Sashe 39
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonta yayi fuska ta jike da hawaye "ni da nazo ki rarrasheni shine zaki barni da rarrashinki. Ki tashi ki zauna naji dadi ina da ke da zan fadawa damuwata. Kaina da zuciyata duka suka kulle na kasa tunani dazu"
Sun cigaba da hira akan wannan mummunar ta'asa da ta addabi al'ummar kasarmu. Taji tausayin Qareeba sosai balle da taji itama tasha duka kusan irin nata.
"Uhmm Yayanmu ita yayi mata dinne ko dukan ne kawai?"
"Bani da tabbas sai gobe idan naje zanji. Kinga da an daura aurenmu tare zamu je"
"Yanzu ma zanyi mata addu'ar samun lafiya domin wannan tabon da wuya yake warkewa duka zahiri da badini. Ka ga har yanzu ina da tabon belt a jikina guda daya yaki bacewa" tace a hankali.
Dahiru ya dubeta soyayyarta na kara samun gurbi a zuciyarsa.
"Ki tuna min ranar da aka kawo min ke wannan tabon zan fara nema a jikinki nayi kissing"
Tashi Mawadda tayi cikin matsananciyar kunya ta diririce tana neman hanyar fita tace "na shigesu"
Dahiru shima ya tashi "ba ke kadai ba nima na shiga." Ya fada yana dukan bakinsa harda yi wa bakin fada.
Ya rigata kaiwa bakin kofa "kinga ni nayi nan ki tabbata kin manta wannan maganar kinji ko."
Da hannu biyu kamar tana korarsa ta rinka nuna masa kofa "jeka ni dai sai da safe"
Takalmansa ya zura ya juyo yana mata murmushi "nace ba...."
Shan kunu tayi kada ya kawo wasa sai dai kana ganinta kasan dauriya tayi don ba karamar kunya take ji ba ganinsa ma da take a wurin "kace me?"
"Zan iya kiranki kafin na kwanta?"
"Na yafe Yayanmu don Allah ka tafi"
Gira daya ya daga yana murmushi "kin tabbata?"
"Eh, eh na tabbata"
"Da gaske zaki iya bacci batare da nace miki sai da safe ba Mawadda?"
Tunda suke bata taba jin tana so ya tafi irin na yau ba. Kuma sai wani jan zance yake yana kara sakata jin kunya.
"Wayyo Yayanmu kaje duka na yafe."
Dariya yayi ya tafi ta sauke ajiyar zuciya tana rike kirjinta da yake bugawa da karfi.
Ta taho zata fita kawai ya sake dawowa ciki idanunsa karaf cikin nata tayi kasa da kanta da sauri.
"Kina sona Mawadda?" Ya fada da wata irin murya a tausashe.
"Wai baza ka tafi ba?"
"Sai kin bani amsa ko na dawo ciki mu zauna naga daren da sauransa"
"Ka fa san amsar"
"Ban taba ji kin fada bane shiyasa yanzu naji ina kokonto"
Idanu ta ware tana ganin me zai sa shi wannan tunanin. So take ya tafi kuma saboda har yanzu maganarsa ta dazu tana mata yawo a kanta
"Ina yi"
Sake matsowa yayi ta ja baya "kina me?"
Cije lebe tayi ya lumshe idanunsa. Baya so tana wannan abin a yanzu dai da suke da katanga tsakaninsu.
Sai da taja numfashi sannan tace "Yayanmu Dahiru ina sonka amma don Allah ka tafi kafin nasa maka ihu"
"Nima ina sonki Mawaddatan wa Rahma, sai da safe"
Sake fita yayi tayi murmushi tana juyi "oh Allah Ka bani Yayanmu Dahiru"
Bata san ta ina ya sake bullowa ba sai ganinsa tayi a bakin kofar yace "Amin Ya Rabbi"
Ihu kawai tasa masa kunyar tayi mata yawa "Ahhhhh"
Yana jin haka ya fice da sauri yana dariya. Toshe bakinta tayi tana fatan babu wanda yaji daga ciki.
*****
A can asibiti an yiwa Qareeba aiki lafiya. Dr Tani kam basu da zabin da ya wuce sedating dinta wato aka sata baccin dole saboda suna so lokacin da zata farka ta ga Qareeba ma ta tashi. Me yiwu wa hakan zai taimaka wurin daidaituwar jinin nata.
Daki daya aka ajiye su zuwa wayewar gari. Dr Auwal sai shabiyun dare ya koma gida. Falon da abin ya afku wanda a waya ya sanar da Maigadi a fadawa maiaikinsu kada ta taba komai da sunan gyara yaje hankalinsa ya tashi haka ya hau sama yana ganin jinin 'yarsa a kasa. Daki gabadaya ya hargitse musamman da yake a nan Dahiru ya yiwa BB duka. Kansa yaji ya soma ciwo ya bar wurin.
Su Najib, matansu da Dr Auwal da sassafe suka koma asibitin. Sun sami Dr Tani tana ta bada order ayi kaza a dauko mata kaza tana tsaye akan Qareeba. Likitocin da nurses sai rokonta suke yi akan ta koma nata gadon ta kwanta zasu kula da Qareeba amma ta ki. Sai ma fada da take yiwa kowa.
"In koma in kwanta ku karasa min yarinya?"
Maigidanta da ta gani ne ta sa kuka murya a shake tace "Daddy ka ga Qareeba taki farkawa tun jiya"
Tausayi ta bashi matuka yasan yadda take bala'in son Qareeba duk cikin 'ya'yanta.
"Zo muje wani dakin ki basu wuri su yi aikinsu. Za ta tashi in sha Allah"
Sai da yayi da gaske ta biyo shi zuwa wani dakin sauran suka tsatstsaya a waje suna jiran bayani game da halin da take ciki. An dade ana bincike har ta fara wata irin jijjiga akan gadon. Can dai aka sake yi mata scanning abin mamaki wani dan karamin gilas ne cikin wanda su ka suke ta ya shige jikinta ya taba kodarta daya. Dole sai an sake yi mata wani aikin. Su Safwan da girmansu su ka rinka kuka yayin da wata nurse take musu bayanin hakan yana faruwa sosai. Aji ciwo da glass ko karfe idan ya karye a jiki yawo yake yi. Zai iya bin duk inda yaso idan anyi rashin sa'a ya taba mahimman sassa ya jiwa mutum mugun rauni.
Dr Tani dagewa tayi ita zata yi aikin tana ta kuka kamar ranta zai fita. Wani azababben ciwon kai ne ya bugeta lokaci guda sai jiri ta fadi a kasa. Gado aka mayar da ita mai yin aikin ya tafi da Qareeba yayin da wasu suka tsaya a kanta.
Iyalan gidan Dr Auwal sun ga abin da basu taba gani ba a wannan rana. Anyi aiki lafiya kafin azahar an fito da ita.
Suna tsaye a kanta ta bude idonta mai lafiyar a hankali tare da motsa hannunta da yake cikin na Dr Tani.
Tana hawaye ta sake riketa tace "Qareeba kalle ni nan, kin gane ni? Mummynki ce"
Baki da ido daya sun suntume da kyar ta iya motsa shi tace "Mummy"
Mahaifinta da 'yan uwa ta rinka bi da ido daya bayan daya tana hawaye. Ina suke lokacin da take ta kiransu da neman agaji. Hannu ta daga ta yafito Dr Auwal ya duka daidai bakinta da kyar tace "Babawo"
Idanunsa sunyi ja sosai yace "na sani Qareeban Daddy bazan barshi ba. Warkewarki kawai nake da bukata"
Dr Tani na kuka tace ina wayarta. Maigidanta ya miko mata tace da su Safwan duk su fita zata yi waya. Kallon juna suka shiga yi kafin su bi umarninta.
Suna fita ta kira Haj Mara. Ringing biyu kamar tana jira ta dauka a lokacin kuma babban wan Dr Tani ya shigo dakin bata da damar katse kiran tunda ya shiga kuma a zuciye take.
Haj Mara kusan kwana tayi tana kiranta dama harda Qareeba babu wanda ya dauka.
"Haba Tani, haba don Allah. Kun daga min hankali ina ta nemanki tun jiya inji ina Babawo yake daga cewa...."
Daga murya Dr Tani tayi irin yadda wani bai taba ji ba cike da masifa tace "dakata min Marakisiyya. Babawon banza, ashe dan naki dan akuya ne dabba mara hankali... "
Gabanta ne ya fadi ba dai yaje ya tafka wata ta'asar ba. Sai kuma bacin rai don bazata taba yin shiru ana zagar mata da ba.
"Tani kinsan da wa ki ke magana kuwa?"
Cikin fada tace "Wacece ke banda macuciya azzaluma. Ni zaki ha'inta ki turo min wannan mahaukacin ya auri Qareeba. To ki saurareni na rantse miki sai naga bayanki da na Babawo"
"Wai meye haka? Me yayi miki?"
"Ashe iskancin nasa na karya ne tunda bai dawo gida ya fada miki ba. Muna asibiti daga jiya zuwa yau anyiwa Qareeba surgery har biyu kinji daya. Yayi mata dukan da ko a film ban taba ganin an yiwa mutum irinsa ba kinji biyu. Ba don tsarewa ta Allah ba sauran kiris ya yi mata fyade kinji uku. Ki tsananta addu'a yarinyata ta shi idan ba haka ba ban ga kudin da kuke dashi da zai hana na rufe danki ba. Idan kin manta 2010 ni ban manta ba. Amma ki sani ta inda aka hau ta nan za'a sauko"
Kashe wayar tayi batare da ta bata damar amsawa ba. Hannu ta dora a ka ta saka kuka. Karo na biyu ana fada mata wannan kalma. Rannan Yasmin ta fada yau Dr Tani. Abu daya ya tsaya mata a rai....Mawadda!
Dr Auwal ne ya kalli matarsa saboda gabadaya ya kasa fahimtar inda ta dosa.
"Me ya faru a 2010 Tani?"
Alh Munzali wan Dr Tani yayi dariya "ashe 'yan boko ma suna boyewa juna sirri"
"Yaya don Allah ka bar maganar nan" kadai ta iya cewa duk da tasan ranar wanka ba'a boyon cibi.
"Fadawa mijinki ba hurumi na bane Tani nazo dubaku ne duk da kin yanke alaka damu saboda sawa ranki da ki ka yi bama kaunarki bama kaunar zuri'arki. Duk wani abu da muke yi miki muna yi ne don gyara son 'ya'ya ya rufe miki ido kin kasa fahimta"
Kujera ta samu ta zauna tana kuka Alh Munzali ya kalli Qareeba yace "Allah Ya baki lafiya Ya saka miki. Fyade ba karshen rayuwa bane zaki cigaba da harkokinki kamar kowa"
Dr Tani ta katse shi "Yaya Munzali baiyi raping dinta ba"
Irin dariyar kin ma raina min hankali yayi kafin yace mata "ko duk jikina kunne ne bazan yarda. Nasan dama dole kiyi kokarin boyewa amma ki sani rufewar ba gata bane. Zan wuce amma zamu dawo anjima tunda na tabbatar da labarin ba jita jita bane"
Sun cigaba da hira akan wannan mummunar ta'asa da ta addabi al'ummar kasarmu. Taji tausayin Qareeba sosai balle da taji itama tasha duka kusan irin nata.
"Uhmm Yayanmu ita yayi mata dinne ko dukan ne kawai?"
"Bani da tabbas sai gobe idan naje zanji. Kinga da an daura aurenmu tare zamu je"
"Yanzu ma zanyi mata addu'ar samun lafiya domin wannan tabon da wuya yake warkewa duka zahiri da badini. Ka ga har yanzu ina da tabon belt a jikina guda daya yaki bacewa" tace a hankali.
Dahiru ya dubeta soyayyarta na kara samun gurbi a zuciyarsa.
"Ki tuna min ranar da aka kawo min ke wannan tabon zan fara nema a jikinki nayi kissing"
Tashi Mawadda tayi cikin matsananciyar kunya ta diririce tana neman hanyar fita tace "na shigesu"
Dahiru shima ya tashi "ba ke kadai ba nima na shiga." Ya fada yana dukan bakinsa harda yi wa bakin fada.
Ya rigata kaiwa bakin kofa "kinga ni nayi nan ki tabbata kin manta wannan maganar kinji ko."
Da hannu biyu kamar tana korarsa ta rinka nuna masa kofa "jeka ni dai sai da safe"
Takalmansa ya zura ya juyo yana mata murmushi "nace ba...."
Shan kunu tayi kada ya kawo wasa sai dai kana ganinta kasan dauriya tayi don ba karamar kunya take ji ba ganinsa ma da take a wurin "kace me?"
"Zan iya kiranki kafin na kwanta?"
"Na yafe Yayanmu don Allah ka tafi"
Gira daya ya daga yana murmushi "kin tabbata?"
"Eh, eh na tabbata"
"Da gaske zaki iya bacci batare da nace miki sai da safe ba Mawadda?"
Tunda suke bata taba jin tana so ya tafi irin na yau ba. Kuma sai wani jan zance yake yana kara sakata jin kunya.
"Wayyo Yayanmu kaje duka na yafe."
Dariya yayi ya tafi ta sauke ajiyar zuciya tana rike kirjinta da yake bugawa da karfi.
Ta taho zata fita kawai ya sake dawowa ciki idanunsa karaf cikin nata tayi kasa da kanta da sauri.
"Kina sona Mawadda?" Ya fada da wata irin murya a tausashe.
"Wai baza ka tafi ba?"
"Sai kin bani amsa ko na dawo ciki mu zauna naga daren da sauransa"
"Ka fa san amsar"
"Ban taba ji kin fada bane shiyasa yanzu naji ina kokonto"
Idanu ta ware tana ganin me zai sa shi wannan tunanin. So take ya tafi kuma saboda har yanzu maganarsa ta dazu tana mata yawo a kanta
"Ina yi"
Sake matsowa yayi ta ja baya "kina me?"
Cije lebe tayi ya lumshe idanunsa. Baya so tana wannan abin a yanzu dai da suke da katanga tsakaninsu.
Sai da taja numfashi sannan tace "Yayanmu Dahiru ina sonka amma don Allah ka tafi kafin nasa maka ihu"
"Nima ina sonki Mawaddatan wa Rahma, sai da safe"
Sake fita yayi tayi murmushi tana juyi "oh Allah Ka bani Yayanmu Dahiru"
Bata san ta ina ya sake bullowa ba sai ganinsa tayi a bakin kofar yace "Amin Ya Rabbi"
Ihu kawai tasa masa kunyar tayi mata yawa "Ahhhhh"
Yana jin haka ya fice da sauri yana dariya. Toshe bakinta tayi tana fatan babu wanda yaji daga ciki.
*****
A can asibiti an yiwa Qareeba aiki lafiya. Dr Tani kam basu da zabin da ya wuce sedating dinta wato aka sata baccin dole saboda suna so lokacin da zata farka ta ga Qareeba ma ta tashi. Me yiwu wa hakan zai taimaka wurin daidaituwar jinin nata.
Daki daya aka ajiye su zuwa wayewar gari. Dr Auwal sai shabiyun dare ya koma gida. Falon da abin ya afku wanda a waya ya sanar da Maigadi a fadawa maiaikinsu kada ta taba komai da sunan gyara yaje hankalinsa ya tashi haka ya hau sama yana ganin jinin 'yarsa a kasa. Daki gabadaya ya hargitse musamman da yake a nan Dahiru ya yiwa BB duka. Kansa yaji ya soma ciwo ya bar wurin.
Su Najib, matansu da Dr Auwal da sassafe suka koma asibitin. Sun sami Dr Tani tana ta bada order ayi kaza a dauko mata kaza tana tsaye akan Qareeba. Likitocin da nurses sai rokonta suke yi akan ta koma nata gadon ta kwanta zasu kula da Qareeba amma ta ki. Sai ma fada da take yiwa kowa.
"In koma in kwanta ku karasa min yarinya?"
Maigidanta da ta gani ne ta sa kuka murya a shake tace "Daddy ka ga Qareeba taki farkawa tun jiya"
Tausayi ta bashi matuka yasan yadda take bala'in son Qareeba duk cikin 'ya'yanta.
"Zo muje wani dakin ki basu wuri su yi aikinsu. Za ta tashi in sha Allah"
Sai da yayi da gaske ta biyo shi zuwa wani dakin sauran suka tsatstsaya a waje suna jiran bayani game da halin da take ciki. An dade ana bincike har ta fara wata irin jijjiga akan gadon. Can dai aka sake yi mata scanning abin mamaki wani dan karamin gilas ne cikin wanda su ka suke ta ya shige jikinta ya taba kodarta daya. Dole sai an sake yi mata wani aikin. Su Safwan da girmansu su ka rinka kuka yayin da wata nurse take musu bayanin hakan yana faruwa sosai. Aji ciwo da glass ko karfe idan ya karye a jiki yawo yake yi. Zai iya bin duk inda yaso idan anyi rashin sa'a ya taba mahimman sassa ya jiwa mutum mugun rauni.
Dr Tani dagewa tayi ita zata yi aikin tana ta kuka kamar ranta zai fita. Wani azababben ciwon kai ne ya bugeta lokaci guda sai jiri ta fadi a kasa. Gado aka mayar da ita mai yin aikin ya tafi da Qareeba yayin da wasu suka tsaya a kanta.
Iyalan gidan Dr Auwal sun ga abin da basu taba gani ba a wannan rana. Anyi aiki lafiya kafin azahar an fito da ita.
Suna tsaye a kanta ta bude idonta mai lafiyar a hankali tare da motsa hannunta da yake cikin na Dr Tani.
Tana hawaye ta sake riketa tace "Qareeba kalle ni nan, kin gane ni? Mummynki ce"
Baki da ido daya sun suntume da kyar ta iya motsa shi tace "Mummy"
Mahaifinta da 'yan uwa ta rinka bi da ido daya bayan daya tana hawaye. Ina suke lokacin da take ta kiransu da neman agaji. Hannu ta daga ta yafito Dr Auwal ya duka daidai bakinta da kyar tace "Babawo"
Idanunsa sunyi ja sosai yace "na sani Qareeban Daddy bazan barshi ba. Warkewarki kawai nake da bukata"
Dr Tani na kuka tace ina wayarta. Maigidanta ya miko mata tace da su Safwan duk su fita zata yi waya. Kallon juna suka shiga yi kafin su bi umarninta.
Suna fita ta kira Haj Mara. Ringing biyu kamar tana jira ta dauka a lokacin kuma babban wan Dr Tani ya shigo dakin bata da damar katse kiran tunda ya shiga kuma a zuciye take.
Haj Mara kusan kwana tayi tana kiranta dama harda Qareeba babu wanda ya dauka.
"Haba Tani, haba don Allah. Kun daga min hankali ina ta nemanki tun jiya inji ina Babawo yake daga cewa...."
Daga murya Dr Tani tayi irin yadda wani bai taba ji ba cike da masifa tace "dakata min Marakisiyya. Babawon banza, ashe dan naki dan akuya ne dabba mara hankali... "
Gabanta ne ya fadi ba dai yaje ya tafka wata ta'asar ba. Sai kuma bacin rai don bazata taba yin shiru ana zagar mata da ba.
"Tani kinsan da wa ki ke magana kuwa?"
Cikin fada tace "Wacece ke banda macuciya azzaluma. Ni zaki ha'inta ki turo min wannan mahaukacin ya auri Qareeba. To ki saurareni na rantse miki sai naga bayanki da na Babawo"
"Wai meye haka? Me yayi miki?"
"Ashe iskancin nasa na karya ne tunda bai dawo gida ya fada miki ba. Muna asibiti daga jiya zuwa yau anyiwa Qareeba surgery har biyu kinji daya. Yayi mata dukan da ko a film ban taba ganin an yiwa mutum irinsa ba kinji biyu. Ba don tsarewa ta Allah ba sauran kiris ya yi mata fyade kinji uku. Ki tsananta addu'a yarinyata ta shi idan ba haka ba ban ga kudin da kuke dashi da zai hana na rufe danki ba. Idan kin manta 2010 ni ban manta ba. Amma ki sani ta inda aka hau ta nan za'a sauko"
Kashe wayar tayi batare da ta bata damar amsawa ba. Hannu ta dora a ka ta saka kuka. Karo na biyu ana fada mata wannan kalma. Rannan Yasmin ta fada yau Dr Tani. Abu daya ya tsaya mata a rai....Mawadda!
Dr Auwal ne ya kalli matarsa saboda gabadaya ya kasa fahimtar inda ta dosa.
"Me ya faru a 2010 Tani?"
Alh Munzali wan Dr Tani yayi dariya "ashe 'yan boko ma suna boyewa juna sirri"
"Yaya don Allah ka bar maganar nan" kadai ta iya cewa duk da tasan ranar wanka ba'a boyon cibi.
"Fadawa mijinki ba hurumi na bane Tani nazo dubaku ne duk da kin yanke alaka damu saboda sawa ranki da ki ka yi bama kaunarki bama kaunar zuri'arki. Duk wani abu da muke yi miki muna yi ne don gyara son 'ya'ya ya rufe miki ido kin kasa fahimta"
Kujera ta samu ta zauna tana kuka Alh Munzali ya kalli Qareeba yace "Allah Ya baki lafiya Ya saka miki. Fyade ba karshen rayuwa bane zaki cigaba da harkokinki kamar kowa"
Dr Tani ta katse shi "Yaya Munzali baiyi raping dinta ba"
Irin dariyar kin ma raina min hankali yayi kafin yace mata "ko duk jikina kunne ne bazan yarda. Nasan dama dole kiyi kokarin boyewa amma ki sani rufewar ba gata bane. Zan wuce amma zamu dawo anjima tunda na tabbatar da labarin ba jita jita bane"