Sashe 23
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata guda Iya tayi kai kace haihuwa ko amarya akayi a gidan. Innar Fatihu da Ade suka zabura suna kallonta ta murmusa sannan ta nuna musu wurin da Mawadda ta tashi.
"Allah Maji rokon bawanSa Yaga zuciyata da irin du'a'in da nake yi kada Ya jarabcemu da goya dan gaba da Fatiha. Ga shaida idona ya gani iftila'in Mawadda bai hada da ciki a dalilin fyaden nan ba"
Ade ta ma manta da abu makamancin wannan bata taba tunani ba akan zai iya yiwuwa fa ciki ya shiga. Wani sanyi itama taji ya ratsa zuciyarta tayi hamdala sannan ta bi bayan Mawadda tace mata ta gyara jikinta don ta lura tunani yayi mata yawa bata san dashi ba.
Innar Fatihu ta tashi ta shiga rumfar maigidanta wurinsa. Yana jingine da bango ya dafe kai yana aikin tunani.
"Fatihu fada min gaskiya ya kuka yi da yaron nan."
Jiki a sanyaye ya fada mata ta shiga tafa hannuwa.
"Amma sun bani mamaki sosai. Nasan ko nice da wuya na amince amma irin haka da sosa rai. Nagode Allah yarinyar nan ba da amincewar ta akayi ba da bansan yadda zamuyi da ranmu a garin nan ba"
******
A fusace Baffa yake ta doka sallama Inna ta saki rariyar da take tankade da sauri saboda tsoro.
"Menene?" ta fada tana mikewa sai kuma ta kula da Dahiru tasa fuskar tayi kalar tausayi harda guntun hawaye a idonsa.
"Kai kuma daga ina?"
"Ki jawa yaron nan kunne ina daf da nuna masa bacin rai mai tsanani. Ta yaya za'ayi naje nayiwa Mal Fatihu magana akan yarinyarsa mun gama yankewa a bar zancen aure danki ya rinka zagayawa ta baya. Wato ace gani mugun uba dana ya fini tausayi ko. To baka isa ba, in ba aure kake so nayi maka gobe goben nan ba kuma na soke karatu a Kanon ka shiga taitayinka"
Inna ta harari Dahiru sannan tace "kayi hakuri Baffa. Yanzu dai fada min me ya yi"
Cikin daga murya ya bata labari don ransa a bace yake. Inna kuwa hannu tasa ta tsinke Dahiru da mari. Tsabar mamaki ya hana shi kuka sai kallon iyayensa da yake yi wani iri. Ya kasa gano meye laifinsa don yace bazai guji masoyiyarsa a wannan lokacin da take bukatar karuwar masoya da masu nuna mata kulawa ba.
Muryar Inna ce ta dawo dashi daga tunaninsa "Dahiru kada kayi abinda zamuyi fushi da kai kana jina ko. An fada maka da ka muka yanke shawarar fasa auren naku? Wannan zamani na cututtuka idan ta shafa maka kanjamau waye da asara? Kuma muna nan galau bamu sani ba kila da ciki a jikinta a ganganda ayi aure a yaba maka dan jaraba"
Kwalla yaji ta taru a idonsa har yana zafi kamar yadda ransa ke yake yi. Ji yake kamar yasa ihu yayi musu bayanin da zasu gamsu. To amma iyaye da girmansu da darajar da Allah Ya basu bazai iya ba.
"Inna, Baffa kuyi hakuri don Allah. Auren nan idan anyi dama ina da niyar kaita ayi mata gwaje-gwaje sannan in taimaka mata yadda zata ji saukin bakincikin da yake ranta ne"
Baffa ya mike kamar ya rufe shi da duka "dan zaman naka a Kano ne yasa kake tunanin ka fimu wayo da sanin ya kamata? Idan baka yi hankali ba na fada maka karatun ma sai a hakura ka dawo gabanmu ka zauna...shashashan yaro ana ga yaki kana ga kura"
Inna tabe baki tayi "duk abin nan kila ma shiryowa tayi tazo ta fada kai kuma ka hau ka zauna. Idan karya take yi fa bariki ce ta kare mata shine ta dawo ayi auren ka rufa mata asiri fa"
Hawayensa ne ya sakko ya kalleta a sanyaye yace "Innaaaa!"
Jikinta ne yayi sanyi yayin da Baffa ya dauki bota ya shige bayan gida.
Abinci tayi masa tayi yace ya koshi kawai ya mike
"zan koma a satin nan zamu fara shiga aji"
"Allah Ya bada sa'a Ya shi albarka. Ungo maza ka tashi ka tafi zan taushi mahaifinka kafin ka sake dawowa"
Zaninta ta dan kwance daga gefe ta hado masa dubu biyu da dari bakwai ta bashi. Karba yayi yasa a aljihu tare da godiya duk da fuskarsa babu annuri ko kadan.
Haka ya juya ko ruwa bai sha ba Inna tana ta masa addua har kofar gida. Yana jin ta koma ya dawo soronsu ya tsaya yaci kukansa sannan ya share ido. Yana son iyayensa amma baiji dadin matakin nan da suka dauka ba sai dai zaiyi hakuri ya barwa Allah ikonSa.
*****
Haj Mara yau tayi bacci harda minshari tamkar an gama shari'ar an basu gaskiya. Juyi tayi akan makeken gadonta don jiya daga kotu gida suka wuto abinsu.
Wayarta ta janyo ta kira Alh Sule cikin isa da kasaita tace "da baka sa hannu ka nuna damuwarka akan danka ba me ya ci mu Alhaji? Na kira ne kawai nayi maka albishir da cewa kiris ya rage mu sami nasara mu baiwa marada kunya"
"Ni kike fadawa haka Marakisiyya?"
"Da 'yan hamayya nake wadanda basu damu da halin da 'ya'yansu suke ciki ba. Ko kana cikinsu ne?" Tayi masa tambayar rainin hankali tana 'yar dariya.
Murmushin takaici yayi "bana cikinsu gaskiya domin ni ina nan ina addu'a akan Allah Ya fitar min da dana idan yana da gaskiya idan kuma shi mai laifi ne Ya fitarwa wadanda aka zalunta hakkinsu"
Kafin ta ankare ta bashi amsa ya kashe wayar. Kallonta ta rinka yi rai na kuna tana ayyana yadda zata rama idan ya dawo.
Shima a nasa bangaren yana bakincikin yadda neman kudi yasa shi sakar mata ragamar gidan. Yayi babbar sa'a sauran yaransu mata babu wata mai mugun hali ko ace miji ya kawo kararta. Ita Haj Mara din ma arzikinsa da ta ga yana ta habbaka ne yasa ta kara kwallafa rai akan tilon namijin nasu ta sangarta shi har ya kai matakin da tankwara shi zaiyi matukar wahala.
Mikewa tayi zata shiga wanka BB ya shigo dakin nata ba ko sallama yana muzurai.
"Babawo lafiyarka kuwa?"
"Ras nake Hajjaju mutan Makka da Madina. Wai yane....?"
Kasa cewa komai ma tayi jin yadda yake mata magana. Gashi kamar yasha wani abu. Da kyar ta iya cewa
"Me kake nema ne?"
"Ke muka yi magana kika ce min idan na fadi abinda kika sani yarinyar nan Mawadda kamar kin aura min ita kin gama ne kuma gashi har mun taho ko iyayenta baki nema ba"
"Bansan rashin hankalin naka ya kai nan ba. Ta yaya za'ayi nayi musu magana ba'a gama shari'a ba? Ka bari a kare komai mana ka ga iya gudun ruwana"
Hade rai yayi yana kunkuni "to ni dai kada ayi min solo don ba yarda zanyi ba na fada miki tun wuri."
Daga haka ya fita tayi saurin sakawa kofarta mukulli don tsoro ma ya bata.
*****
Dr Tani ta wuni a asibiti tana gyara duk wani report na Mawadda. Wadancan na gaskiyar ta sa wani masinja ya dauko mata ainihin file din ta bashi kudi sannan ta tura a jakarta. Nan ta zauna ta sake komai da taimakon masinjan ta buga sababbin takardu da suka dace da kwanan watan wadancan. Tana aikin tana tausayawa BB domin ba karamin abu bane ace anyiwa mutum sharrin fyade.
Wayarsu ta dazu da Haj Mara ta dada tayar mata da hankali inda tace mata ko ruwa baya iya sha zabgegen namiji kamarsa wai jiya har kuka yayi mata da suka dawo yana cewa rayuwarsa tazo karshe wace mace ce zata taba aurensa. Cikin lallashi Dr Tani tace ta bashi hakuri ta san duk wannan tashin hankalin nasa akan Qareeba ne kuma alkawari ne tayi masa kamar anyi aure an gama tsakaninsu.
Kwafa tayi a hankali tana jin tsanar su Mawadda. Tunda take ita dai tasan 'yarta ba mummuna bace gata fara amma samari basa wuce zuwa uku idan sun kai zuciya nesa suke zukewa a nemesu a rasa. 'Ya'yan nata duka sunki aurowa saboda yanayinsu. Ita kuma hakan bai taba damunta ba balle ta gane sokoncinsu yake hanasu aure. Murnar samun BB a matsayin suruki yasa komai aka fada mata take hawa ta zauna daram.
Sai da ta gama gyara komai ta tafi gida gabanin magariba.
Dahiru yana zaune a kan benci a kofar gidan ya nisa cikin tunani wani yaro da baifi shekara hudu ba ya taho kan titin gidajen wurin yana buga ball. Dr Tani ta taho ga duhu ya kawo kai saura kadan ta buge shi Dahiru ya tashi a guje ya dauke yaron har yana faduwa.
Kanta ta zuro ta taga tace masa "don tsabar wulakanci me ya hanaka dauke yaron tun da na karyo kwana?"
Batare da ya saki yaron ba yace "Hajiya kiyi hakuri"
Tsaki ta doka ta shige bayan maigadi ya bude mata gate.
Shi kuma Dahiru ya fuskanci yaron.
"Assha ba dai kaji ciwo ba ko, daga ina kake?"
"Nan gidan" ya nuna wani gida da tun zuwansa ya kula aikin gininsa ake yi.
"Shine zaka fito kai kadai kana buga kwallo akan titi. To wuce muje ka shiga ciki kuma idan na sake ganin kafarka a wajen nan sai na yanketa."
Yaro yayi kwalkwal da idanu "da wuka ko reza?"
Dahiru ya dan murmusa. Shi tsorata yaron yayi niyar yi saboda ba karamin ganganci bane fitowar tasa "da almakashi zan yanke nasan yafi zafi. Idan zaka yi wasanka kayi a cikin gida banda titi kaji ko"
"Naji sakeni na tafi to.." yaro ya fada duk ya tsure.
"A'a sai na kaika har ciki nace a zaneka kana fita titi"
Wani mutum da yake jinsu daga gefen gate din gidan da ake aikin sanye da 'yar shara ne ya fito yadda zasu ganshi sosai. Yaron ya ruga wurinsa shi kuma Dahiru yana ganin haka yayi zaton ko maigadin gidan ne.
"Baba don Allah a rinka kulawa da amana. Kaga da bana kusa yau da karshen aikinka yazo idan da tsautsayi"
Mutumin ya gimtse dariyarsa yace "Allah dannan me ya faru?"
Dahiru ya sanar dashi duk da cewa akan idonsa akayi komai. Shima da sauri ya biyo bayan jikan nasa sai dai kafin ya iso ya tsallaka titin.
"Zan kiyaye in sha Allahu. A nan kake ne?"
"Eh ina aiki a gidan can ne."
"Allah Maji rokon bawanSa Yaga zuciyata da irin du'a'in da nake yi kada Ya jarabcemu da goya dan gaba da Fatiha. Ga shaida idona ya gani iftila'in Mawadda bai hada da ciki a dalilin fyaden nan ba"
Ade ta ma manta da abu makamancin wannan bata taba tunani ba akan zai iya yiwuwa fa ciki ya shiga. Wani sanyi itama taji ya ratsa zuciyarta tayi hamdala sannan ta bi bayan Mawadda tace mata ta gyara jikinta don ta lura tunani yayi mata yawa bata san dashi ba.
Innar Fatihu ta tashi ta shiga rumfar maigidanta wurinsa. Yana jingine da bango ya dafe kai yana aikin tunani.
"Fatihu fada min gaskiya ya kuka yi da yaron nan."
Jiki a sanyaye ya fada mata ta shiga tafa hannuwa.
"Amma sun bani mamaki sosai. Nasan ko nice da wuya na amince amma irin haka da sosa rai. Nagode Allah yarinyar nan ba da amincewar ta akayi ba da bansan yadda zamuyi da ranmu a garin nan ba"
******
A fusace Baffa yake ta doka sallama Inna ta saki rariyar da take tankade da sauri saboda tsoro.
"Menene?" ta fada tana mikewa sai kuma ta kula da Dahiru tasa fuskar tayi kalar tausayi harda guntun hawaye a idonsa.
"Kai kuma daga ina?"
"Ki jawa yaron nan kunne ina daf da nuna masa bacin rai mai tsanani. Ta yaya za'ayi naje nayiwa Mal Fatihu magana akan yarinyarsa mun gama yankewa a bar zancen aure danki ya rinka zagayawa ta baya. Wato ace gani mugun uba dana ya fini tausayi ko. To baka isa ba, in ba aure kake so nayi maka gobe goben nan ba kuma na soke karatu a Kanon ka shiga taitayinka"
Inna ta harari Dahiru sannan tace "kayi hakuri Baffa. Yanzu dai fada min me ya yi"
Cikin daga murya ya bata labari don ransa a bace yake. Inna kuwa hannu tasa ta tsinke Dahiru da mari. Tsabar mamaki ya hana shi kuka sai kallon iyayensa da yake yi wani iri. Ya kasa gano meye laifinsa don yace bazai guji masoyiyarsa a wannan lokacin da take bukatar karuwar masoya da masu nuna mata kulawa ba.
Muryar Inna ce ta dawo dashi daga tunaninsa "Dahiru kada kayi abinda zamuyi fushi da kai kana jina ko. An fada maka da ka muka yanke shawarar fasa auren naku? Wannan zamani na cututtuka idan ta shafa maka kanjamau waye da asara? Kuma muna nan galau bamu sani ba kila da ciki a jikinta a ganganda ayi aure a yaba maka dan jaraba"
Kwalla yaji ta taru a idonsa har yana zafi kamar yadda ransa ke yake yi. Ji yake kamar yasa ihu yayi musu bayanin da zasu gamsu. To amma iyaye da girmansu da darajar da Allah Ya basu bazai iya ba.
"Inna, Baffa kuyi hakuri don Allah. Auren nan idan anyi dama ina da niyar kaita ayi mata gwaje-gwaje sannan in taimaka mata yadda zata ji saukin bakincikin da yake ranta ne"
Baffa ya mike kamar ya rufe shi da duka "dan zaman naka a Kano ne yasa kake tunanin ka fimu wayo da sanin ya kamata? Idan baka yi hankali ba na fada maka karatun ma sai a hakura ka dawo gabanmu ka zauna...shashashan yaro ana ga yaki kana ga kura"
Inna tabe baki tayi "duk abin nan kila ma shiryowa tayi tazo ta fada kai kuma ka hau ka zauna. Idan karya take yi fa bariki ce ta kare mata shine ta dawo ayi auren ka rufa mata asiri fa"
Hawayensa ne ya sakko ya kalleta a sanyaye yace "Innaaaa!"
Jikinta ne yayi sanyi yayin da Baffa ya dauki bota ya shige bayan gida.
Abinci tayi masa tayi yace ya koshi kawai ya mike
"zan koma a satin nan zamu fara shiga aji"
"Allah Ya bada sa'a Ya shi albarka. Ungo maza ka tashi ka tafi zan taushi mahaifinka kafin ka sake dawowa"
Zaninta ta dan kwance daga gefe ta hado masa dubu biyu da dari bakwai ta bashi. Karba yayi yasa a aljihu tare da godiya duk da fuskarsa babu annuri ko kadan.
Haka ya juya ko ruwa bai sha ba Inna tana ta masa addua har kofar gida. Yana jin ta koma ya dawo soronsu ya tsaya yaci kukansa sannan ya share ido. Yana son iyayensa amma baiji dadin matakin nan da suka dauka ba sai dai zaiyi hakuri ya barwa Allah ikonSa.
*****
Haj Mara yau tayi bacci harda minshari tamkar an gama shari'ar an basu gaskiya. Juyi tayi akan makeken gadonta don jiya daga kotu gida suka wuto abinsu.
Wayarta ta janyo ta kira Alh Sule cikin isa da kasaita tace "da baka sa hannu ka nuna damuwarka akan danka ba me ya ci mu Alhaji? Na kira ne kawai nayi maka albishir da cewa kiris ya rage mu sami nasara mu baiwa marada kunya"
"Ni kike fadawa haka Marakisiyya?"
"Da 'yan hamayya nake wadanda basu damu da halin da 'ya'yansu suke ciki ba. Ko kana cikinsu ne?" Tayi masa tambayar rainin hankali tana 'yar dariya.
Murmushin takaici yayi "bana cikinsu gaskiya domin ni ina nan ina addu'a akan Allah Ya fitar min da dana idan yana da gaskiya idan kuma shi mai laifi ne Ya fitarwa wadanda aka zalunta hakkinsu"
Kafin ta ankare ta bashi amsa ya kashe wayar. Kallonta ta rinka yi rai na kuna tana ayyana yadda zata rama idan ya dawo.
Shima a nasa bangaren yana bakincikin yadda neman kudi yasa shi sakar mata ragamar gidan. Yayi babbar sa'a sauran yaransu mata babu wata mai mugun hali ko ace miji ya kawo kararta. Ita Haj Mara din ma arzikinsa da ta ga yana ta habbaka ne yasa ta kara kwallafa rai akan tilon namijin nasu ta sangarta shi har ya kai matakin da tankwara shi zaiyi matukar wahala.
Mikewa tayi zata shiga wanka BB ya shigo dakin nata ba ko sallama yana muzurai.
"Babawo lafiyarka kuwa?"
"Ras nake Hajjaju mutan Makka da Madina. Wai yane....?"
Kasa cewa komai ma tayi jin yadda yake mata magana. Gashi kamar yasha wani abu. Da kyar ta iya cewa
"Me kake nema ne?"
"Ke muka yi magana kika ce min idan na fadi abinda kika sani yarinyar nan Mawadda kamar kin aura min ita kin gama ne kuma gashi har mun taho ko iyayenta baki nema ba"
"Bansan rashin hankalin naka ya kai nan ba. Ta yaya za'ayi nayi musu magana ba'a gama shari'a ba? Ka bari a kare komai mana ka ga iya gudun ruwana"
Hade rai yayi yana kunkuni "to ni dai kada ayi min solo don ba yarda zanyi ba na fada miki tun wuri."
Daga haka ya fita tayi saurin sakawa kofarta mukulli don tsoro ma ya bata.
*****
Dr Tani ta wuni a asibiti tana gyara duk wani report na Mawadda. Wadancan na gaskiyar ta sa wani masinja ya dauko mata ainihin file din ta bashi kudi sannan ta tura a jakarta. Nan ta zauna ta sake komai da taimakon masinjan ta buga sababbin takardu da suka dace da kwanan watan wadancan. Tana aikin tana tausayawa BB domin ba karamin abu bane ace anyiwa mutum sharrin fyade.
Wayarsu ta dazu da Haj Mara ta dada tayar mata da hankali inda tace mata ko ruwa baya iya sha zabgegen namiji kamarsa wai jiya har kuka yayi mata da suka dawo yana cewa rayuwarsa tazo karshe wace mace ce zata taba aurensa. Cikin lallashi Dr Tani tace ta bashi hakuri ta san duk wannan tashin hankalin nasa akan Qareeba ne kuma alkawari ne tayi masa kamar anyi aure an gama tsakaninsu.
Kwafa tayi a hankali tana jin tsanar su Mawadda. Tunda take ita dai tasan 'yarta ba mummuna bace gata fara amma samari basa wuce zuwa uku idan sun kai zuciya nesa suke zukewa a nemesu a rasa. 'Ya'yan nata duka sunki aurowa saboda yanayinsu. Ita kuma hakan bai taba damunta ba balle ta gane sokoncinsu yake hanasu aure. Murnar samun BB a matsayin suruki yasa komai aka fada mata take hawa ta zauna daram.
Sai da ta gama gyara komai ta tafi gida gabanin magariba.
Dahiru yana zaune a kan benci a kofar gidan ya nisa cikin tunani wani yaro da baifi shekara hudu ba ya taho kan titin gidajen wurin yana buga ball. Dr Tani ta taho ga duhu ya kawo kai saura kadan ta buge shi Dahiru ya tashi a guje ya dauke yaron har yana faduwa.
Kanta ta zuro ta taga tace masa "don tsabar wulakanci me ya hanaka dauke yaron tun da na karyo kwana?"
Batare da ya saki yaron ba yace "Hajiya kiyi hakuri"
Tsaki ta doka ta shige bayan maigadi ya bude mata gate.
Shi kuma Dahiru ya fuskanci yaron.
"Assha ba dai kaji ciwo ba ko, daga ina kake?"
"Nan gidan" ya nuna wani gida da tun zuwansa ya kula aikin gininsa ake yi.
"Shine zaka fito kai kadai kana buga kwallo akan titi. To wuce muje ka shiga ciki kuma idan na sake ganin kafarka a wajen nan sai na yanketa."
Yaro yayi kwalkwal da idanu "da wuka ko reza?"
Dahiru ya dan murmusa. Shi tsorata yaron yayi niyar yi saboda ba karamin ganganci bane fitowar tasa "da almakashi zan yanke nasan yafi zafi. Idan zaka yi wasanka kayi a cikin gida banda titi kaji ko"
"Naji sakeni na tafi to.." yaro ya fada duk ya tsure.
"A'a sai na kaika har ciki nace a zaneka kana fita titi"
Wani mutum da yake jinsu daga gefen gate din gidan da ake aikin sanye da 'yar shara ne ya fito yadda zasu ganshi sosai. Yaron ya ruga wurinsa shi kuma Dahiru yana ganin haka yayi zaton ko maigadin gidan ne.
"Baba don Allah a rinka kulawa da amana. Kaga da bana kusa yau da karshen aikinka yazo idan da tsautsayi"
Mutumin ya gimtse dariyarsa yace "Allah dannan me ya faru?"
Dahiru ya sanar dashi duk da cewa akan idonsa akayi komai. Shima da sauri ya biyo bayan jikan nasa sai dai kafin ya iso ya tsallaka titin.
"Zan kiyaye in sha Allahu. A nan kake ne?"
"Eh ina aiki a gidan can ne."