← Book details Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 68

Sashe 61

Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da yamma Dahiru ya fadawa Mawadda zasu fita da Bilya da Attahir.

"Zaki je wurin Nawal ko zaki kwanta idan na dawo muyi hira"

"Wurin Nawal zani idan ka dawo muyi bacci dai"

Dariya yayi yana cewa sai ya dawo din a zabi daya sannan yace "Gidansu Anti Qareeba zamuje neman aure"
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰25

*Batul Mamman*💖

Da gudu Attahir yabi motar batare da yasan ina zata ko me yake yi ba. Ko kadan bai cimmata ba ya sake dawo a guje wurin da Dahiru yake ya samu maigadinsu Qareeba ya dora kansa a cinyarsa yana ce masa ya dauko motarsu a tafi asibiti. To yace kawai ya tafi gidan tsabar rudewa ya ma manta gidan nasa iyayen yafi kusa.

Gate a rufe ya shiga bugu baji ba gani. Dr Tani tana sama dakin mijinta don tuni ta sallama nata dakin inda aka kusa gamawa da Qareeba ta jiyo bugun. Tasowa tayi tana mitar waye da gajen hakuri kuma ina maigadinsu.

Mai aikinsu mace ce tazo ta zare sakatar da basu san ta yaya akayi ta dawo ta rufe da kanta ba ya banko kofar ya shiga.

"Bude min gate, bude min da sauri" yace yana kokarin zura mukullin gidansa ya bude motar.

Dr Tani har ta fito lokacin ta ganshi duk a daburce. Dama Haj Mama takance Attahir bai iya shiga tashin hankali ba tamkar mace idan ya rude kasa tunanin kirki yake. To a yanzu Attahir babu abinda yake hange sai Dahiru yana ganin kamar ya mutu ne.

A tsorace tace "Attahir me ya faru haka?"

"Dahiru ne. BB ne yazo ya buge Dahiru da mota zan kaishi asibiti" ya amsa yana laluben aljihunsa babu mukullin motar da ya manta suna wurin Dahiru.

Bilya ne yace "Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" fitowarsu kenan shi da Qareeba su ma sunji bugun da takun Dr Tani cikin sauri.

Duka su hudun tare suka fita. Motar Bilya tana waje yayi saurin budeta. Baba Prof da Haj Mama sun fito tana kuka maigadinsu ne ya fada musu. Dunguma suka yi sai asibiti hankalin kowa a tashe.

Emergency akayi da Dahiru domin samun taimakon gaggawa. Ana cewa hatsari ne likitoci suka fara cewa a nemo 'yan sanda. Ana cewa 'yan sanda Bilya yace a nemi wayar Dahiru a kira DPO din bompai su ji ya akayi haka ta faru sannan su zo domin a karbe shi. An dauko wayar ta kwankwatse aka saka sim din a wayar Attahir yana sawa kuwa wayar wani inspector ta shigo.

"Mal.Dahiru ina ka shiga muna ta nemanka. Babawo ya gudu yanzu haka nemansa muke ido rufe..."

Wata tsawa Attahir yayi rai a bace "Dahiru yana kwance yanzu haka muna asibiti BB ya bige shi da mota saboda sakacinku"

Inspector ya zaro idanu ya mikawa DPO. Yana karba ya tambayi asibitin da kansa da wasu suka tafi yayin da suka baza nema BB lungu da sako.

Kafin su iso Baba Prof yana zaune ya mike da sauri "Mawadda, Attahir su Mawadda suna gida?"

Hankulansu sai lokacin suka kara tashi ya amsa a gigice yana tunanin Nawal da Mawadda su kadai a gidan.

"Suna gida Baba bari na tafi"

Bilya yace ya dakata "daga nan zuwa unguwarku da tafiya Attahir abinda yafi shine su fito daga gidan. Danlami ne a kusa bari na fada masa amma dole su fito yanzu yanzu babu bata lokaci"

Jikin Haj Mama da Dr Tani yayi mugun sanyi domin kuwa tun dazu ya kamata suyi wannan tunanin. Yanzu da wuya idan su BB basu je ba indai sun san gidan.

Qareeba harda kuka ganin Ahirin a wannan yanayin ga kuma matarsa ana tunanin zai je gidansu.

Attahir ya dage sai ya tafi Baba Prof yace ya fara kira masa Nawal ya bashi wayar zaiyi mata magana. Kuskure kalilan zasu yi komai ya ruguje BB ya sake samun dama a karo na biyu.

Shi dai Attahir ji yake kamar ya tashi sama haka ya kira Nawal shi kuma Bilya ya fadawa Danlami ya gaggauta zuwa gidansu Dahiru ya taho dasu.

******

Nawal zata shiga wanka kenan wurin karfe takwas na dare taji wayar ta dauka da murmushi ganin sunan mijinta. Muryarsa ce ta bata tsoro yace ta rike waya Baba zaiyi mata magana.

Cike da nutsuwa da kokarin danne tashin hankali saboda sanin halin mata yace "kuna tare da Mawadda?"

Gabanta yayi mugun bugu tace masa ta tafi gida yanzun nan.

"To ki saurareni da kyau Nawal rayuwarki da ta Mawadda tana ga Allah tana gareki"

Fitsari ne kawai bata saki ba bayan Baba Prof ya gama fada mata yadda zata yi da halin da ake ciki.

Kayan da ta cire ta saka da sauri ta dauko mukullin motar Attahir da gudu har tana tuntube ta hau sama.

Mawadda tana hada fruitsalad ta ganta ta shigo babu sallama ta tashi tana neman gudu kafin taji me yake faruwa.

"Nawal ke da waye?"

"Dauko mayafi Mawadda yi sauri"

"Lafiya?"

Daurewa take kada ta tsorata amma abu yaci tura "BB ya gudo daga police station"

Wata irin kadawa cikinta yayi har ya kulle taji gumi yana kwararo mata. Hannu na rawa ta rarumi wayarta tuni har ta soma hawaye "Yayanmu zan kira Nawal yaya zanyi?"

Sai kuka tana ta kokarin kira Nawal ta karbe wayar ta dauko hijabin da ta ajiye a falon bayan ta dawo daga kasa ta dora mata.

"Tuki yake yi hankalinsa a tashe yake shine Yaya Attahir yace gara mu fita kada mu zauna a gidan"

A gurguje suka sauko suna zuwa bakin mota Mawadda ta koma sama da gudu ba jimawa sai gata da tabarya da muciya tayi musu riko na musamman.

Gate taje budewa Nawal da ta iya mota tun a gida ta tayar da ta Attahir ta juyata yadda zasu iya fita. Batare da bata lokaci ba suka shiga ko rufe gidan basu yi ba suka fice daga layin.

Suna hanya Danlami ya kira suka sanar dashi inda suke yace su hadu a Health Matters wani sabon asibitin kudi.

A gigice tace "wurin wa zamu je?"

"Mu hadu a can din dai kada ku tsaya ko ina"

Kashe wayar yayi ta shiga rusa kuka jikinta yana bata wani abu ya sami Dahirunta. Ta tabbata ba tuki ba ko me yake yi bazai taba kin nemanta ba idan yaji BB ya fito. Ta rasa me yake faruwa sai addu'o'i take janyowa.

Layi biyar su BB suka shiga suna neman gidan Dahiru amma kamar wandanda aka shafewa kwakwalwa sun kasa tuna wanne ne gidan har fada ya kaure musu. Bobo yana layi na uku BB yana cewa dazu da suka zo layi na hudu ne. A wannan yanayin su Nawal suka wucesu batare da sun gane su ba.

Daga karshe sun gane gidan a layi na biyu amma ganin gate din irin wanda ake ja gefe a bude suka san cewa tabbas babu kowa a ciki. Duk da haka sun shiga ga sun ga shatin yadda Nawal taci taya wurin ribas. Duka BB ya kaiwa gate din da hannunsa wani mugun bakinciki yana cin ransa. Yaso kwarai ya sami Mawadda da sai yayi mata rashin mutumci fiye da wanda yayi mata a shekarun baya. Wulakanta ta yayi niyar yi saboda tana zaman aure da mutumin da ya zubar masa da hakora har uku.

Bobo ya dafa kafadarsa "BB kazo mu tafi kasan dole 'yan sanda zasu biyo ka"

"Bazan iya hakura da yarinyar nan ba fa. I must have her kafin na haukace da sonta" yace yana furzar da iska.

Bobo yayi murmushin gefen baki. Wai soyayya BB yake kira. Wannan abu yafi dacewa da hauka zalla amma yadda ya kula ransa ya kai kololuwar baci gara yayi shiru.

Chanjin wurin zama suka yi ya dauko kwalaben giya biyu daga karkashin kujerar ya bawa BB wai ya sha yaji sanyi a ransa. Ba bata lokaci kuwa ya kafa kai duka kwalba biyun ya shanye kafin su isa gidan wani kawun Haj Mara inda ta koma a dole saboda kudin hotel yana ruguza musu guzuri. Kawun nata ma dai a bisa dole saboda girman zumunci ya bata masauki ba don yaso ba.

*******

Suna shiga asibitin Attahir da Danlami da yazo a babur din abokinsa suna bakin gate. Ko kashe motar bata yi ba suka fito Nawal tayi wurin Attahir da gudu Mawadda kuwa ciki tayi saboda ganin adaidaita sahu ya ajiye iyayenta a ciki.

Su Yaya sunyi zaton ta san Dahiru ne a kwance suka fara tausarta akan hakuri. Wani irin kuka ta saka ta wuce ciki idanunta rufe da hawaye masu dumi.

Kofar dakin da ta hango Bilya da 'yan sanda wurin biyar ta nufa sai ga Qareeba da basu taba haduwa ba ta taho ta rungumeta cikin muryar rarrashi da tausasawa tace "Mawadda ki dena kuka zai tashi in sha Allah"

Ita bata san wannan ce Anti Qareeba ba sai dai kawai ta tsinci kanta da kankameta saboda wani tukukin zuciya da ya debota tana jin kamar ta zube a wurin. Hawaye take yi babu kakkautawa babu mai cewa tayi shiru sai Qareeba da take bubbuga bayanta.

Kofar dakin aka bude idanuwa sama da goma suka yo kan likitan da nurse da suka fito. Sai tambayoyi akan yaya jikin nasa.

"Alhamdulillah munyi mamaki kuma mungode Allah domin Ya takaitawa Dahiru wahala. Ya sami gocewar kashi ne a kafa wannan likitan kashin..." ya nuna wanda ya fito a lokacin "shine ya gyara masa. Sai kuma buguwa nasan zaiyi kwanaki yana fama da ciwon jiki. Idan an cire wannan babu wata matsala in sha Allahu"

Ajiyar zuciya suke ta saukewa ana da mika godiya ga Allah sai kuma tsinuwa ga BB ta biyo baya. A kidime Mawadda ta kalli Attahir.

"Ba hatsari kuka yi bane?"

"BB ne ya buge shi da mota"

Sulalewa tayi kasa zuciyarta tana matsanancin bugu kamar ta faso kirjinta ga wata irin mutuwar jiki da ta saukar mata.

Muryarta tana rawa ta dago ta kalli Baba "Baba kaji saboda ni zai kashe Yayanmu" cure jikinta tayi a wuri daya ta saki kuka. Ta bawa kowa tausayi.

Nawal tazo ta rungumeta a wurin suna kukansu tare da Qareeba.

Baba Prof yace "to yanzu kuka zaku yi in sa a mayar daku gida ko zaku yi shiru mu shiga mu ga halin da yake ciki?"
Chapter 61 · 0% Book details