Sashe 18
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su Yaya kuwa rokon Dr. Tani sukayi da ta taimaka ta amince sun bada sunanta a matsayin shaida a kotu.
Dan nazari tayi ita bata son shiga sabgar mutanen to amma tana tausayin rayuwar yarinyar nan.
"Ba komai ai aikinmu ne. Duk lokacin da shari'a ta hado da aikinmu dole mu tsaya mu fadi abinda bincike ya nuna"
Su Ade sai godiya suke mata. Ciki ta shiga ta duba Mawadda tare da hadata da wasu magungunan.
Bayan fitarsu wayar Haj Mara ta shigo mata.
Cikin nishadi da shewa yadda ta saba tace "Bokan turai gani a Kano anjima zanzo gidanki yau nayi zuwan bazata"
Dr. Tani sai murna ko akan maganar auren ne. Qareeba ta kira tace idan batayi wanka ba maza ta shiga tayi amma kafin nan a hadata da Kuku. Umarnin gyaran gida da girki ta basu sannan ta tattara kayanta ta fito.
A gidan Haj Mara tayi la'asar suka zauna hira.
"Hmmm kinga yadda Babawo ya sakani a gaba kan kanwarsa kuwa? Baban ma duk ya damu so yake yayi ya kammala abinda ya kaishi China azo asa rana"
Wani mugun dadi Dr Tani taji ta kara fadada murmushinta "nima haka Qareeba take min, motsi kadan tace BB. Gara asa ranar kurkusa don naga sun fimu doki"
Dariyar shakiyanci suka yi suka tafa. Haj Mara ta lura ba karamin matsuwa aminiyar ta tayi da ayi bikin ba. A ranta tace ta sami makamin dafawa.
"Ya kamata muyi zama na musamman akan shirye-shiryen bikin. Yanzu ma fa in fada miki wai sammaci aka kawo mana har gida gobe zamu kotu"
"Ko... me?"
Haj Mara ta tabe baki "kar fa ki damu ba wani abin arziki bane da ya wuce sharrin 'yan aiki"
Ina zata ki damuwa ana batun kotu.
"Me ya faru?" Wannan karon muryarta ta soma sanyi
"Yarinya ce take min aiki kinsan halinsu da sun sami dama su fara bibiyar maza. Shine fa tayi wani saurayi mai shago ashe irin 'yan duniyan nan ne ina gida aka zo aka ce min anga mai aikina a dakinsa can bayanmu"
Kirji Dr Tani ta dafe "kinji halin yaran nan ko, kana zaman zamanka su janyo maka masifa"
Rangwadar da kai Haj Mara tayi "nima ai ta jaza min. Tana dawowa nayi mata duka kin sanni da zuciya ga raina ya baci. Kuma nace gida zan mayar da ita. Duk yadda ta bani haushi haka naje gidan yaranki da kaina nasa suka hado min kayayyakinsu na sawa da na yara na bata da dubu ashirin nace ta shirya washegari zan mayar da ita."
"Dama zaman me zata yi miki sai taje tayi ciki ta dorawa maigida ko dansa"
"Kamar ko kin sani"
Jikin Dr Tani ya hau rawa danginta da na Daddy kusan babu wanda bata sanarwa Qareeba tayi miji ba don su huta da gori. Mijin ma dan gidan Alh Sule Chanji.
Ganin ta tsorata Haj Mara tayi murmushi "ita ba ciki tayi ba fitar da nayi ne ta lallaba ta shiga dakina zata yi min sata Babawo ya ganta. Cikin fushi ya mammareta da safe muka kaita gida. Wai kawai bayan sallah sai ga sammaci ana zarginsa da yi mata fyade"
"Me???" Kanta taji yana sarawa. Idan makiyanta suka ji zancen nan ai ta banu.
"Ban fada miki don ki tada hankali ba domin ina da shaidu da zasu kareni. Babawo ban taba jin ya yabi wata mace ba balle ince fuska ta gani sai Qareeba. Alfarma daya nake nema kada babansu yaji zancen nan ku hanamu 'ya a gaba"
"Wa? Ni? yaya ma za'ayi na fadawa kowa. Ko shi bazaiji ba" ji tayi kamar ta saki ihu. Damarsu daya ta aurar da Qareeba tana neman subuce musu.
Haj Mara ta sami yadda take so ta cigaba "ai Mawadda da iyayenta sun dauko ruwan dafa kansu. Mistake dina bai wuce na rashin kula ba tun farko kila da na gano suna wani abu da saurayin nata da wuri"
Idanu a waje Dr. Tani tace "Mawadda kika ce?"
"Eh, kinji sunan wani iri ko" ta fada tana satar kallonta
"Patient dina ce indai wadda za'a shiga kotu gobe ne Mawadda Fatihu"
"Laaahhhhhh" Haj Mara ta saki baki ita a dole mamaki take "kinji wani abu kamar a fim"
Ran Dr. Tani ya baci matuka. Tasan kawarta bazata yi mata karya ba musamman ma da bata san ta sansu ba. Yadda ta matsu Qareeba tayi aure shine tana tausayinsu zasu kullawa yaron da yake son 'yarta sharri. Lallai zata shayar dasu mamaki. Kwafa tayi ta riko hannun Haj Mara wadda ta dukar da kai harda hawaye
"Tunda suka zo asibiti da gaske an mata fyade kenan zata dorawa Babawo"
"Babawo ba naki bane ke kadai Marakisiyya. Barni dasu kawai".
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰8
*Batul Mamman*💖
Fuska na nuni da alhini Dr Tani tace "ina Babawon yake yanzu?"
"Yana tare da wani abokinsa yace zai kwana a wurinsa. Nima akwai 'yar kanwar babana gidanta zan wuce yanzu" Haj Mara ta bata amsa muryarta har tana dan rawa kamar zatayi kuka.
"Haba ke kuwa Marakisiyya maimakon kuyi zamanku a nan, kada ki manta fa alaka mai karfi ke shirin shiga tsakaninmu banda ta kawance. Kiyi zamanki a nan. Shima ki kira shi ya taho ya kwana dakin 'yan uwansa. Ai mun zama daya"
Dadi ya baibaye Haj Mara. Batayi zaton abin zai zo da sauki kamar haka ba. Cigaba suka yi da tattauna yadda zasu bullowa su Mawadda a kotu washegari.
*****
Saukarsu kenan daga tasi suka ga gaban kotun cike da jama'a. Wasu 'yan kallo ne kawai wasu kuma 'yan jarida.
Cincirindonsu kadai ya sanyayarwa da Mawadda gwiwa ta daga hannu ta kamo Ade.
"Mu koma gida" tace a hankali wani siririn hawaye yana fita daga idanunta.
"Ki karfafi zuciyarki Mawadda. Idan kika sare tun yanzu to shari'ar nan bata da wani amfani. Ni dama nasan za'a rina tun jiya a rediyo da naji ana zancen fyade da ake yiwa 'yan aiki har aka bada misali da zaman kotun da za'ayi yau akan irin case din" Inji Basira kanwar Yaya.
Suna tsaye daga gefe wasu 'yan sanda biyu suka zo za'ayi musu jagora zuwa cikin kotun. Nan da nan 'yan jarida suka rufar musu domin sai sannan suka gane su waye. Tambayoyi ne ake ta jefa musu su dai suka samu suka shige da kyar fuskar Mawadda lullube da mayafi.
Kotu tayi shiru an gama sauraren shari'ar wasu kamar daga sama suka ji ance.
"Shari'a ta gaba da za'a saurara ita ce tsakanin Mawadda Fatihu da Babawo Sule Chanji inda ake tuhumar Malam Babawo dake zaune a gida mai lamba 190 Gambara cresent Kaduna da laifin yiwa Mawadda duka tare da fyade a ranar 14 ga watan Yuni 2010."
Hantar cikinta ce ta kada sosai da taji ance idan tana kusa ta taso. Mikewa tayi tana ji a jikinta duk wani mai ido a wurin ita yake kallo. Tamkar ta shige cikin kasa ta rufe kanta haka taji a lokacin. Wurin da aka kebe domin tsayuwar wadanda shari'a ta shafa taje ta tsaya kanta a kasa. Alkali ya bukaci Babawo ya fito shima. A razane ta daga kai su ka hada ido. Zuciyarta ce ta dauki zafi saboda radadin da take ji da ta sake ganinsa ga Haj Mara itama a zaune hankalinsu duk su biyun a kwance.
Bayan shima ya tsaya lauyoyi suka gabatar da kawunansu gaban kotu.
"Sunana Barista Shafa'atu Aminu. Lauyan gwamnati mai kare mai korafi wato Mawadda Fatihu"
Cewar wata mace mai cike da nutsuwa da kamala.
Kujera ce ta danyi kara yayin da Barista Dalhatu Talba ya tashi ya gabatar da kansa a matsayin lauyan wanda ake tuhuma.
Alkali Dawud ya gyada kai sannan yace su fara tambayoyi da kawo shaidunsu.
Barista Shafa'atu ta taso ta matsu gaban zagayen inda Mawadda take tsaye
"Malama Mawadda ko zaki iya sanar da kotu abinda ya faru a ranar shahudu ga watan Yuni tsakaninki da Babawo?"
Shiru tayi gabanta na lugude, wuri yayi tsit ita kadai ake kallo da sauraro. Tunawa tayi da yadda Baba da Iya suka sakata a gaba da magiyar kada ta cuci kanta tayi shiru. Idan taji tsoro taki fadar gaskiya tamkar ta amince gobe Babawo ya sake yiwa wata yarinyar kwatankwacin abinda yayi mata ne.
Wani mugun yawu ta hadiya sannan ta soma bada labari harda yadda ya rinka bibiyarta kafin wannan rana. Da kyar ta iya kai karshen labarin saboda kukan da take yi mai taba zuciya. Mutane da dama a wurin wannan abu ya tabasu sosai. Sai da Alkali ya buga gudumarsa ya samu aka tsagaita da kananun surutan da suka soma tashi.
Barista Shafa'atu ta dan ja hanci alamun itama labari ya tabata sannan ta sake tambayarta game da Haj Mara. Shima duk yadda suka yi haka ta bada labari.
"My lord ina rokon wannan kotu mai adalci kamar yadda muka saurari bayani daga bakin Mawadda ta taimaka tayi mata adalci wurin hukunta Babawo da mahaifiyarsa daidai da laifinsu domin sunyi tarayya wurin cutar da ita" cewar Barista Shafa'atu.
Sai da yayi 'yan rubuce-rubuce sannan ya dubi Barista Dalhatu yace ko yana da tambaya da zai yiwa Mawadda ya amsa da eh.
Tun daga kallon da yake jifanta dashi tasan ba mutumin kirki bane. Wani kallo yake mata kasa-kasa irin na sai na gama dake.
"Kince Babawo ya dauki wani lokaci yana bibiyarki da son ki bashi hadin kai haka ne?"
"Eh"
"To amma me ya hana tun tsahon wannan lokacin ki sanar da mahaifiyarsa domin a yiwa tufkar hanci?"
Da sauri ta dago kai ta kalli Alkalin shi kuma yace ta amsa tambayar.
"Saboda....uhmmm dama saboda ina tsoron kada Hajiya ta dakeni ne"
"Uhmm Mawadda kenan, kina jin akwai uwar da zata daki wadda ta kawo karar danta yana neman keta mata haddi. A tunanina zata yi saurin kawo karshen matsalar ne ko don kada a wayi gari a rana irin ta yau"
Haj Mara daga inda take zaune tayi wani murmushin jindadi gamin Mawadda ta kasa bada amsa.
"Don baka santa bane na rantse duka na take yi ko yaya nayi laifi. Kuma tana sonsa shiyasa naji tsoron kada na fada tace karya nake"
"Ke kuma gaki jaruma zaki iya kwatar kanki ko ki jure duk wani hari da zai kawo miki"
Dan nazari tayi ita bata son shiga sabgar mutanen to amma tana tausayin rayuwar yarinyar nan.
"Ba komai ai aikinmu ne. Duk lokacin da shari'a ta hado da aikinmu dole mu tsaya mu fadi abinda bincike ya nuna"
Su Ade sai godiya suke mata. Ciki ta shiga ta duba Mawadda tare da hadata da wasu magungunan.
Bayan fitarsu wayar Haj Mara ta shigo mata.
Cikin nishadi da shewa yadda ta saba tace "Bokan turai gani a Kano anjima zanzo gidanki yau nayi zuwan bazata"
Dr. Tani sai murna ko akan maganar auren ne. Qareeba ta kira tace idan batayi wanka ba maza ta shiga tayi amma kafin nan a hadata da Kuku. Umarnin gyaran gida da girki ta basu sannan ta tattara kayanta ta fito.
A gidan Haj Mara tayi la'asar suka zauna hira.
"Hmmm kinga yadda Babawo ya sakani a gaba kan kanwarsa kuwa? Baban ma duk ya damu so yake yayi ya kammala abinda ya kaishi China azo asa rana"
Wani mugun dadi Dr Tani taji ta kara fadada murmushinta "nima haka Qareeba take min, motsi kadan tace BB. Gara asa ranar kurkusa don naga sun fimu doki"
Dariyar shakiyanci suka yi suka tafa. Haj Mara ta lura ba karamin matsuwa aminiyar ta tayi da ayi bikin ba. A ranta tace ta sami makamin dafawa.
"Ya kamata muyi zama na musamman akan shirye-shiryen bikin. Yanzu ma fa in fada miki wai sammaci aka kawo mana har gida gobe zamu kotu"
"Ko... me?"
Haj Mara ta tabe baki "kar fa ki damu ba wani abin arziki bane da ya wuce sharrin 'yan aiki"
Ina zata ki damuwa ana batun kotu.
"Me ya faru?" Wannan karon muryarta ta soma sanyi
"Yarinya ce take min aiki kinsan halinsu da sun sami dama su fara bibiyar maza. Shine fa tayi wani saurayi mai shago ashe irin 'yan duniyan nan ne ina gida aka zo aka ce min anga mai aikina a dakinsa can bayanmu"
Kirji Dr Tani ta dafe "kinji halin yaran nan ko, kana zaman zamanka su janyo maka masifa"
Rangwadar da kai Haj Mara tayi "nima ai ta jaza min. Tana dawowa nayi mata duka kin sanni da zuciya ga raina ya baci. Kuma nace gida zan mayar da ita. Duk yadda ta bani haushi haka naje gidan yaranki da kaina nasa suka hado min kayayyakinsu na sawa da na yara na bata da dubu ashirin nace ta shirya washegari zan mayar da ita."
"Dama zaman me zata yi miki sai taje tayi ciki ta dorawa maigida ko dansa"
"Kamar ko kin sani"
Jikin Dr Tani ya hau rawa danginta da na Daddy kusan babu wanda bata sanarwa Qareeba tayi miji ba don su huta da gori. Mijin ma dan gidan Alh Sule Chanji.
Ganin ta tsorata Haj Mara tayi murmushi "ita ba ciki tayi ba fitar da nayi ne ta lallaba ta shiga dakina zata yi min sata Babawo ya ganta. Cikin fushi ya mammareta da safe muka kaita gida. Wai kawai bayan sallah sai ga sammaci ana zarginsa da yi mata fyade"
"Me???" Kanta taji yana sarawa. Idan makiyanta suka ji zancen nan ai ta banu.
"Ban fada miki don ki tada hankali ba domin ina da shaidu da zasu kareni. Babawo ban taba jin ya yabi wata mace ba balle ince fuska ta gani sai Qareeba. Alfarma daya nake nema kada babansu yaji zancen nan ku hanamu 'ya a gaba"
"Wa? Ni? yaya ma za'ayi na fadawa kowa. Ko shi bazaiji ba" ji tayi kamar ta saki ihu. Damarsu daya ta aurar da Qareeba tana neman subuce musu.
Haj Mara ta sami yadda take so ta cigaba "ai Mawadda da iyayenta sun dauko ruwan dafa kansu. Mistake dina bai wuce na rashin kula ba tun farko kila da na gano suna wani abu da saurayin nata da wuri"
Idanu a waje Dr. Tani tace "Mawadda kika ce?"
"Eh, kinji sunan wani iri ko" ta fada tana satar kallonta
"Patient dina ce indai wadda za'a shiga kotu gobe ne Mawadda Fatihu"
"Laaahhhhhh" Haj Mara ta saki baki ita a dole mamaki take "kinji wani abu kamar a fim"
Ran Dr. Tani ya baci matuka. Tasan kawarta bazata yi mata karya ba musamman ma da bata san ta sansu ba. Yadda ta matsu Qareeba tayi aure shine tana tausayinsu zasu kullawa yaron da yake son 'yarta sharri. Lallai zata shayar dasu mamaki. Kwafa tayi ta riko hannun Haj Mara wadda ta dukar da kai harda hawaye
"Tunda suka zo asibiti da gaske an mata fyade kenan zata dorawa Babawo"
"Babawo ba naki bane ke kadai Marakisiyya. Barni dasu kawai".
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰8
*Batul Mamman*💖
Fuska na nuni da alhini Dr Tani tace "ina Babawon yake yanzu?"
"Yana tare da wani abokinsa yace zai kwana a wurinsa. Nima akwai 'yar kanwar babana gidanta zan wuce yanzu" Haj Mara ta bata amsa muryarta har tana dan rawa kamar zatayi kuka.
"Haba ke kuwa Marakisiyya maimakon kuyi zamanku a nan, kada ki manta fa alaka mai karfi ke shirin shiga tsakaninmu banda ta kawance. Kiyi zamanki a nan. Shima ki kira shi ya taho ya kwana dakin 'yan uwansa. Ai mun zama daya"
Dadi ya baibaye Haj Mara. Batayi zaton abin zai zo da sauki kamar haka ba. Cigaba suka yi da tattauna yadda zasu bullowa su Mawadda a kotu washegari.
*****
Saukarsu kenan daga tasi suka ga gaban kotun cike da jama'a. Wasu 'yan kallo ne kawai wasu kuma 'yan jarida.
Cincirindonsu kadai ya sanyayarwa da Mawadda gwiwa ta daga hannu ta kamo Ade.
"Mu koma gida" tace a hankali wani siririn hawaye yana fita daga idanunta.
"Ki karfafi zuciyarki Mawadda. Idan kika sare tun yanzu to shari'ar nan bata da wani amfani. Ni dama nasan za'a rina tun jiya a rediyo da naji ana zancen fyade da ake yiwa 'yan aiki har aka bada misali da zaman kotun da za'ayi yau akan irin case din" Inji Basira kanwar Yaya.
Suna tsaye daga gefe wasu 'yan sanda biyu suka zo za'ayi musu jagora zuwa cikin kotun. Nan da nan 'yan jarida suka rufar musu domin sai sannan suka gane su waye. Tambayoyi ne ake ta jefa musu su dai suka samu suka shige da kyar fuskar Mawadda lullube da mayafi.
Kotu tayi shiru an gama sauraren shari'ar wasu kamar daga sama suka ji ance.
"Shari'a ta gaba da za'a saurara ita ce tsakanin Mawadda Fatihu da Babawo Sule Chanji inda ake tuhumar Malam Babawo dake zaune a gida mai lamba 190 Gambara cresent Kaduna da laifin yiwa Mawadda duka tare da fyade a ranar 14 ga watan Yuni 2010."
Hantar cikinta ce ta kada sosai da taji ance idan tana kusa ta taso. Mikewa tayi tana ji a jikinta duk wani mai ido a wurin ita yake kallo. Tamkar ta shige cikin kasa ta rufe kanta haka taji a lokacin. Wurin da aka kebe domin tsayuwar wadanda shari'a ta shafa taje ta tsaya kanta a kasa. Alkali ya bukaci Babawo ya fito shima. A razane ta daga kai su ka hada ido. Zuciyarta ce ta dauki zafi saboda radadin da take ji da ta sake ganinsa ga Haj Mara itama a zaune hankalinsu duk su biyun a kwance.
Bayan shima ya tsaya lauyoyi suka gabatar da kawunansu gaban kotu.
"Sunana Barista Shafa'atu Aminu. Lauyan gwamnati mai kare mai korafi wato Mawadda Fatihu"
Cewar wata mace mai cike da nutsuwa da kamala.
Kujera ce ta danyi kara yayin da Barista Dalhatu Talba ya tashi ya gabatar da kansa a matsayin lauyan wanda ake tuhuma.
Alkali Dawud ya gyada kai sannan yace su fara tambayoyi da kawo shaidunsu.
Barista Shafa'atu ta taso ta matsu gaban zagayen inda Mawadda take tsaye
"Malama Mawadda ko zaki iya sanar da kotu abinda ya faru a ranar shahudu ga watan Yuni tsakaninki da Babawo?"
Shiru tayi gabanta na lugude, wuri yayi tsit ita kadai ake kallo da sauraro. Tunawa tayi da yadda Baba da Iya suka sakata a gaba da magiyar kada ta cuci kanta tayi shiru. Idan taji tsoro taki fadar gaskiya tamkar ta amince gobe Babawo ya sake yiwa wata yarinyar kwatankwacin abinda yayi mata ne.
Wani mugun yawu ta hadiya sannan ta soma bada labari harda yadda ya rinka bibiyarta kafin wannan rana. Da kyar ta iya kai karshen labarin saboda kukan da take yi mai taba zuciya. Mutane da dama a wurin wannan abu ya tabasu sosai. Sai da Alkali ya buga gudumarsa ya samu aka tsagaita da kananun surutan da suka soma tashi.
Barista Shafa'atu ta dan ja hanci alamun itama labari ya tabata sannan ta sake tambayarta game da Haj Mara. Shima duk yadda suka yi haka ta bada labari.
"My lord ina rokon wannan kotu mai adalci kamar yadda muka saurari bayani daga bakin Mawadda ta taimaka tayi mata adalci wurin hukunta Babawo da mahaifiyarsa daidai da laifinsu domin sunyi tarayya wurin cutar da ita" cewar Barista Shafa'atu.
Sai da yayi 'yan rubuce-rubuce sannan ya dubi Barista Dalhatu yace ko yana da tambaya da zai yiwa Mawadda ya amsa da eh.
Tun daga kallon da yake jifanta dashi tasan ba mutumin kirki bane. Wani kallo yake mata kasa-kasa irin na sai na gama dake.
"Kince Babawo ya dauki wani lokaci yana bibiyarki da son ki bashi hadin kai haka ne?"
"Eh"
"To amma me ya hana tun tsahon wannan lokacin ki sanar da mahaifiyarsa domin a yiwa tufkar hanci?"
Da sauri ta dago kai ta kalli Alkalin shi kuma yace ta amsa tambayar.
"Saboda....uhmmm dama saboda ina tsoron kada Hajiya ta dakeni ne"
"Uhmm Mawadda kenan, kina jin akwai uwar da zata daki wadda ta kawo karar danta yana neman keta mata haddi. A tunanina zata yi saurin kawo karshen matsalar ne ko don kada a wayi gari a rana irin ta yau"
Haj Mara daga inda take zaune tayi wani murmushin jindadi gamin Mawadda ta kasa bada amsa.
"Don baka santa bane na rantse duka na take yi ko yaya nayi laifi. Kuma tana sonsa shiyasa naji tsoron kada na fada tace karya nake"
"Ke kuma gaki jaruma zaki iya kwatar kanki ko ki jure duk wani hari da zai kawo miki"