Sashe 62
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sharewa Mawadda hawaye Nawal tayi ta tayar da ita tsaye. Manyan suna gaba suka yi tururuwar shiga dakin.
Idanun Dahiru akan kofa yana nemanta. Ita kuwa daga karshe ta tsaya tana zubar hawaye da fargabar yadda zata ganshi.
Suna hada ido ya sakar mata wani lallausan murmushi a take taji hawayen nata har sunfi na da. Qareeba ta kama hannunta ta janyota gaban gadon tana yi mata radar da kowa yake ji.
"Kanwata ba'a haka. Mijinki yana kwance yanzu ya kamata ki nuna masa kulawa yadda ya kamata ba ki tsaya a baya kina rabe-rabe ba"
Tun daga Bilya har su Nawal babu wanda baiji kunya ba musamman Mawadda da aka fadawa. Danlami dariya ya rinka yi kasa-kasa. Manyan kuma sai suka dauke kai kamar basu ji ba. Dr Tani dai tamkar kasa ta dare ta shige haka taji. Daukar 'yarta zatayi su tafi kafin ta saida hali kowa ya gane wacece Qareeban Dr Tani.
Sun gaisa da Dahiru ana tambayarsa jikinsa yace da sauki. Mawadda ce kawai bata yi magana ba sai ruwan hawayen da yake daga masa hankali.
Bayan dan lokaci Baba yace zasu koma gida kada su rasa abin hawa.
"Haba Mal Fatihu yaushe zamu bari ku fita neman abin hawa" cewar Baba Prof.
"Hanyarmu ta baude ne bana son dora muku nauyi"
Baba Prof yace babu matsala Attahir ya daukesu a motarsa.
Bilya yace zai tafi dasu. Shi kuma Attahir ya tambaya ko ya kai Mawadda da Nawal gidan Baba Prof sai ya dawo ya kwana.
"Ji min wani abu. Mutum da matarsa kace zaka yi jinyarsa. Ka daukesu ku koma ita Mawadda ta dauko musu abubuwan bukata na kwana kai kuma sai mu wuce gida da Nawal kafin a kama dan iskan yaron nan"
Maimakon su tafi sai hira ta koma kan BB da bakin halinsa. Da zasu tafi Ade, Yaya da Baba aka ce su shiga motar Bilya Danlami su Baba Prof suka ce ya jira su tafi a motarsu sai a ajiye shi a hanya.
Duka suka fito sai 'yan sanda biyu sannan aka ce daya ya bi su Attahir tunda gidan zasu koma daukar kaya.
Qareeba tayi saurin biyo su Mawadda dama motar tasu tana kusa da ta Bilya. Dr Tani tace ina zata je ga tasu motar.
"Kanwata zan raka dauko kaya kinga har yanzu bata da nutsuwa"
Janyota baya tayi da sauri basu san Bilya yana cikin motarsa ba ya gama waya da Baffa ya fada masa komai.
"Bana son wannan rawar kan Qareeba don Allah ki ja mutumcinki ki wuce mu tafi"
Ta bata rai "Mummy ba a yiwa dangin miji haka. Idan banyi kokari mun saba da ita tun yanzu ba ko anyi auren ba zata saki jiki dani ba."
Toshe mata baki Dr Tani tayi tana waige "shashasha anyi auren ne ko me? Maza ki cigaba da wannan bare-baren shima yace ya fasa. Dazu ko kunyar idon mutane kika hau sakin baki"
Turbune fuska sosai Qareeba tayi "yanzu Mummy meye laifina? Wallahi ina son Bilyamin to don ina son samarwa kaina wuri a zuciyarsa sai ya zama rawar kai? Su fa maza akan 'yan uwansu basa ji basa gani"
Wannan karon haba Dr Tani ta rike cike da mamakin Qareebar "you are just unbelievable Qareeba. Ni kike fadawa me ya kamata da dangin miji?"
"To Mummy kowa yasan tsakaninki da 'yan uwan Daddy fa. Ni kuma ina so su Ahirin su so ni kuma su so 'ya'yana"
Maganarta gaskiya ce shiyasa Dr Tani ta kasa cewa komai. Bilya da ya gama sauraronsu sai yaji ta sake burge shi yayi murmushi shi kadai.
Duka aka watse Attahir ya kai Mawadda ta dauko kaya da abinci suka dawo da ita. Zai sake shiga ciki bayan ya tayata diban kaya ya kai Nawal ta rike masa hannu. Ya fahimci dai nufinta a kyalesu shiyasa suka yi mata sai da safe suka wuce.
******
A hankali ta tura kofar dakin ta shiga. Dahiru yana kwance idanunsa a rufe kamar mai bacci. Kayan hannunta ta ajiye sauran duka Attahir ya shiga dasu. Ta koma gefen gadon ta tsaya tana kallon shi cike da so da tausayi.
Banda gocewar kashin gwiwar hannunsa ta kalla wanda take nade da bandeji saboda muguwar daujewa da wurin yayi. Ga kuma gefen idonsa na hagu da plasta shima yaji ciwo. A hankali ta tako zuwa bakin gadon ta kura masa ido tana zubar da hawaye.
Sautin kukanta a hankali yake shiga kunnuwansa yana taba masa zuciya. Bude idanunsa yayi ya sauke a kanta tana ganin ya tashi ta fada jikinsa ta kankame shi iya karfinta.
"Nayi zaton na rasa ka. Idan ka tafi ka barni nima mutuwa zanyi. Yayanmu ka yafe min a dalilina ka ke ta ganin bacin rai gashi yau harda lafiyarka an taba...."
Dago fuskarta yayi idanunta sun kankance saboda kuka "kada ki sake cewa a dalilinki ne domin duk abinda ya shafeki ya shafemu ne gabadaya"
Murmushi tayi ga hawaye na zuba "kai komai naka daban yake"
"Sosai kuwa. Shiyasa ma banyi korafi ba kinzo kin cika min kunne da kuka da surutu babu yaya jiki ko sannu"
Rungumarsa yaji ta sake yi tana dariya a hankali "ba sai nace yaya jiki ba saboda nima ina jin ciwon yadda kake jinsa"
"Mawaddana mai dadin baki. Idan anzo allura sai mu raba kenan"
"Ni na hakura ayi maka kai kadai saboda ka samu sauki da wuri"
Sai da ta sashi dariyar da baiyi niyya ba saboda jikinsa ya fara tsami ko ina ciwo yake masa. Sallah yace zaiyi ta dauko ruwa da bokiti ta taimaka masa yayi alwala a wurin sannan yayi sallolinsa akan gadon. Ita ma tayi isha ta bashi abinci. Kadan ya iya ci yace ya koshi. Fita tayi da sauran abincin wurin masu shara ta taho tare da nurse aka cire masa ruwan da ya kare aka sa wani. Har sandunan tafiya aka kawo masa ko da zai bukaci tashi.
Shirin bacci suka yi ta kula ya zurfafa a tunani wanda tasan bazai wuce na BB ba. Kashe fitilar dakin tayi ta dawo kusa dashi akan gadon "matsa min"
"Gadon mara lafiyan?"
Ta zauna tana riko hannunsa "baka ganeni bane? Matar patient ce tazo raba jinya da patient dinta"
Tasan yana cikin damuwa shiyasa take kokarin kwantar masa da hankali duk da itama nata hankalin ba a kwance yake ba.
"Ni dai gaskiya ki kwanta a waccan kujerar zata isheki."
"Yayanmu mana don Allah" tace tana bubbuga kafa a kasa.
Matsawa yayi yana murmushi. "shagwababbiya kawai"
"Zama da kai ne"
"Saura ki fama min kafata"
"Saura ka danneni garin juyi"
Kansa yana daga wurin kirjinta don ya bar mata filon ya zame jikinsa kasa kadan yace "yaushe kika koyi surutu ne?"
Fuskarsa ta dago tace "saka min kayi"
Muryarsa a shake yace "yaushe?"
"Ranar da ka fara wannan..." ta amsa masa tare da kissing dinsa.
Ba don rashin lafiyarsa ba da ta ga tukwicin wannan kulawa da yasan da biyu take masa kamar yadda shima yake yi mata idan tana da damuwa. A hankali bacci ya kwashesu tana rungume dashi.
Can cikin dare ta soma jin zafin jikinsa yana shirgarta. Tana bude ido ta shafa kansa da wuya sunyi zafi sosai. Kusan fadowa tayi daga kan gadon don sauri ta fita neman likita. Zazzabi yake mai zafi da azababben ciwon kai. Allurai da magunguna aka bashi tana gefe tana kuka har suka gama.
"Wannan fever da headache din are normal. Ya bugu sosai amma in sha Allah zuwa safiya zai fara jin saukin jikin"
Godiya tayi masa tana share hawaye. Zama tayi tana ta masa sannu tun yana amsawa da kyar har bacci ya daukeshi. Ita kanta sace ta yayi ba don taso ba tana rike da hannunsa.
******
A can gidan Kawun Haj Mara kuwa Bobo ne ya kirata a waya ya sanar da ita sun iso. Unguwar babu wuta amma an tada inji a gidan gashi dama yana da girma bari-bari ginin gargajiya inda wasu 'ya'yansa suke zaune da iyalansu. Dakatar dasu tayi a waje ta je ta sanar da kawun nata an sako BB saboda bincike ya nuna sharri aka yi masa. Ko kallonta baiyi ba yace tace su shigo sai ya kwana a dakin samarin gidan amma da safe yana so su tafi saboda shi baya son harkar 'yan sanda. Maganar ta bata mata rai amma bata da wata mafita da ta wuce kwana a gidansa shiyasa bata mayar masa da baka ba.
Tana fita ta ga BB a jikin Bobo yayi mankas ko tsayuwa baya iyawa. Kirji ta dafe a tsorace "kai Boiboi a buge yake ne?"
"Hajiya Bobo nake fa. Ya dan kurba ne ya wanke yawa. Yau yarinyar nan ta kwafsa mana amma ai jikin mijinta ya fada idan bai mutu ba kenan"
A fusace ta janyo BB har yana faduwa ta wanka masa mari tana hakin bacin rai "Babawo bazaka barni na huta ba ashe? Me kuka sake aikatawa kuma?"
Bobo da ya fara jin kansa a sama shima saboda ya sha rabin kwalba shine yayi mata bayani sannan ya shige motarsa yayi gaba. Mayafinta ta cire ta lullube BB tana kukan bakinciki. Maimakon dakin samarin inda akayi mata masauki ta wuce dashi saboda bata son kowa ya ganshi a wannan yanayin. Suna shiga ta kama kofa ta rufe harda saka sakata ta warbar dashi akan katifa ta koma gefe ta tsaya tana share hawaye.
Tafiya ta jiyo alamun ana tahowa hanyar dakin ta saki labule da sauri. A sannan kuma BB ya fara tari ta saka hannu ta rufe masa baki. Ai yana jin hannun ya mika nasa ya shafa yaji alamun mace kawai ya shiga kokawar danneta. Tun tana mutsu-mutsu a hankali har ta ga abin ba na hankali bane ya fara cire nasa kayan.
Duk da duhun dakin ta lalubi kumatunsa ta tsinka masa mari "kai don ubanka nice, Hajiyarka ce"
Yadda idanuwansa suka rufe haka kunnuwansa suka toshe. Mawadda yake tunani da yadda yaso kwarai yau ya sameta. Haj Mara bata yi aune ba ya soma tafkarta yana mari da duka yana mata fadan taci amanarsa tunda ta auri waninsa. Kayanta ya shiga yagawa a haukace.
Idanun Dahiru akan kofa yana nemanta. Ita kuwa daga karshe ta tsaya tana zubar hawaye da fargabar yadda zata ganshi.
Suna hada ido ya sakar mata wani lallausan murmushi a take taji hawayen nata har sunfi na da. Qareeba ta kama hannunta ta janyota gaban gadon tana yi mata radar da kowa yake ji.
"Kanwata ba'a haka. Mijinki yana kwance yanzu ya kamata ki nuna masa kulawa yadda ya kamata ba ki tsaya a baya kina rabe-rabe ba"
Tun daga Bilya har su Nawal babu wanda baiji kunya ba musamman Mawadda da aka fadawa. Danlami dariya ya rinka yi kasa-kasa. Manyan kuma sai suka dauke kai kamar basu ji ba. Dr Tani dai tamkar kasa ta dare ta shige haka taji. Daukar 'yarta zatayi su tafi kafin ta saida hali kowa ya gane wacece Qareeban Dr Tani.
Sun gaisa da Dahiru ana tambayarsa jikinsa yace da sauki. Mawadda ce kawai bata yi magana ba sai ruwan hawayen da yake daga masa hankali.
Bayan dan lokaci Baba yace zasu koma gida kada su rasa abin hawa.
"Haba Mal Fatihu yaushe zamu bari ku fita neman abin hawa" cewar Baba Prof.
"Hanyarmu ta baude ne bana son dora muku nauyi"
Baba Prof yace babu matsala Attahir ya daukesu a motarsa.
Bilya yace zai tafi dasu. Shi kuma Attahir ya tambaya ko ya kai Mawadda da Nawal gidan Baba Prof sai ya dawo ya kwana.
"Ji min wani abu. Mutum da matarsa kace zaka yi jinyarsa. Ka daukesu ku koma ita Mawadda ta dauko musu abubuwan bukata na kwana kai kuma sai mu wuce gida da Nawal kafin a kama dan iskan yaron nan"
Maimakon su tafi sai hira ta koma kan BB da bakin halinsa. Da zasu tafi Ade, Yaya da Baba aka ce su shiga motar Bilya Danlami su Baba Prof suka ce ya jira su tafi a motarsu sai a ajiye shi a hanya.
Duka suka fito sai 'yan sanda biyu sannan aka ce daya ya bi su Attahir tunda gidan zasu koma daukar kaya.
Qareeba tayi saurin biyo su Mawadda dama motar tasu tana kusa da ta Bilya. Dr Tani tace ina zata je ga tasu motar.
"Kanwata zan raka dauko kaya kinga har yanzu bata da nutsuwa"
Janyota baya tayi da sauri basu san Bilya yana cikin motarsa ba ya gama waya da Baffa ya fada masa komai.
"Bana son wannan rawar kan Qareeba don Allah ki ja mutumcinki ki wuce mu tafi"
Ta bata rai "Mummy ba a yiwa dangin miji haka. Idan banyi kokari mun saba da ita tun yanzu ba ko anyi auren ba zata saki jiki dani ba."
Toshe mata baki Dr Tani tayi tana waige "shashasha anyi auren ne ko me? Maza ki cigaba da wannan bare-baren shima yace ya fasa. Dazu ko kunyar idon mutane kika hau sakin baki"
Turbune fuska sosai Qareeba tayi "yanzu Mummy meye laifina? Wallahi ina son Bilyamin to don ina son samarwa kaina wuri a zuciyarsa sai ya zama rawar kai? Su fa maza akan 'yan uwansu basa ji basa gani"
Wannan karon haba Dr Tani ta rike cike da mamakin Qareebar "you are just unbelievable Qareeba. Ni kike fadawa me ya kamata da dangin miji?"
"To Mummy kowa yasan tsakaninki da 'yan uwan Daddy fa. Ni kuma ina so su Ahirin su so ni kuma su so 'ya'yana"
Maganarta gaskiya ce shiyasa Dr Tani ta kasa cewa komai. Bilya da ya gama sauraronsu sai yaji ta sake burge shi yayi murmushi shi kadai.
Duka aka watse Attahir ya kai Mawadda ta dauko kaya da abinci suka dawo da ita. Zai sake shiga ciki bayan ya tayata diban kaya ya kai Nawal ta rike masa hannu. Ya fahimci dai nufinta a kyalesu shiyasa suka yi mata sai da safe suka wuce.
******
A hankali ta tura kofar dakin ta shiga. Dahiru yana kwance idanunsa a rufe kamar mai bacci. Kayan hannunta ta ajiye sauran duka Attahir ya shiga dasu. Ta koma gefen gadon ta tsaya tana kallon shi cike da so da tausayi.
Banda gocewar kashin gwiwar hannunsa ta kalla wanda take nade da bandeji saboda muguwar daujewa da wurin yayi. Ga kuma gefen idonsa na hagu da plasta shima yaji ciwo. A hankali ta tako zuwa bakin gadon ta kura masa ido tana zubar da hawaye.
Sautin kukanta a hankali yake shiga kunnuwansa yana taba masa zuciya. Bude idanunsa yayi ya sauke a kanta tana ganin ya tashi ta fada jikinsa ta kankame shi iya karfinta.
"Nayi zaton na rasa ka. Idan ka tafi ka barni nima mutuwa zanyi. Yayanmu ka yafe min a dalilina ka ke ta ganin bacin rai gashi yau harda lafiyarka an taba...."
Dago fuskarta yayi idanunta sun kankance saboda kuka "kada ki sake cewa a dalilinki ne domin duk abinda ya shafeki ya shafemu ne gabadaya"
Murmushi tayi ga hawaye na zuba "kai komai naka daban yake"
"Sosai kuwa. Shiyasa ma banyi korafi ba kinzo kin cika min kunne da kuka da surutu babu yaya jiki ko sannu"
Rungumarsa yaji ta sake yi tana dariya a hankali "ba sai nace yaya jiki ba saboda nima ina jin ciwon yadda kake jinsa"
"Mawaddana mai dadin baki. Idan anzo allura sai mu raba kenan"
"Ni na hakura ayi maka kai kadai saboda ka samu sauki da wuri"
Sai da ta sashi dariyar da baiyi niyya ba saboda jikinsa ya fara tsami ko ina ciwo yake masa. Sallah yace zaiyi ta dauko ruwa da bokiti ta taimaka masa yayi alwala a wurin sannan yayi sallolinsa akan gadon. Ita ma tayi isha ta bashi abinci. Kadan ya iya ci yace ya koshi. Fita tayi da sauran abincin wurin masu shara ta taho tare da nurse aka cire masa ruwan da ya kare aka sa wani. Har sandunan tafiya aka kawo masa ko da zai bukaci tashi.
Shirin bacci suka yi ta kula ya zurfafa a tunani wanda tasan bazai wuce na BB ba. Kashe fitilar dakin tayi ta dawo kusa dashi akan gadon "matsa min"
"Gadon mara lafiyan?"
Ta zauna tana riko hannunsa "baka ganeni bane? Matar patient ce tazo raba jinya da patient dinta"
Tasan yana cikin damuwa shiyasa take kokarin kwantar masa da hankali duk da itama nata hankalin ba a kwance yake ba.
"Ni dai gaskiya ki kwanta a waccan kujerar zata isheki."
"Yayanmu mana don Allah" tace tana bubbuga kafa a kasa.
Matsawa yayi yana murmushi. "shagwababbiya kawai"
"Zama da kai ne"
"Saura ki fama min kafata"
"Saura ka danneni garin juyi"
Kansa yana daga wurin kirjinta don ya bar mata filon ya zame jikinsa kasa kadan yace "yaushe kika koyi surutu ne?"
Fuskarsa ta dago tace "saka min kayi"
Muryarsa a shake yace "yaushe?"
"Ranar da ka fara wannan..." ta amsa masa tare da kissing dinsa.
Ba don rashin lafiyarsa ba da ta ga tukwicin wannan kulawa da yasan da biyu take masa kamar yadda shima yake yi mata idan tana da damuwa. A hankali bacci ya kwashesu tana rungume dashi.
Can cikin dare ta soma jin zafin jikinsa yana shirgarta. Tana bude ido ta shafa kansa da wuya sunyi zafi sosai. Kusan fadowa tayi daga kan gadon don sauri ta fita neman likita. Zazzabi yake mai zafi da azababben ciwon kai. Allurai da magunguna aka bashi tana gefe tana kuka har suka gama.
"Wannan fever da headache din are normal. Ya bugu sosai amma in sha Allah zuwa safiya zai fara jin saukin jikin"
Godiya tayi masa tana share hawaye. Zama tayi tana ta masa sannu tun yana amsawa da kyar har bacci ya daukeshi. Ita kanta sace ta yayi ba don taso ba tana rike da hannunsa.
******
A can gidan Kawun Haj Mara kuwa Bobo ne ya kirata a waya ya sanar da ita sun iso. Unguwar babu wuta amma an tada inji a gidan gashi dama yana da girma bari-bari ginin gargajiya inda wasu 'ya'yansa suke zaune da iyalansu. Dakatar dasu tayi a waje ta je ta sanar da kawun nata an sako BB saboda bincike ya nuna sharri aka yi masa. Ko kallonta baiyi ba yace tace su shigo sai ya kwana a dakin samarin gidan amma da safe yana so su tafi saboda shi baya son harkar 'yan sanda. Maganar ta bata mata rai amma bata da wata mafita da ta wuce kwana a gidansa shiyasa bata mayar masa da baka ba.
Tana fita ta ga BB a jikin Bobo yayi mankas ko tsayuwa baya iyawa. Kirji ta dafe a tsorace "kai Boiboi a buge yake ne?"
"Hajiya Bobo nake fa. Ya dan kurba ne ya wanke yawa. Yau yarinyar nan ta kwafsa mana amma ai jikin mijinta ya fada idan bai mutu ba kenan"
A fusace ta janyo BB har yana faduwa ta wanka masa mari tana hakin bacin rai "Babawo bazaka barni na huta ba ashe? Me kuka sake aikatawa kuma?"
Bobo da ya fara jin kansa a sama shima saboda ya sha rabin kwalba shine yayi mata bayani sannan ya shige motarsa yayi gaba. Mayafinta ta cire ta lullube BB tana kukan bakinciki. Maimakon dakin samarin inda akayi mata masauki ta wuce dashi saboda bata son kowa ya ganshi a wannan yanayin. Suna shiga ta kama kofa ta rufe harda saka sakata ta warbar dashi akan katifa ta koma gefe ta tsaya tana share hawaye.
Tafiya ta jiyo alamun ana tahowa hanyar dakin ta saki labule da sauri. A sannan kuma BB ya fara tari ta saka hannu ta rufe masa baki. Ai yana jin hannun ya mika nasa ya shafa yaji alamun mace kawai ya shiga kokawar danneta. Tun tana mutsu-mutsu a hankali har ta ga abin ba na hankali bane ya fara cire nasa kayan.
Duk da duhun dakin ta lalubi kumatunsa ta tsinka masa mari "kai don ubanka nice, Hajiyarka ce"
Yadda idanuwansa suka rufe haka kunnuwansa suka toshe. Mawadda yake tunani da yadda yaso kwarai yau ya sameta. Haj Mara bata yi aune ba ya soma tafkarta yana mari da duka yana mata fadan taci amanarsa tunda ta auri waninsa. Kayanta ya shiga yagawa a haukace.