Sashe 57
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani abun idan yayi har mamaki take wai Dahirunta ne tun na da can ko kuwa. Komai yayi burgeta yake yi shiyasa idan ya fita sai taji kamar bata da lafiya. Wani dan tunani tayi ta tashi zaune da sauri tana ture shi.
"Me kuma nayi yanzu?"
Bata rai tayi "wallahi ba haka ake yi ba Yayanmu"
"Har yanzu ban fara yi miki yadda ake yiwa amaren bane?" Ya fada yana kamota.
"Ni ka kyaleni bana so"
Muryarsa da take matukar so mai tayar mata da tsigar jiki ya sake ragewa yana turmurmusata "Uhm uhmm ni ina so"
Hawaye ne ya digo mata dama ta iya saurin kuka "ya zaka rinka yi min hakane?"
Ganin abin nata na gaske ne ya dena wasan ya zama serious "what is wrong?"
"A iya sanina mata ne suke shagwaba amma tunda nazo gidan nan kullum kaine kake yi duk ka tare komai. To ni me zanyi don Allah" ta fada tana ware hannuwanta tayi kicin kicin da fuska.
Sai da yayi dariya mai isarsa har ta kule ta fara kai masa duka yana karewa yana cigaba da dariyar yace "idan nayi ki rarrasheni"
"Haka akeyi dama?"
"A gidan Dahiru da Mawadda ba" ya riko hannayenta da take kokarin dukansa dasu.
Kwafa tayi tace "har fa huduba aka yi min akan na rinka maka"
Cikin tausayawa yace "Allah sarki kice a baki wata satar amsar wannan dai na riga bari ma ki gani"
Zillewa ta soma yi ya kankameta suka kwanta yana dariya tana masa kukan shagwaba.
"Iyyeee ashe kin iya, kara sautin muji"
Rasa yadda zatayi dashi tayi duk abinda tayi sai ya mayar na tsokana. Wayarta ce ta soma ringing ya miko mata. Sunan Nawal ta gani amma muryar Attahir.
Muryarsa ta nuna yana cikin damuwa yace "Mawadda ina Dahiru?"
Kansa a cinyarta sai shige mata yake ta kasa magana da kyar tace "gashi nan"
Ajiyar zuciya yayi "bashi please"
Wayar ta dora masa akan kunne ya hada da hannunta ya rike. Attahir yace "dadinta dai nima ina da tawa matar amma Allah sai na rama. Kace karfe biyar zamu fita amma gashi shida saura kwata ina ta waya baka dauka"
Sai lokacin ya tuna wayarsa na falo. Attahir yana ta mita ya rinka dariya yana bashi hakuri. Idan yana tare da Mawadda baya sanin lokaci ya ja sosai.
Kafin ya ajiye wayar Attahir yace "kuma sai na fadawa Yaya Bilya me ka tsaya yi"
Kashewa Mawadda ido yayi ta kawar da kai tana murmushi yace "me nayi"
"Abinda zuciyarka ta raya maka" ya amsa da shakiyanci.
Jikin Mawadda ya sake makalewa ya sassauta "kai Attahir har kasa naji kunya"
Attahir ya hau salati "shikenan Dahiru ya lalace"
"Muka lalace dai"
Mawadda ta juyo da sauri ya dora hannu akan bakinsa yana duka sannan ya cewa Attahir ya bashi minti goma yana zuwa.
Kaya ta dauko masa yadi mara nauyi sky blue da hula mai fari da blue itama. Yana shiryawa yace mata shi dai baya son fitar ko yace musu sai gobe.
"Idan ka fasa ma bazan zauna a gidan ba saboda munyi fada"
Turare take fesa masa suke maganar ya karbi kwalbar ya ajiye "duk kin tayar da kwantacciyar soyayya zaki koreni. Haka zan tafi kina yi min gizo"
Kunya ce ta kamata ta rufe ido ya juyata tana kallon madubin.
A daidai kunnenta yace "bude ido ki tayani ganin matata"
Kanta ta kalla ta ba kanta dariya. Dahiru na bayanta yayi kyau sosai ita kuwa kayan jikinta duk sun gama yamutsewa saboda yadda ya tumurmusata akan gadon. Gashin kanta ya fita daga cikin ribbon din shima ya baje ko ina.
"Ji yadda ka mayar dani kamar sabon kamu"
"Sababbin kamu dai....amma na kin gane" ya kashe ido yana rike da hannunta suka je falo.
"Kije kasa bana son ki zauna kiyi ta tunani na kewata na damunki"
"Wai ni yaushe ka zama haka ne?"
"Tun lokacin da na fara ganinki. Sani ne bakiyi ba. Hmm bari naje kada mu tsinci Attahir a bakin kofa"
Bakin kofar kasa ta raka shi zai fita ta riko hannunsa "i will miss you"
"I know"
Ya saka idonsa cikin nata ta runtse nata da sauri. Hannu yasa a bayan kanta ya matso da ita ya shiga kissing dinta kamar wanda za'a kwace masa ita. Horn Attahir yayi da karfi ta ture shi ba shiri ya fita.
Yasha tsiya a mota tun yana ramawa har ya kama bakinsa ya tsuke don duk bakin da yayi yanzu still Attahir ya dama shi ya shanye.
******
*Kwana biyu da suka wuce*
Kamar ta durkusa a gaban mutanen biyu don magiya da roko. Fito da kudin da bata san adadinsu tayi ba.
"Bobo ga wannan ka bashi kuma na rantse idan ya fito min da Babawo a yau zan kara masa"
Bobo aminin BB wanda a gidansa aka ajiye Mawadda lokacin da suka sato ta. Mahaifinsa babba ne a gwamnati ya taso cikin gata da sangarta kamar BB din. A halin yanzu iyayensa ko keyarsa basa son gani saboda abubuwan kunya da ya jawo musu a unguwa da gari. Shiyasa ya karasa kangarewa duk abinda yasan zaiyi karshe ya komawa iyayensa baya bata lokaci wurin aiwatarwa kawai don ya bakanta musu. Uwa uba BB baisan zafin kudi ba yana sakar masa sosai.
Haj Mara da taimakon kofur Pascal wanda ta jika da kudi ta sami damar ganin BB shine ya bata numbar Bobo yace ta neme shi su fitar dashi.
Sunyi iya yinsu sun rasa hanyar kubutar dashi suka rasa mafitar da ta wuce hada baki da Kofur Pascal.
Kudaden hannunsa ya shafa yaji da nauyi ko da bai kirga ba.
"Hajiya kada ki damu. Nayi miki alkawarin zaki dauki yaronki ku tafi"
Wani abu da ya jima akan kirjinta taji ya sauka. Mutumin da ta bawa miliyan uku domin yayi musu visa ya bace a doron kasa don kuwa ta neme shi ta rasa. Kudaden hannunta sunyi mugun kasa amma bazata karaya ba. Idan Babawo ya fito sai su koma wani garin da zama. Zata ja masa kunne akan mata ko ta sami wata yar masu karamin karfin ta aura masa kowa ya huta.
Sun gama tsarin komai don Bobo master planner ne. Ko satar Mawadda shi ya kawo idea din yadda za'ayi. Wannan karon ma ya baje basirarsa ta kulle kulle kamar wata mace.
*4:07pm Police Station*
Kofur Pascal yana ganin abokan aikinsa mutum uku da suke teburin karbar korafi na farko da an shigo station din sun bingere da bacci ya kira Bobo yace ya shirya idan komai ya tafi daidai yanzu BB zai fito domin kamar yadda ya fada musu an shiga meeting akan case din wasu barayi. Sa'arsu daya cell din BB shine na farko ana shiga kuma an raba shi da Danmani saboda dukan da yake masa ko da an hukunta shi. Bude shi yayi ya fito sai wari yake ga ciwukan jikinsa jini ya bushe ya dankare. Da sauri sauri suka fito saboda yana kallo security dinsu ya zaga bandaki saboda murdawar ciki a dalilin abinda ya saka masa a fura.
Suna fitowa inda wadancan ke bacci guda cikinsu ashe baccin baiyi nisa ba amma bashi da kuzarin daga koda yatsa sai dai ya ga fitar BB da Pascal wanda ya kawo musu youghurt mai sanyi da aka sakawa maganin bacci.
A guje Bobo ya fizgi mota suka bar wurin shi kuma Pascal ya koma ya kwanta cikinsu kafin su DPO su fito daga meeting.
Ruwa da abinci wanda Haj Mara ta bada domin yaci kafin su iso inda zaa dauketa su wuce Kaduna ta tattare abinda zata iya su nausa kudu Bobo ya bashi. Kamar tsohon maye haka ya ringa gabzar abincin nan ko taunawa babu. Sai da yaji cikinsa kamar zai fashe yayi wata muguwar gyatsa.
Idanu a kekashe bayan Bobo ya gama yi masa bayanin komai yace "bazan bar garin nan ba sai na lahanta munafukin nan da ya aure min mata. Ko baccin kirki bana iyawa saboda tunanin suna can suna cin amanata"
Dariyar mugunta Bobo yayi "nasan zaka bukaci hakan BB shiyasa rannan nazo station din na bi bayansa bayan Pascal da ya fito da kai ya tabbatar min shine mijinta. To cut the story kit nasan gidansu"
"Muje gidan Bobo"
"What? Yanzun nan? Haba ka bari kaje wurin Hajiyarka idan an natsa kwana biyu ka dawo muje a gabansa wallahi ayi mata aiki"
"Idan banje yau ba bacin rai sai ya kasheni kafin 'yan sanda. Muje da wannan kazamin jikin a gaban idonsa ka daure min shi ya ga yadda ake nunawa mace soyayya"
Tafawa suka yi Bobo ya karkata mota sai unguwar Rijiyar zaki. Suna zuwa gidan Attahir da Dahiru suna fita. Gilashin motar Dahiru saboda tint ne sai suka yi zaton Mawadda tana baya suka shiga binsu har gate din gidan Dr Auwal. Ciki suka shiga da motar su BB suka jira a waje don yau sai ya wulalanta Mawadda da mijinta zaiji dadi. Haj Mara tana ta bugo wayar Bobo amma BB yace kada ya dauka bata plan zata yi.
*******
Da rawar jiki Dr Tani ta fito bakin nan har kunne tana ta murmushi.
"Menene haka 'ya'yana zaku tsaya daga waje. Ku shigo nan gidanku ne ku ba baki bane"
Murmushi suka yi a tare suka bi bayanta. Bayan sun gaisa ta tashi da kanta kawo musu abin sha sai bare-bare take bata son abinda zata batawa Dahiru yanzu ko kadan kuwa. Yaron yana burgeta inama nata ne ko mijin 'yarta.
Tana kawo musu ta tafi kiran Qareeba wai tazo sun zo dubata ne.
Itama da sauri ta tashi Dr Tani tace "yi hankali cikinki bai gama warkewa ba"
"To Mummy zabar mim kayan da zan saka"
Murmushin Dr Tani ya fadada ta dauko mata wani hadadden material ta saka. Fuska tasha kwalliya tana zuba kamshi suka fito tare.
"AHIRIIIINNN" tace tana saukowa baki bude.
"Anti Qareebaaaa" shima ya fada yadda tayi suna dariya shi da Attahir wanda sai lokacin ta kula dashi.
"Attashir ashe tare kuke"
"Eh wallahi Antinmu yaya karfin jiki?"
Sun gama gaisawa a mutumce suna dan taba hira Bilya ya kira yace ya iso dama cewa yayi zaizo da motarsa saboda yana da uzuri daga nan.
"Me kuma nayi yanzu?"
Bata rai tayi "wallahi ba haka ake yi ba Yayanmu"
"Har yanzu ban fara yi miki yadda ake yiwa amaren bane?" Ya fada yana kamota.
"Ni ka kyaleni bana so"
Muryarsa da take matukar so mai tayar mata da tsigar jiki ya sake ragewa yana turmurmusata "Uhm uhmm ni ina so"
Hawaye ne ya digo mata dama ta iya saurin kuka "ya zaka rinka yi min hakane?"
Ganin abin nata na gaske ne ya dena wasan ya zama serious "what is wrong?"
"A iya sanina mata ne suke shagwaba amma tunda nazo gidan nan kullum kaine kake yi duk ka tare komai. To ni me zanyi don Allah" ta fada tana ware hannuwanta tayi kicin kicin da fuska.
Sai da yayi dariya mai isarsa har ta kule ta fara kai masa duka yana karewa yana cigaba da dariyar yace "idan nayi ki rarrasheni"
"Haka akeyi dama?"
"A gidan Dahiru da Mawadda ba" ya riko hannayenta da take kokarin dukansa dasu.
Kwafa tayi tace "har fa huduba aka yi min akan na rinka maka"
Cikin tausayawa yace "Allah sarki kice a baki wata satar amsar wannan dai na riga bari ma ki gani"
Zillewa ta soma yi ya kankameta suka kwanta yana dariya tana masa kukan shagwaba.
"Iyyeee ashe kin iya, kara sautin muji"
Rasa yadda zatayi dashi tayi duk abinda tayi sai ya mayar na tsokana. Wayarta ce ta soma ringing ya miko mata. Sunan Nawal ta gani amma muryar Attahir.
Muryarsa ta nuna yana cikin damuwa yace "Mawadda ina Dahiru?"
Kansa a cinyarta sai shige mata yake ta kasa magana da kyar tace "gashi nan"
Ajiyar zuciya yayi "bashi please"
Wayar ta dora masa akan kunne ya hada da hannunta ya rike. Attahir yace "dadinta dai nima ina da tawa matar amma Allah sai na rama. Kace karfe biyar zamu fita amma gashi shida saura kwata ina ta waya baka dauka"
Sai lokacin ya tuna wayarsa na falo. Attahir yana ta mita ya rinka dariya yana bashi hakuri. Idan yana tare da Mawadda baya sanin lokaci ya ja sosai.
Kafin ya ajiye wayar Attahir yace "kuma sai na fadawa Yaya Bilya me ka tsaya yi"
Kashewa Mawadda ido yayi ta kawar da kai tana murmushi yace "me nayi"
"Abinda zuciyarka ta raya maka" ya amsa da shakiyanci.
Jikin Mawadda ya sake makalewa ya sassauta "kai Attahir har kasa naji kunya"
Attahir ya hau salati "shikenan Dahiru ya lalace"
"Muka lalace dai"
Mawadda ta juyo da sauri ya dora hannu akan bakinsa yana duka sannan ya cewa Attahir ya bashi minti goma yana zuwa.
Kaya ta dauko masa yadi mara nauyi sky blue da hula mai fari da blue itama. Yana shiryawa yace mata shi dai baya son fitar ko yace musu sai gobe.
"Idan ka fasa ma bazan zauna a gidan ba saboda munyi fada"
Turare take fesa masa suke maganar ya karbi kwalbar ya ajiye "duk kin tayar da kwantacciyar soyayya zaki koreni. Haka zan tafi kina yi min gizo"
Kunya ce ta kamata ta rufe ido ya juyata tana kallon madubin.
A daidai kunnenta yace "bude ido ki tayani ganin matata"
Kanta ta kalla ta ba kanta dariya. Dahiru na bayanta yayi kyau sosai ita kuwa kayan jikinta duk sun gama yamutsewa saboda yadda ya tumurmusata akan gadon. Gashin kanta ya fita daga cikin ribbon din shima ya baje ko ina.
"Ji yadda ka mayar dani kamar sabon kamu"
"Sababbin kamu dai....amma na kin gane" ya kashe ido yana rike da hannunta suka je falo.
"Kije kasa bana son ki zauna kiyi ta tunani na kewata na damunki"
"Wai ni yaushe ka zama haka ne?"
"Tun lokacin da na fara ganinki. Sani ne bakiyi ba. Hmm bari naje kada mu tsinci Attahir a bakin kofa"
Bakin kofar kasa ta raka shi zai fita ta riko hannunsa "i will miss you"
"I know"
Ya saka idonsa cikin nata ta runtse nata da sauri. Hannu yasa a bayan kanta ya matso da ita ya shiga kissing dinta kamar wanda za'a kwace masa ita. Horn Attahir yayi da karfi ta ture shi ba shiri ya fita.
Yasha tsiya a mota tun yana ramawa har ya kama bakinsa ya tsuke don duk bakin da yayi yanzu still Attahir ya dama shi ya shanye.
******
*Kwana biyu da suka wuce*
Kamar ta durkusa a gaban mutanen biyu don magiya da roko. Fito da kudin da bata san adadinsu tayi ba.
"Bobo ga wannan ka bashi kuma na rantse idan ya fito min da Babawo a yau zan kara masa"
Bobo aminin BB wanda a gidansa aka ajiye Mawadda lokacin da suka sato ta. Mahaifinsa babba ne a gwamnati ya taso cikin gata da sangarta kamar BB din. A halin yanzu iyayensa ko keyarsa basa son gani saboda abubuwan kunya da ya jawo musu a unguwa da gari. Shiyasa ya karasa kangarewa duk abinda yasan zaiyi karshe ya komawa iyayensa baya bata lokaci wurin aiwatarwa kawai don ya bakanta musu. Uwa uba BB baisan zafin kudi ba yana sakar masa sosai.
Haj Mara da taimakon kofur Pascal wanda ta jika da kudi ta sami damar ganin BB shine ya bata numbar Bobo yace ta neme shi su fitar dashi.
Sunyi iya yinsu sun rasa hanyar kubutar dashi suka rasa mafitar da ta wuce hada baki da Kofur Pascal.
Kudaden hannunsa ya shafa yaji da nauyi ko da bai kirga ba.
"Hajiya kada ki damu. Nayi miki alkawarin zaki dauki yaronki ku tafi"
Wani abu da ya jima akan kirjinta taji ya sauka. Mutumin da ta bawa miliyan uku domin yayi musu visa ya bace a doron kasa don kuwa ta neme shi ta rasa. Kudaden hannunta sunyi mugun kasa amma bazata karaya ba. Idan Babawo ya fito sai su koma wani garin da zama. Zata ja masa kunne akan mata ko ta sami wata yar masu karamin karfin ta aura masa kowa ya huta.
Sun gama tsarin komai don Bobo master planner ne. Ko satar Mawadda shi ya kawo idea din yadda za'ayi. Wannan karon ma ya baje basirarsa ta kulle kulle kamar wata mace.
*4:07pm Police Station*
Kofur Pascal yana ganin abokan aikinsa mutum uku da suke teburin karbar korafi na farko da an shigo station din sun bingere da bacci ya kira Bobo yace ya shirya idan komai ya tafi daidai yanzu BB zai fito domin kamar yadda ya fada musu an shiga meeting akan case din wasu barayi. Sa'arsu daya cell din BB shine na farko ana shiga kuma an raba shi da Danmani saboda dukan da yake masa ko da an hukunta shi. Bude shi yayi ya fito sai wari yake ga ciwukan jikinsa jini ya bushe ya dankare. Da sauri sauri suka fito saboda yana kallo security dinsu ya zaga bandaki saboda murdawar ciki a dalilin abinda ya saka masa a fura.
Suna fitowa inda wadancan ke bacci guda cikinsu ashe baccin baiyi nisa ba amma bashi da kuzarin daga koda yatsa sai dai ya ga fitar BB da Pascal wanda ya kawo musu youghurt mai sanyi da aka sakawa maganin bacci.
A guje Bobo ya fizgi mota suka bar wurin shi kuma Pascal ya koma ya kwanta cikinsu kafin su DPO su fito daga meeting.
Ruwa da abinci wanda Haj Mara ta bada domin yaci kafin su iso inda zaa dauketa su wuce Kaduna ta tattare abinda zata iya su nausa kudu Bobo ya bashi. Kamar tsohon maye haka ya ringa gabzar abincin nan ko taunawa babu. Sai da yaji cikinsa kamar zai fashe yayi wata muguwar gyatsa.
Idanu a kekashe bayan Bobo ya gama yi masa bayanin komai yace "bazan bar garin nan ba sai na lahanta munafukin nan da ya aure min mata. Ko baccin kirki bana iyawa saboda tunanin suna can suna cin amanata"
Dariyar mugunta Bobo yayi "nasan zaka bukaci hakan BB shiyasa rannan nazo station din na bi bayansa bayan Pascal da ya fito da kai ya tabbatar min shine mijinta. To cut the story kit nasan gidansu"
"Muje gidan Bobo"
"What? Yanzun nan? Haba ka bari kaje wurin Hajiyarka idan an natsa kwana biyu ka dawo muje a gabansa wallahi ayi mata aiki"
"Idan banje yau ba bacin rai sai ya kasheni kafin 'yan sanda. Muje da wannan kazamin jikin a gaban idonsa ka daure min shi ya ga yadda ake nunawa mace soyayya"
Tafawa suka yi Bobo ya karkata mota sai unguwar Rijiyar zaki. Suna zuwa gidan Attahir da Dahiru suna fita. Gilashin motar Dahiru saboda tint ne sai suka yi zaton Mawadda tana baya suka shiga binsu har gate din gidan Dr Auwal. Ciki suka shiga da motar su BB suka jira a waje don yau sai ya wulalanta Mawadda da mijinta zaiji dadi. Haj Mara tana ta bugo wayar Bobo amma BB yace kada ya dauka bata plan zata yi.
*******
Da rawar jiki Dr Tani ta fito bakin nan har kunne tana ta murmushi.
"Menene haka 'ya'yana zaku tsaya daga waje. Ku shigo nan gidanku ne ku ba baki bane"
Murmushi suka yi a tare suka bi bayanta. Bayan sun gaisa ta tashi da kanta kawo musu abin sha sai bare-bare take bata son abinda zata batawa Dahiru yanzu ko kadan kuwa. Yaron yana burgeta inama nata ne ko mijin 'yarta.
Tana kawo musu ta tafi kiran Qareeba wai tazo sun zo dubata ne.
Itama da sauri ta tashi Dr Tani tace "yi hankali cikinki bai gama warkewa ba"
"To Mummy zabar mim kayan da zan saka"
Murmushin Dr Tani ya fadada ta dauko mata wani hadadden material ta saka. Fuska tasha kwalliya tana zuba kamshi suka fito tare.
"AHIRIIIINNN" tace tana saukowa baki bude.
"Anti Qareebaaaa" shima ya fada yadda tayi suna dariya shi da Attahir wanda sai lokacin ta kula dashi.
"Attashir ashe tare kuke"
"Eh wallahi Antinmu yaya karfin jiki?"
Sun gama gaisawa a mutumce suna dan taba hira Bilya ya kira yace ya iso dama cewa yayi zaizo da motarsa saboda yana da uzuri daga nan.