Sashe 41
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daurewa yayi duk da yana ganin lokaci na kara tafiya ya fada masa wayar Bilya. Murna sosai ya tayashi don ya kula ba karamin so yake yiwa Mawadda ba. Abu ne kuma na gida shiyasa da Dahirun ya nemi ya raka shi yace ba yau ba. Har ya fita ya dawo ya mika masa hannu suka yi musabaha.
Rike da hannun nasa Dahiru yace "nagode kuma kayi hakuri ina ta masifa"
"Its called love babu damuwa. Abu daya ne dai idan ka kwaso mana Anti Qareeba ..."
Fita yayi yana dariya ya tafi gidansa domin ya shirya. Fatansa dai iyayen nasu su taimaka su amince wannan karon kada wani abu ya sake rabasu.
******
Garwashi da yaransa sunyi nasarar zuwa garin Tariwa inda da naira dari biyu suka sami wani mai bakin reza ya kwashe komai da ya sani game dasu Mawadda ya fada musu. Gidan ne kawai bai sani ba a Kano amma yasan na Maigari ne.
******
Mawadda tana kwance a daki Ade ta shiga ta sameta. Tashi tayi da sauri don tasan Ade ta hanata wannan kwanciyar da tunani. Kamar ta sani kuwa Ade tace
"Me na fada miki dazu da na shigo?"
"Kiyi hakuri na tashi yanzu" ta amsa tana gyara katifar da ta kasance tasu ita da Rafi'a a da.
"Dazu me yasa da aka turo tambayar gyaran jiki ki ka sallami yaron wai baki da lafiya? Zaki fara wasa da sana'arki ne saboda damuwa ko me."
Yadda tayi maganar da fushi yasa Mawadda yin kasa da kanta. Bata da wani kuzarin aikin kanta cushe yake da tunanin rayuwarta.
Sakaya kofar Ade tayi kada ace tasa 'yar fari a daki ta sassauta murya
"Ki kara hakuri yadda ki ka saba kinji ko? Ni kaina abin nan ba karamin damuna yake ba amma yaya muka iya da abinda ya gagaremu." Hawaye ne ya taho mata tayi saurin sa gefen dankwalinta sai dai Mawadda ta riga ta gani. Hankalinta yayi matukar tashi kuwa.
"Ade wallahi na dena. Me zan dafa idan kin tafi?" Tace tana bude kofar dakin.
Yau ake kai lefen 'yar Barira kanwar Yaya shiyasa ta fita da wuri. Itama Ade yanzu zata karasa shiryawa su tafi dasu Iya. Mawadda kadai zata rage saboda Baba.
Fara'ar dole ta kirkiro domin kwantarwa mahaifiyarta hankali ta tafi kitchen. Tana fita Ade ta zauna taci kukanta don tasan babu wani abu da zasu iya yi domin kawowa 'yarsu farincikin da kaddara ta shiga tsakaninta dashi.
******
Shabiyu Dahiru ya isa gidan Bilya. Baffa ya gama fadan ya bata musu lokaci yayi ta aikin bada hakuri.
Inna ta kalle shi a ranta ta yaba da yadda 'ya'yanta suka koma. Burinta yanzu akansa ya kare shima ya ajiye iyali kamar 'yan uwansa.
Hansa'u ana ta firirita Dahiru yazo. Abinci ta kawo masa dayake yunwa yake ji yau bai gwaleta ba yaci.
Furaira tace "kana yawo da yunwa har tsakar rana haka ance kayi aure ka zauna shiririta."
"Kai Yaya Furaira kin matsawa Yayanmu Dahiru" cewar Hansa'u tana satar kallonsa.
Inna ta gane ina zancen ya dosa don Furaira ta jima tana maganar a hada Hansa'u da Dahiru aure. Sauya hirar tayi saboda kada su fara rigimar da suka saba.
"Ince ko ka sanar da su Mal Fatihu zamu zo?"
Dafe kai yayi tace ya hanzarta kiran Mawadda ta fada kafin Baffa ya fito daga dakin da suke tattaunawa da Bilya.
Jin an ambaci Mawadda yasa Furaira hade rai "Inna gidansu Mawadda zaku je kuma? Yanzu biye masa zaku yi ya auri yarinyar da ta gama lalata rayuwartaa titi? Idan ma Hansa'u ce bakwa so ba dole amma bai kamata ku barshi ya dauko wadda zata gurbata mana dangi ba"
"Tashi ki bar wurin nan kafin na saba miki" Bilya ya daka mata tsawa yana shiga falon. Ranta a bace ta mike Hansa'u na mara mata baya suka fita.
Inna tace ya rinka hakuri tunda yasan halinta. Dahiru kuma ya fita waje ya kira Mawadda. Wayar tana ringing gabansa yana faduwa kada taki dauka.
Su Ade sun gama shiryawa suna jiran Adaidaita sahu da Marwanu yaje samowa a bakin titi ita kuma tana gyaran salad taji wayar.
Ganin sunan mai kiran ya sanya zuciyarta tsananta bugu. Muryarta ma gabadaya chanjawa tayi kamar wadda tayi gudu tayi masa sallama.
Lumshe idanu yayi yana jin daddadar muryarta tana gaishe shi.
"Yayanmu ko baka ji ne?" Ta fada tana jijjaga wayar.
Ajiyar zuciyarsa taji sannan yace "ina jinki, kin tashi lafiya?"
"Lafiya kalau" tace duk ta kidime da jin muryarsa.
"Zamu zo dasu Inna nan da...ina ganin bazai kai awa ba. Baba yana nan ko?"
"Eh zan sanar dashi"
Kashe wayar tayi ta tashi. Yanzu me zata fadawa Baban. Tana tsoron kada ace ita tace ya kawosu tunda bata san yadda suka kare jiya ba. Ade taje ta fadawa ta hau salati
"Mu da zamu fita? Tsaya na sanar da babanku"
Basu jima ba suka fito tare da kansa ya fadawa su Inna. Mawadda kitchen ta koma Ade tace ta kara abincin. Tana aiki tana ji suna tattaunawa akan amsar da Baba zai bayar idan Mal Isiyaku ya tado da zancen Dahiru. Iya kadai ce tabi mai adaidaita sahun aka bar Ade da Inna.
Biyu saura suka karaso. Mawadda ta sake gyara gida ko'ina yaji turaren wuta. Falonsu na soro a gyare sai kuma dakin Ade inda Inna zata zauna shima da tsakar gidan fes. Hatta abinci, kunun aya da ruwan sanyi duka ta ajiye musu.
Marwanu ne ya yiwa Inna jagora zuwa cikin gidan yayin da Baffa, Bilya da Dahiru suka tsaya a falon tare da Baba.
Tamkar wani abu bai taba hadasu ba Baba ya taso ya tarbe su cikin mutumci da karamci. Haka Innar Fatihu da Ade suka yiwa Inna suma a ciki.
Da Mawadda ta fito gaisheta janyota tayi jikinta kwalla na taruwa a idanunta.
"Allah Sarki 'yata, na rasa me zan ce dake. Kiyi hakuri kinji 'yannan"
Innar Fatihu tace "Haba Indo do Allah banda dawo da hannun agogo baya. Yadda lokaci ya shude haka komai ya wuce. Ziyarar da kuka kawo mana tafi komai a wurinmu"
Ade ta tursasawa Inna cin abinci tace ciwon suga ke damunta bata dade da samun sauki ba shiyasa take tsoron shinkafa.
Wata karamar jaka Ade ta dauko ta ciro kudi ta bawa Mawadda.
"Yi maza ki bawa Marwanu ya siyo cous-cous a bakin titi. Idan baya nan ki hanzarta kije"
"Kai Sa'ade kamar baki ki barshi ba yunwa nake ji ba"
Mawadda tuni ta saka hijabinta mai hannu wanda ya sauko zuwa gwiwarta tayi waje. Tana jin Inna na cewa ai fa dole ne taci.
Kiran Marwanu tayi a waya yace ya tafi gidan Anti Barira. Takalmi ta dauko wasu masu tudu kadan ta saka ta fita. Dahiru yana cikin falon soron kuma inda yake zauna yana fuskantar kofa ya ganta ta wuce da sauri kada su hangota. Tashi yayi yace yana zuwa ya biyo bayanta.
Tana fita daga gidan ya fito shima.
"Ina zaki je?"
Cak ta tsaya har ya iso gefenta ya tsaya.
"Uhmm, uhmm cous-cous zan siyo"
Ya dan bata fuska "da kanki?"
"Marwanu baya nan"
"Tsaya a nan na siyo miki"
"Ka koma ciki zanyi sauri ba nisa sosai"
Yadda ya kalleta yasa ta mika masa kudin. Ko kallonsu baiyi ba ya wuceta ya shige mota ya ja. Tafiyar da tasan da ita ce a kafa zata kai har yanzu bata isa titin ba shi da yaje a mota sai gashi ya dawo cikin 'yan mintuna.
Mamaki ya bata ganin ya dauko katan guda ta bude baki tana kallonsa har ya iso bakin kofar gidan inda take tsaye.
Murmushi yayi ganin tana ta kallon ikon Allah ita da zata siyo kwali daya shi ya dauko katan
"Rufe bakin mana Kanwarmu"
Kamar tayi masa kuka tace "Yayanmu me zance idan na shiga da wannan?"
"Aikena ki ka yi shiyasa baki dade ba mana"
Turo baki tayi "kasan ba haka nake nufi ba"
Jingina bayansa yayi da bango a gefenta sannan ya juya kansa bangaren da take. Shashantar da zancen yayi don ba hirar katan din cous-cous yake so suyi ba.
"Wane irin so nake yi miki ne? Komai naki ina so harda wannan tura bakin"
Daburcewa tayi ta shiga tura katan iya karfinta saboda kunyar da taji. A nan waje ta barshi yana mata dariya ta tura shi kitchen ta dafa rabin kwali daya ta kaiwa Inna.
A falo su Baba suna hirar yaushe gamo inda Baffa ya roke shi da ya yafe masa abinda ya faru a Tariwa.
"Fitar maganar nan daga gidana ne sai na kasa zama aboki nagari nima na biyewa sauran jama'a"
"Kada muyi haka da kai mana Mal.Isiyaku. Kaddara ai ba'a guje mata. Ni dai don Allah mu bar zancen nan. Zumunci yafi komai gashi kazo har gidana me zance banda godiya?"
Bilya taya Baffa bada hakuri yayi Baba yace shi dai a bar tada tsohon zance baya so.
Baffa yace da Bilya "ina kaninka ne?"
Shima dayake yaga fitar Mawadda dazu sai yayi murmushi kawai "ina jin iska ya fita sha"
Sun cigaba da hirarsu Mawadda kuma ta koma daki. Zamanta ke da wuya Dahiru ya kira. Kai ta girgiza kafin ta dauka.
"Ki fito muyi hira"
Kamar yana gabanta ta zaro idanu "Da wa? Rufa min asiri"
"So nake naji yaya kika kwana jiya?"
Zancen jiyan take ta gudu don bata son tunawa ma.
"Lafiya kalau"
"Kizo na ganki na tabbatar"
"Ba yanzu ka ganni ba?"
"Aikena fa kika yi daga fitowata"
Yana ji tana dariya kasa-kasa.
"Ina mota ni kadai bana son hirar manya. Ke da nake son taki hirar kuma kina ja min aji. Bari kawai na kira Anti Qareeba" yace a kalar tausayi.
Dariya yaji ta sake yi ya shiga bata labarin haduwarsu ta gidan mai jiya. Mawadda sai da ta koma rufe bakinta kada a jiyo ta. Yayin da shi kuma yaji ransa ya sake gabadaya babu sauran damuwa tunda ya sakata farinciki.
*****
Sai da suka yi la'asar suka fara haramar tafiya saboda a ranar zasu koma Tariwa. Bilya ne ya fara fita Baffa ya danyi gyaran murya Baba ya kalle shi.
"Mal Fatihu game da yaran nan..."
Baba yace "munyi magana da Dahiru jiya nace ya hakura mu cigaba da zumuncinmu"
Rike da hannun nasa Dahiru yace "nagode kuma kayi hakuri ina ta masifa"
"Its called love babu damuwa. Abu daya ne dai idan ka kwaso mana Anti Qareeba ..."
Fita yayi yana dariya ya tafi gidansa domin ya shirya. Fatansa dai iyayen nasu su taimaka su amince wannan karon kada wani abu ya sake rabasu.
******
Garwashi da yaransa sunyi nasarar zuwa garin Tariwa inda da naira dari biyu suka sami wani mai bakin reza ya kwashe komai da ya sani game dasu Mawadda ya fada musu. Gidan ne kawai bai sani ba a Kano amma yasan na Maigari ne.
******
Mawadda tana kwance a daki Ade ta shiga ta sameta. Tashi tayi da sauri don tasan Ade ta hanata wannan kwanciyar da tunani. Kamar ta sani kuwa Ade tace
"Me na fada miki dazu da na shigo?"
"Kiyi hakuri na tashi yanzu" ta amsa tana gyara katifar da ta kasance tasu ita da Rafi'a a da.
"Dazu me yasa da aka turo tambayar gyaran jiki ki ka sallami yaron wai baki da lafiya? Zaki fara wasa da sana'arki ne saboda damuwa ko me."
Yadda tayi maganar da fushi yasa Mawadda yin kasa da kanta. Bata da wani kuzarin aikin kanta cushe yake da tunanin rayuwarta.
Sakaya kofar Ade tayi kada ace tasa 'yar fari a daki ta sassauta murya
"Ki kara hakuri yadda ki ka saba kinji ko? Ni kaina abin nan ba karamin damuna yake ba amma yaya muka iya da abinda ya gagaremu." Hawaye ne ya taho mata tayi saurin sa gefen dankwalinta sai dai Mawadda ta riga ta gani. Hankalinta yayi matukar tashi kuwa.
"Ade wallahi na dena. Me zan dafa idan kin tafi?" Tace tana bude kofar dakin.
Yau ake kai lefen 'yar Barira kanwar Yaya shiyasa ta fita da wuri. Itama Ade yanzu zata karasa shiryawa su tafi dasu Iya. Mawadda kadai zata rage saboda Baba.
Fara'ar dole ta kirkiro domin kwantarwa mahaifiyarta hankali ta tafi kitchen. Tana fita Ade ta zauna taci kukanta don tasan babu wani abu da zasu iya yi domin kawowa 'yarsu farincikin da kaddara ta shiga tsakaninta dashi.
******
Shabiyu Dahiru ya isa gidan Bilya. Baffa ya gama fadan ya bata musu lokaci yayi ta aikin bada hakuri.
Inna ta kalle shi a ranta ta yaba da yadda 'ya'yanta suka koma. Burinta yanzu akansa ya kare shima ya ajiye iyali kamar 'yan uwansa.
Hansa'u ana ta firirita Dahiru yazo. Abinci ta kawo masa dayake yunwa yake ji yau bai gwaleta ba yaci.
Furaira tace "kana yawo da yunwa har tsakar rana haka ance kayi aure ka zauna shiririta."
"Kai Yaya Furaira kin matsawa Yayanmu Dahiru" cewar Hansa'u tana satar kallonsa.
Inna ta gane ina zancen ya dosa don Furaira ta jima tana maganar a hada Hansa'u da Dahiru aure. Sauya hirar tayi saboda kada su fara rigimar da suka saba.
"Ince ko ka sanar da su Mal Fatihu zamu zo?"
Dafe kai yayi tace ya hanzarta kiran Mawadda ta fada kafin Baffa ya fito daga dakin da suke tattaunawa da Bilya.
Jin an ambaci Mawadda yasa Furaira hade rai "Inna gidansu Mawadda zaku je kuma? Yanzu biye masa zaku yi ya auri yarinyar da ta gama lalata rayuwartaa titi? Idan ma Hansa'u ce bakwa so ba dole amma bai kamata ku barshi ya dauko wadda zata gurbata mana dangi ba"
"Tashi ki bar wurin nan kafin na saba miki" Bilya ya daka mata tsawa yana shiga falon. Ranta a bace ta mike Hansa'u na mara mata baya suka fita.
Inna tace ya rinka hakuri tunda yasan halinta. Dahiru kuma ya fita waje ya kira Mawadda. Wayar tana ringing gabansa yana faduwa kada taki dauka.
Su Ade sun gama shiryawa suna jiran Adaidaita sahu da Marwanu yaje samowa a bakin titi ita kuma tana gyaran salad taji wayar.
Ganin sunan mai kiran ya sanya zuciyarta tsananta bugu. Muryarta ma gabadaya chanjawa tayi kamar wadda tayi gudu tayi masa sallama.
Lumshe idanu yayi yana jin daddadar muryarta tana gaishe shi.
"Yayanmu ko baka ji ne?" Ta fada tana jijjaga wayar.
Ajiyar zuciyarsa taji sannan yace "ina jinki, kin tashi lafiya?"
"Lafiya kalau" tace duk ta kidime da jin muryarsa.
"Zamu zo dasu Inna nan da...ina ganin bazai kai awa ba. Baba yana nan ko?"
"Eh zan sanar dashi"
Kashe wayar tayi ta tashi. Yanzu me zata fadawa Baban. Tana tsoron kada ace ita tace ya kawosu tunda bata san yadda suka kare jiya ba. Ade taje ta fadawa ta hau salati
"Mu da zamu fita? Tsaya na sanar da babanku"
Basu jima ba suka fito tare da kansa ya fadawa su Inna. Mawadda kitchen ta koma Ade tace ta kara abincin. Tana aiki tana ji suna tattaunawa akan amsar da Baba zai bayar idan Mal Isiyaku ya tado da zancen Dahiru. Iya kadai ce tabi mai adaidaita sahun aka bar Ade da Inna.
Biyu saura suka karaso. Mawadda ta sake gyara gida ko'ina yaji turaren wuta. Falonsu na soro a gyare sai kuma dakin Ade inda Inna zata zauna shima da tsakar gidan fes. Hatta abinci, kunun aya da ruwan sanyi duka ta ajiye musu.
Marwanu ne ya yiwa Inna jagora zuwa cikin gidan yayin da Baffa, Bilya da Dahiru suka tsaya a falon tare da Baba.
Tamkar wani abu bai taba hadasu ba Baba ya taso ya tarbe su cikin mutumci da karamci. Haka Innar Fatihu da Ade suka yiwa Inna suma a ciki.
Da Mawadda ta fito gaisheta janyota tayi jikinta kwalla na taruwa a idanunta.
"Allah Sarki 'yata, na rasa me zan ce dake. Kiyi hakuri kinji 'yannan"
Innar Fatihu tace "Haba Indo do Allah banda dawo da hannun agogo baya. Yadda lokaci ya shude haka komai ya wuce. Ziyarar da kuka kawo mana tafi komai a wurinmu"
Ade ta tursasawa Inna cin abinci tace ciwon suga ke damunta bata dade da samun sauki ba shiyasa take tsoron shinkafa.
Wata karamar jaka Ade ta dauko ta ciro kudi ta bawa Mawadda.
"Yi maza ki bawa Marwanu ya siyo cous-cous a bakin titi. Idan baya nan ki hanzarta kije"
"Kai Sa'ade kamar baki ki barshi ba yunwa nake ji ba"
Mawadda tuni ta saka hijabinta mai hannu wanda ya sauko zuwa gwiwarta tayi waje. Tana jin Inna na cewa ai fa dole ne taci.
Kiran Marwanu tayi a waya yace ya tafi gidan Anti Barira. Takalmi ta dauko wasu masu tudu kadan ta saka ta fita. Dahiru yana cikin falon soron kuma inda yake zauna yana fuskantar kofa ya ganta ta wuce da sauri kada su hangota. Tashi yayi yace yana zuwa ya biyo bayanta.
Tana fita daga gidan ya fito shima.
"Ina zaki je?"
Cak ta tsaya har ya iso gefenta ya tsaya.
"Uhmm, uhmm cous-cous zan siyo"
Ya dan bata fuska "da kanki?"
"Marwanu baya nan"
"Tsaya a nan na siyo miki"
"Ka koma ciki zanyi sauri ba nisa sosai"
Yadda ya kalleta yasa ta mika masa kudin. Ko kallonsu baiyi ba ya wuceta ya shige mota ya ja. Tafiyar da tasan da ita ce a kafa zata kai har yanzu bata isa titin ba shi da yaje a mota sai gashi ya dawo cikin 'yan mintuna.
Mamaki ya bata ganin ya dauko katan guda ta bude baki tana kallonsa har ya iso bakin kofar gidan inda take tsaye.
Murmushi yayi ganin tana ta kallon ikon Allah ita da zata siyo kwali daya shi ya dauko katan
"Rufe bakin mana Kanwarmu"
Kamar tayi masa kuka tace "Yayanmu me zance idan na shiga da wannan?"
"Aikena ki ka yi shiyasa baki dade ba mana"
Turo baki tayi "kasan ba haka nake nufi ba"
Jingina bayansa yayi da bango a gefenta sannan ya juya kansa bangaren da take. Shashantar da zancen yayi don ba hirar katan din cous-cous yake so suyi ba.
"Wane irin so nake yi miki ne? Komai naki ina so harda wannan tura bakin"
Daburcewa tayi ta shiga tura katan iya karfinta saboda kunyar da taji. A nan waje ta barshi yana mata dariya ta tura shi kitchen ta dafa rabin kwali daya ta kaiwa Inna.
A falo su Baba suna hirar yaushe gamo inda Baffa ya roke shi da ya yafe masa abinda ya faru a Tariwa.
"Fitar maganar nan daga gidana ne sai na kasa zama aboki nagari nima na biyewa sauran jama'a"
"Kada muyi haka da kai mana Mal.Isiyaku. Kaddara ai ba'a guje mata. Ni dai don Allah mu bar zancen nan. Zumunci yafi komai gashi kazo har gidana me zance banda godiya?"
Bilya taya Baffa bada hakuri yayi Baba yace shi dai a bar tada tsohon zance baya so.
Baffa yace da Bilya "ina kaninka ne?"
Shima dayake yaga fitar Mawadda dazu sai yayi murmushi kawai "ina jin iska ya fita sha"
Sun cigaba da hirarsu Mawadda kuma ta koma daki. Zamanta ke da wuya Dahiru ya kira. Kai ta girgiza kafin ta dauka.
"Ki fito muyi hira"
Kamar yana gabanta ta zaro idanu "Da wa? Rufa min asiri"
"So nake naji yaya kika kwana jiya?"
Zancen jiyan take ta gudu don bata son tunawa ma.
"Lafiya kalau"
"Kizo na ganki na tabbatar"
"Ba yanzu ka ganni ba?"
"Aikena fa kika yi daga fitowata"
Yana ji tana dariya kasa-kasa.
"Ina mota ni kadai bana son hirar manya. Ke da nake son taki hirar kuma kina ja min aji. Bari kawai na kira Anti Qareeba" yace a kalar tausayi.
Dariya yaji ta sake yi ya shiga bata labarin haduwarsu ta gidan mai jiya. Mawadda sai da ta koma rufe bakinta kada a jiyo ta. Yayin da shi kuma yaji ransa ya sake gabadaya babu sauran damuwa tunda ya sakata farinciki.
*****
Sai da suka yi la'asar suka fara haramar tafiya saboda a ranar zasu koma Tariwa. Bilya ne ya fara fita Baffa ya danyi gyaran murya Baba ya kalle shi.
"Mal Fatihu game da yaran nan..."
Baba yace "munyi magana da Dahiru jiya nace ya hakura mu cigaba da zumuncinmu"