ma juyewa yayi ya kasa gane hanyar komawa inda ya baro su.
Zaman awa kusan biyu suka yi kafin a kirasu. Baba yace su shiga da Yaya zai jira su a waje. Takardun wancan asibitin da na 'yan sanda duka ya bata suka shiga.
Mawadda ta yiwa likitan bayani daidai gwargwado tana kuka. Shi tunda yake bai taba jin abu irin wannan ace daga fyade sai kasa rikon fitsari ba. Ya kira nos tazo ta duba masa jikinta har sai da tayi kwalla ganin yadda karamar yarinya irin wannan ta tsinci kanta a wannan yanayi. Ta yarda mutanen kauye akwai dauriya ba raki irin na 'yan matan birni.
Suna jiran su ji me zai ce ya daga waya ya kira. Da gani dai da na gaba dashi yake magana saboda yadda yake ta kwantar da kai tare da yin bayanin lalurar patient dinsa.
Dan dakatawa yayi yace "daga ina kuke?"
Yaya ta amsa masa "kauyen Tariwa"
Da ya gama yace suje daga waje zai kirasu akwai wadda zata zo ta duba ta.
*****
Dr Tani ta ajiye wayar ta gyara kwanciyarta tana tsaki. Maigidanta Dr Auwal yayi murmushi
"Ke da wa wannan tsakin haka?"
"Dr Yunus mana. Wai ya kasa gane kan wani case ne shine yake neman alfarmar nazo. Ni kuma yau bani ma da ra'ayin fita. Raina daya naje AKTH naje nawa asibitin."
"Idan bazai yiwu ba ko ajiye aikin AKTH din mana ki mayarda hankalinki ga naki."
"Ina jin haka za'ayi don na gaji. Yace mutanen daga kauye suke so nasan zasu iya jira ba tare da damuwa ba"
Gyara kwanciya tayi abinta duk da tasan dama ita zata karbi Dr Yunus din karfe daya. Bata jima ba ta koma bacci sai shabiyu da rabi ta farka. Shima zafi ne ya tasheta saboda an dauke wuta.
A tsanake take komai hankali kwance. Marasa lafiya indai sun damu da lafiyarsu ai dole su jira. Ba ita ta gama shiryawa ba sai wuraren biyu.
Cikin shigar da ta saba yi idan zata je asibiti ta sauko. Doguwar riga ce mai dogon hannu ta atamfa sai hijab dan madaidaici saboda dora labcoat.
Qareeba ce kadai a falon tana kallo.
""Mummy kin sauko" shine kalmar da ta fara fada mata a madadin gaisuwa.
"Eh, ina su Najib?"
"Basu tashi ba"
"Jeki ki taso min su bana son suna kaiwa rana basu yi breakfast ba" ta fada tana ajiye jakarta a gefen kujera.
Baki Qareeba ta soma turowa ta tashi ba don taso ba.
Dakunan yayyenta ta je Najib, Faisal da kuma kaninta Safwan. Da gunaguni suka iso falon Mummynsu tana cewa su ci abinci bata son suna zama da yunwa.
Abin da zai bada mamaki shine dukkaninsu sun bawa shekara ashirin baya. Safwan shekarunsa ashirin da uku. Shi da sauran duka shekaru bibbiyu ne a tsakaninsu. Dr. Tani ba karamin so take yi musu ba shiyasa tsabar gata yasa suka tashi su ba dolaye ba su ba shagwabbabu ba. Har gara Qareeba mace ce amma mazan idan suka yi wani abin tamkar a bugesu don takaici.
Zamanta tayi suna ta tabara da sokonci har suka gama cin abinci sannan ta tashi ta fita dreba ya kaita asibitin.
******
Yunwa, gajiya, kishi da bacci duka babu wanda su Mawadda basa ji. Gashi suna tattalin 'yan kudadensu saboda basu san yadda zata kaya musu ba.
Dan abin kunzugun da Ade tace ta rinka sakawa saboda danshin fitsari tuni ya gama jikewa ita kanta tasan idan ta mike za'a gani.
Yaya tana sallah a gefensu akan dankwalinta Mawadda ta dan matsa kusa da Baba. Duk yawan marasa lafiyan gurin duk sun kare sai su kadai.
"Baba ko zamu tafi gobe mu dawo" tayi maganar a hankali.
Cike da tausayawa ya kalleta "kiyi hakuri Mawadda tunda likitan yace akwai me zuwa dubaki. Nasan basu manta ba. Kinsan fa aiki yawa yake musu shiyasa kika ji shiru har yanzu"
So take ta fada masa ta soma jikewa amma kunya ta hana.
Wata mata ce ta shigo ganin Yaya tana sallah a wurin ta tabe baki.
"Babu wanda ya kai dan kauye kazanta. Ji wannan matar ta rasa wurin da zata shimfida dankwali tayi sallah sai nan da kowa yake wucewa."
Ba wasu manya bane masu maganar amma sunyi shiga ta alfarma da zata nuna ba kananun mutane bane.
Mawadda da Baba sunji ta amma duka sukayi shiru. Wadda aka nunawa yaya harda yin tsaki. Kamar hadin baki sai ga nurses da wasu likitoci uku sun fito suna gaisawa dasu. Ashe 'yar wani minista ce.
Sannan Dr Yunus ya hango su Mawadda wanda ya ma manta dasu gabadaya.
"Har yanzu kuna nan dama? Nayi zaton kun gama kun tafi tun dazu"
Baba ya danne bacin ransa. Su da babu wanda ya kulasu tun fitowarsu me zasu gama?
"Likitan da zata dubata bata iso bane?"
Dr Yunus ya dauko waya yana son sake kiran Dr. Tani amma kuma yana tsoron fadanta. Sai gashi yayi sa'a ta shigo lokacin uku da rabi tuni ta wuce ana neman hudu.
A mutumce suka gaisa da kowa musamman 'yar minista ana ta tambayarta yaya jiki sannan tace ina mara lafiyar da zata duba.
Fayil din Mawadda aka kai mata office sannan aka kirata.
Tana tashi kusan kowa a wurin ya ga yadda kujerar da ta zauna tayi naso alamun danshi. Ganin ana musu kallon wulakanci Yaya ta dauki dankwalinta ta tsiyaya pure water a wurin ta hau gogewa. Daga wannan ya yamutsa fuska sai masu kananun maganganu don me tasan tana da lalura zata zauna akan kujerar. Maganganun sun yiwa Yaya zafi ta dai gyara wurin ta bi bayan Mawadda da Baba zuwa ofishin likitar.
A nutse take gabatar da komai Baba duk haushi ya ishe shi. Sai da ta gama karanta duka bayanan wancan asibitin sannan ta dan kalli Baba.
"Yallabai a bamu wuri muyi aikinmu ko. Ko a gabanka zan dubata?"
Har dan rissinawa yayi mata saboda kawai ta kyautata duba masa Mawadda "yi hakuri ranki ya dade bari na dakata daga waje. Mawadda kiyi bayani sosai kinji ko"
Kai ta gyada masa ya rufo kofar. Dama a tsaye take saboda yanayin jikinta. Gadon da yake cikin ofishin Dr. Tani ta nuna mata tace ta kwanta.
Yaya dai tana gefe Dr. Tani ta tsaya a gaban Mawadda tana dubata. Yanayin da taganta yasa jikinta yayi matukar sanyi ba kadan ba. Wane dabba ne yayi mata wannan mugun aikin haka. Da kyar ta iya hadiyar yawu saboda tashin hankali. Musamman da taga ko yaya ta tabata sai ta runtse ido ko hawaye ya fito.
"Har yanzu wurin da ciwo ko?"
Yayi sa'a Mal Fatihu ya dawo daga kasuwa inda ya sayar da dabbobin Iya tun magariba domin kuwa lokacin tara saura na dare ne.
Da Baba ya fito suka kalli juna sai wani nauyi ya sake lullube shi.
Da kyar ya iya bude baki yace "Mal Fatihu do Allah do Annabi kayi hakuri. Kuruciya da tsabagen surutu yasa Ummiyo wannan barambarama"
"Babu komai kada ka damu"
Yadda Baba ya amsa Baffa yasan ko kadan bai kai zuci ba to amma baya son jan zancen.
"Ga wannan ka rike saboda kulawa da ita." Kudi ya mikawa Mal.Fatihu har naira dubu biyar.
Shi kuwa ya noke hannu "idan domin abinda ya faru ne Mal Isiyaku ka dena damun kanka dama ko ba dade ko ba jima ai gaskiya zata fito"
Duk yadda Baffa yaso Baba yaki karbar kudin har sai da yace ko dai ya rike shi a rai ne. Jin haka yasa ya karba suka yi sallama.
Washegari Baba ne ya jagoranci tafiyarsu Kano tare da Mawadda da Yaya. Iya ba yadda batayi ba akan Ade ta bisu tace kada a ga rashin kawaicinta tunda Yayan ta tsaya tsayin daka akan lamarin. Idan sun je Baba zai kira ya sanar dasu halin da ake ciki. Idan da bukatar su tafi sai su bi bayansu.
Dubu talatin yasa a aljihu banda kudin mota. Kanwar Yaya da take aure a sallari wata unguwa cikin Kano ita ce zata shige musu gaba zuwa asibitin Malam Aminu Kano. Da isarsu gidanta suka fara wucewa. Mawadda tana ta dararewa a baya saboda ko yaya aka kalleta sai ta tsargu.
Gani take kamar ana ganinta ake gane abinda BB yayi mata. Uwa uba ta kara shiga takura saboda fitsarin nan. Duk wani motsi a sannu take yinsa sannan tana bakin kokarinta wurin ganin ta rike fitsarin. Da aka kawo musu abinci baifi loma biyar tayi ba shima don an matsa mata ne. Suna gamawa kuwa suka wuce asibitin kai tsaye.
Ita Barira a iya saninta layi ake bi idan anje asibiti a karbi kati. Saboda haka wurin ta kaisu gashi shadaya saura. Sun jima a kan layin da basu tantance na menene ba sai daga baya wani ya sanar dasu na karbar sakamakon gwaji ne ba na karbar ko bude fayil ba. Haka suka sake komawa su ka bi layin da aka nuna musu. Sun sha matukar wahala kafin suyi sa'ar bude kati amma saboda makara da suka yi aka ce bazasu ga likita ba a ranar sai washegari su tabbatar sunyi sammako.
Baba yaso su ga likita a yau saboda baya son takurawa Barira da maigidanta. Ita ce autar su Yaya bata fi shekarun Bilki ba. Bisa lalura suka kwana a gidan inda aka bawa Baba wani daki a soro.
Duk yadda suka yi ya sanar da Ade ita kuma ta fadawa su Malam. Da safe kuwa waahegari bakwai akan layi tayi musu. Suna nan har rana ta gama budewa suka karbi kati aka ce su bi layin ganin likita. Har wata ajiyar zuciya Baba yayi don murnar suna gab da samun abinda ya kawosu. Da yake ko karyawa basuyi ba suka fito yace su jira shi ya samo musu wani abin da zasu ci.
Ya dan sha wahala kafin ya sami wurin masu abinci don shi gabadaya kansa ma juyewa yayi ya kasa gane hanyar komawa inda ya baro su.
Zaman awa kusan biyu suka yi kafin a kirasu. Baba yace su shiga da Yaya zai jira su a waje. Takardun wancan asibitin da na 'yan sanda duka ya bata suka shiga.
Mawadda ta yiwa likitan bayani daidai gwargwado tana kuka. Shi tunda yake bai taba jin abu irin wannan ace daga fyade sai kasa rikon fitsari ba. Ya kira nos tazo ta duba masa jikinta har sai da tayi kwalla ganin yadda karamar yarinya irin wannan ta tsinci kanta a wannan yanayi. Ta yarda mutanen kauye akwai dauriya ba raki irin na 'yan matan birni.
Suna jiran su ji me zai ce ya daga waya ya kira. Da gani dai da na gaba dashi yake magana saboda yadda yake ta kwantar da kai tare da yin bayanin lalurar patient dinsa.
Dan dakatawa yayi yace "daga ina kuke?"
Yaya ta amsa masa "kauyen Tariwa"
Da ya gama yace suje daga waje zai kirasu akwai wadda zata zo ta duba ta.
*****
Dr Tani ta ajiye wayar ta gyara kwanciyarta tana tsaki. Maigidanta Dr Auwal yayi murmushi
"Ke da wa wannan tsakin haka?"
"Dr Yunus mana. Wai ya kasa gane kan wani case ne shine yake neman alfarmar nazo. Ni kuma yau bani ma da ra'ayin fita. Raina daya naje AKTH naje nawa asibitin."
"Idan bazai yiwu ba ko ajiye aikin AKTH din mana ki mayarda hankalinki ga naki."
"Ina jin haka za'ayi don na gaji. Yace mutanen daga kauye suke so nasan zasu iya jira ba tare da damuwa ba"
Gyara kwanciya tayi abinta duk da tasan dama ita zata karbi Dr Yunus din karfe daya. Bata jima ba ta koma bacci sai shabiyu da rabi ta farka. Shima zafi ne ya tasheta saboda an dauke wuta.
A tsanake take komai hankali kwance. Marasa lafiya indai sun damu da lafiyarsu ai dole su jira. Ba ita ta gama shiryawa ba sai wuraren biyu.
Cikin shigar da ta saba yi idan zata je asibiti ta sauko. Doguwar riga ce mai dogon hannu ta atamfa sai hijab dan madaidaici saboda dora labcoat.
Qareeba ce kadai a falon tana kallo.
""Mummy kin sauko" shine kalmar da ta fara fada mata a madadin gaisuwa.
"Eh, ina su Najib?"
"Basu tashi ba"
"Jeki ki taso min su bana son suna kaiwa rana basu yi breakfast ba" ta fada tana ajiye jakarta a gefen kujera.
Baki Qareeba ta soma turowa ta tashi ba don taso ba.
Dakunan yayyenta ta je Najib, Faisal da kuma kaninta Safwan. Da gunaguni suka iso falon Mummynsu tana cewa su ci abinci bata son suna zama da yunwa.
Abin da zai bada mamaki shine dukkaninsu sun bawa shekara ashirin baya. Safwan shekarunsa ashirin da uku. Shi da sauran duka shekaru bibbiyu ne a tsakaninsu. Dr. Tani ba karamin so take yi musu ba shiyasa tsabar gata yasa suka tashi su ba dolaye ba su ba shagwabbabu ba. Har gara Qareeba mace ce amma mazan idan suka yi wani abin tamkar a bugesu don takaici.
Zamanta tayi suna ta tabara da sokonci har suka gama cin abinci sannan ta tashi ta fita dreba ya kaita asibitin.
******
Yunwa, gajiya, kishi da bacci duka babu wanda su Mawadda basa ji. Gashi suna tattalin 'yan kudadensu saboda basu san yadda zata kaya musu ba.
Dan abin kunzugun da Ade tace ta rinka sakawa saboda danshin fitsari tuni ya gama jikewa ita kanta tasan idan ta mike za'a gani.
Yaya tana sallah a gefensu akan dankwalinta Mawadda ta dan matsa kusa da Baba. Duk yawan marasa lafiyan gurin duk sun kare sai su kadai.
"Baba ko zamu tafi gobe mu dawo" tayi maganar a hankali.
Cike da tausayawa ya kalleta "kiyi hakuri Mawadda tunda likitan yace akwai me zuwa dubaki. Nasan basu manta ba. Kinsan fa aiki yawa yake musu shiyasa kika ji shiru har yanzu"
So take ta fada masa ta soma jikewa amma kunya ta hana.
Wata mata ce ta shigo ganin Yaya tana sallah a wurin ta tabe baki.
"Babu wanda ya kai dan kauye kazanta. Ji wannan matar ta rasa wurin da zata shimfida dankwali tayi sallah sai nan da kowa yake wucewa."
Ba wasu manya bane masu maganar amma sunyi shiga ta alfarma da zata nuna ba kananun mutane bane.
Mawadda da Baba sunji ta amma duka sukayi shiru. Wadda aka nunawa yaya harda yin tsaki. Kamar hadin baki sai ga nurses da wasu likitoci uku sun fito suna gaisawa dasu. Ashe 'yar wani minista ce.
Sannan Dr Yunus ya hango su Mawadda wanda ya ma manta dasu gabadaya.
"Har yanzu kuna nan dama? Nayi zaton kun gama kun tafi tun dazu"
Baba ya danne bacin ransa. Su da babu wanda ya kulasu tun fitowarsu me zasu gama?
"Likitan da zata dubata bata iso bane?"
Dr Yunus ya dauko waya yana son sake kiran Dr. Tani amma kuma yana tsoron fadanta. Sai gashi yayi sa'a ta shigo lokacin uku da rabi tuni ta wuce ana neman hudu.
A mutumce suka gaisa da kowa musamman 'yar minista ana ta tambayarta yaya jiki sannan tace ina mara lafiyar da zata duba.
Fayil din Mawadda aka kai mata office sannan aka kirata.
Tana tashi kusan kowa a wurin ya ga yadda kujerar da ta zauna tayi naso alamun danshi. Ganin ana musu kallon wulakanci Yaya ta dauki dankwalinta ta tsiyaya pure water a wurin ta hau gogewa. Daga wannan ya yamutsa fuska sai masu kananun maganganu don me tasan tana da lalura zata zauna akan kujerar. Maganganun sun yiwa Yaya zafi ta dai gyara wurin ta bi bayan Mawadda da Baba zuwa ofishin likitar.
A nutse take gabatar da komai Baba duk haushi ya ishe shi. Sai da ta gama karanta duka bayanan wancan asibitin sannan ta dan kalli Baba.
"Yallabai a bamu wuri muyi aikinmu ko. Ko a gabanka zan dubata?"
Har dan rissinawa yayi mata saboda kawai ta kyautata duba masa Mawadda "yi hakuri ranki ya dade bari na dakata daga waje. Mawadda kiyi bayani sosai kinji ko"
Kai ta gyada masa ya rufo kofar. Dama a tsaye take saboda yanayin jikinta. Gadon da yake cikin ofishin Dr. Tani ta nuna mata tace ta kwanta.
Yaya dai tana gefe Dr. Tani ta tsaya a gaban Mawadda tana dubata. Yanayin da taganta yasa jikinta yayi matukar sanyi ba kadan ba. Wane dabba ne yayi mata wannan mugun aikin haka. Da kyar ta iya hadiyar yawu saboda tashin hankali. Musamman da taga ko yaya ta tabata sai ta runtse ido ko hawaye ya fito.
"Har yanzu wurin da ciwo ko?"