← Book details Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 68

Sashe 48

Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Su BB kuwa bukata na biya dama yawancin motocin duk an gama shiga kawai suka tada motoci suka shiga cin taya suna tada kura. Kan kace kwabo sun fice daga layin a guje.

Kowa yayi zaton sun fara gaba ne nan fa akayi ta shiga mota ana tafiya. Attahir yana tsayawa ya tura a yi masa magana da daya daga cikin iyayen Dahiru. Anyi sa'a ta dazu ce kanwar Mal Isiyaku.

"Kaine Attahirun?"

"Eh Gwaggo, Dahiru ya fada miki a motata zamu tafi da amaryar ko?"

Tayi shiru sai kuma tace "ya fada amma yanzu wani abokinku yace wata lalura ta hanaka zuwa kace yazo ya dauketa. Ko minti biyar basuyi da tafiya ba"

Me kenan yace a ransa yana tunanin waye wannan. Bai bata lokaci ba ya kira Dahiru ya dauka yana dariya "sarkin zumudi gata nan sun fito da ita yanzu zamu taho. Ka dauko min tawa?"

Gaban Attahir ya fadi ya tabbata Dahiru bai turo kowa ba kenan ya daure yace "yanzu na iso"

Cike da murna Dahiru yace "nagode Dan uwanmu Attahiru angon Nawal"

Kashe wayar yayi jikinsa gabadaya yaji yayi matukar sanyi. Mota ya koma yace bari ya dan kara lokaci ya tabbatar kada ya tayar musu hankali a banza.
******

Sunyi tafiya mai dan nisa dreban da yake jan su Mawadda ya kira daya daga cikin na bayansu wanda suke tare yace sunyi faci ya kira sauran su jira su.

Su Yaya a tunaninsu duk 'yan daukar amaryar tare suke. Nan kuwa plan ne. Motoci hudun nasu duk suka tsaya. Sauran idan sun tsaya sai suce suyi gaba. Sai da ya rage su kadai kowane dreba banda nasu Mawadda suka fadawa matan da suka debo wai kwatancen kuskure akayi musu ba amaryarsu suka dauko ba. Su unguwar Diga zasu ce jen gaban zawaciki sai suka zaci tunga aka ce. Mata rai a bace balle da suka nuna bazasu mayar dasu ba. Haka suka sassauka suna ta mita su kuwa suka yi gaba. Yaya ce ta kula babu motocin suna ta tafiya an bar mata. Saboda su biyun sun fito don a cire taya dreban yace amarya tayi zamanta a ciki.

"Ya haka abokanku suke bar mana 'ya'ya a titi?" Tace tana lekawa gaban motar inda ta kula mutumin ciki ko kala bai ce ba.

Dago kai yayi ya kalleta yayi wani murmushin mugunta "ku ma sai ku nemi mota ku kara gaba. Kai Bobo zo mu ware"

Cikin Mawadda ne yayi wani mahaukacin kara saboda komai dadewar lokaci tasan bazata taba manta muryar BB ba. Ta mika hannu ta bude kofa Bobo dreba ya danna lock yayin da su Yaya suka soma ihu suna kallo ya figi mota suka yi gaba.

Innalillahi Yaya take ta maimaitawa jikinta tamkar mazari ta shiga firgicin sake ganin wannan yaro da ya tarwatsa musu rayuwa. Sauran matan suka nufosu jin tana kuka tace an sace amarya.

******

Attahir kasa zama yayi ganin motocin sun gama tafiya. Wata yarinya ya tura ciki yace yana son magana da Ade don ya tabbatar tana gida.

Jin ance Attahir ta taso da sauri ta same shi a bakin kofa rike da hula. Baya son firgitasu da abinda babu tabbas sai dai hankalinsa yaki kwanciya. Duk abokansu da zai tambaya game da daukar Mawadda kowa yace ba motarsa ta shiga ba.

"Attahir yaya akayi, naji ance kaine mai daukar amarya.

Kai ya dukar yace "Ade wallahi bani bane na dauketa. Nazo ance sun tafi "

Maganarsa bata gama shigarta ba suka ji kukan Bilki tana kiran Ade. Ita dama babu ita a 'yan kai amarya saboda faduwar da tayi ga jikin kiba tana ta dingisa kafa.

Ade ta ruga ciki a guje Attahir ma baiyi wata wata ba yabi bayanta.

Kuka take sosai tana fadawa Ade dasu Iya wayar da ta gama da Yaya.

"INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN"

Suka ce a tare sai ga Ade ta fasa ihu tana kuka iya karfinta. Ba karamin so take yiwa Mawadda ba sai dai kara da kunyar 'yar fari yasa take boyewa. Amma tun da akayi mata fyade ta ajiye abubuwa da dama ta jawo 'yarta jikinta.

Innar Fatihu tace ba kuka zata yi ba a kirawo Baba. Cikin dan lokaci ya shigo dama yana masallaci suna hira da abokan arziki.

Gida fa ya rude gabadaya sai koke-koke. Attahir ya rasa inda zai sa kansa. Baba ne yayi ta maza yace su wuce ya kaishi can gidan nasu inda za'a kai Mawadda. Gara su tabbatar basu je ba kafin a tayar da hankalin kowa.

Ade najin haka ta tashi "wallahi nima sai naje"

Inna da Iya ma suka ce zasu. Attahir yace duk su fito. Bilki aka bari da kalilan cikin 'yan biki sai yaransu.

******

An shige da amarya Nawal ciki Dahiru ya janye motarsa gefe yana duban hanya. Ya sani nan da 'yan mintuna Attahir zai shigo masa da Mawadda. Murmushi ne ya kufce masa shi kadai yana hango anjima shi da Mawaddatan wa Rahma.

Zance har ya fara isowa nan yana mota yana tsarawa Mawadda text bai sani ba. Gilmawar motar Attahir ya gani ta shigo fargajiyar gidan a guje. Fitowa yayi a ransa yana cewa sai yaja masa kunne tunda yayi gudu da ita.

Tsayawa yayi gabansa yana wani irin matsanancin bugu saboda ganin Baba, Ade, Iya da Inna sun fito daga motar Attahir din.

Ya soma takowa zuwa garesu ya ga Yaya da wasu mata biyu sun shigo a adaidaita sahun da Attahir ya yiwa kwatancen gidan ta wayarta.

Haj Mama ya gani ta fito da dankwali a hannu bai san me suke cewa ba ya ga ta riko Ade wadda ta sake zube musu a kasa tana kuka Yaya tana rungume da ita suna yi tare.

"Babu lafiya" ya furta cikin wata irin murya mai ban tausayi da taba zuciya a lokaci guda yana runtse idanuwansa.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰20

*Batul Mamman*💖

Dahiru ya fara tafiya zuwa garesu kawai yaji zuciyarsa bata da karfin daukar ko ma menene ya faru. Juyawa yayi abinsa ya shige mota ya tayar zai fita daga gidan.

Attahir ne ya fara hango shi ya shiga kiran wayarsa yaki dauka. Hannunsa har rawa yake ya kira maigadinsu yace yayi maza ya rufe gate da sauri. Maigadi ya cika umarni daidai isowar Dahiru bakin gate din yana ce masa ya bude masa. Sai dai yana magana zaka gane muryarsa bata tsayawa ma rawa take yi ya karaya sosai.

A guje Attahir ya iso gareshi "fito mu koma ciki Dahiru"

"Ku kyaleni don Allah, ku barni na tafi Attahir bani da lafiya" ya dago kai suka hada ido kawai sai ga hawaye yana zirarowa daga idanunsa.

Ba karamin tausayi ya bashi bawa Attahir ba yasa hannu ya bude motar ya janyo shi yana nuna masa su Ade "ka duba halin da mahaifiyarta take ciki Dahiru they need you now more than ever."

Daurewa yayi kafin zuciyarsa ta buga yace "me ya sameta?"

"Mu shiga ciki zaka ji komai" ya fada yana jan hannunsa.

Wani katon falo suka shige dukkaninsu. Dahiru iyakarsa kofa yana jin kamar ya fita kada yaji.

Baba Prof da Baba sune manya a maza sai su Iya da kuma iyaye mata.

Yaya ce ta fada musu yadda abin ya kasance daga fitowarsu kawo amarya.

Naushi Dahiru ya kaiwa bango da hannunsa mai targaden da bai gama warkewa ba jikinsa yana tsuma kamar wadda zashi filin daga. Zuciyarsa ce take zafi kamar zata tarwatsa kirjinsa ta fito. A karo na biyu wannan matsiyacin ya sake shiga tsakaninsa da Mawadda. Fita daga gidan zaiyi ya nemo ta duk inda take. Idonsa idon mutumin nan baya jin zai iya barin shi da rai.

Baba yaji yace "Dahiru ina zaka je?"

Murya a dake yace "neman Mawadda"

Baba Prof da kansa yaje ya dawo dashi ciki ya zaunar dashi a gabansa.

"Wannan al'amari ba karami bane amma duk da haka kada muyi garaje. Idan ka fita kasan ta ina zaka fara nemanta? Hukuma zamu sanar sannan mu dage da addu'a Allah Ya tsare mana ita"

Zaman me zaiyi har sai 'yan sanda sun iso. Sake tashi yayi kawai cikin zafin nama "Baba banki taku ba amma suyi nasu nima nayi nawa. Wallahi bazan iya zama ina jiran sai ranar da 'yan sanda su ka ganta ba. Idan yana tunanin yaci galaba akaina ya dauketa ni rayuwarsa zan karar sai dai nima a kasheni"

"Ka dawo ka zauna Dahiru mu bi komai a sannu" Innar Fatihu tace tana hawaye.

Ade da Yaya ya sake kallo yadda suka fita hayyacinsu kawai ya fita daga falon ransa yana kuna. Yana ji ana kiransa ko waige baiyi ba. Ya kusa mota Attahir ya cimmasa a guje.

"Bude mota Dahiru Ade is unconcious" yace yana juyawa da gudu.

"La haula wala quwwata ila billah" ya rike kansa da yake zugi ya bude motar da sauri.

Saifullahi da Marwanu ne suka riko Ade bata san inda kanta yake ba. Gidan ya kaure da koke-koken mata. Danlami da yake gidan ake wannan hatsaniya tuni ya kira iyayensu sun kamo hanya a daren.

A bayan motarsa aka sakata. Baba Prof yace Attahir ya tuka kada a kuskura abar Dahiru yaja mota.

Dahiru yana gaba Ade, Yaya da Marwanu a baya. Sai motoci biyu na bayansu wadanda su Baba suke binsu a baya. Asibitin Dr Tani yace su je banda rashin nisa sosai yana ganin ita zata fi fahimtar halin da Ade take ciki tunda har yanzu a cikinsa take ita ma.

******

Dr Tani tana tsaye a reception din asibitin tare da kusan duka ma'aikatanta harda masu shara da goge-goge. Ranta a bace yake ta dora hannunta akan kafadar Qareeba da take zaune akan wheelchair tana ta sharbar kuka.

"Kiyi shiru haka nan Qareeba ki nuna min waye a cikinsu yayi maganar?"

Qareeba kuka ya ci karfinta ta kasa kallon mutanen gabadaya. Dr Tani ta daga yatsa tana nuna su daya bayan daya daga likitoci zuwa kananan ma'aikata.
Chapter 48 · 0% Book details