Sashe 12
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rai a bace Iya tace "ko da nace ki kwantar da kai ba cewa nayi ki wulakanta kanki ba kina jina. Kwantar da kai daban, shi iyaka ki sawa ranki mutum ya fiki arziki babu ke babu girman kai a neman halak. Amma ban yarda kowa cikinku ya wulakanta kansa akan kudi ba. Kada kuje ana cin zarafinku kuna hadiyewa don wani abu da za'a baku mai karewa a duniya. Duk zafin talauci wuyarta ka mutu kana mumini magana ta kare. Hakkinki kuma ki bar musu muna nan dake ko ba a gaban idonki ba sai tayi nadamar abin da tayi miki" Iyan kanta tana magana kuka na menan cin karfinta. Sai dai dattijuwa ce mai matukatar dauriya kuma a matsayinta na uwa garesu bata so ta karyar musu da zuciya.
Baba ta cewa ya koma gida akwai tumakinta uku da awaki biyar ya kama duka ya kai kasuwa.
"Ayi haka Iya gabadaya?" Yace a kunyace.
"Don kaniyarka ko ban haifi uwar Mawadda ba kai din ba dana bane? Ko matsayin nawa zaka nuna min eyee?"
Murmushi yayi yana bata hakuri. Ade ma tace kudaden da take tarawa na bikin Mawadda zata fito dasu idan yaso gobe da sassafe sai su wuce Kano.
*****
Da wuri Dahiru ya isa Kano saboda sammako da yayi. Rijiyar zaki ya nufa gidan Bilya. Da yake yasan da zuwansa dama yana gida yana jiransa. Abinci ya fara ci sannan suka zauna tattaunawa da dan uwan nasa.
Bilya ya nuna alhinin wannan al'amari bayan Dahiru ya gama bashi labari. Sannan suka koma batun gurbin karatu da ya samu.
"Kasan na fada maka yayan ubangidana na garejin mu ne ya sama maka adimishon din. To Alhamdulillahi jiya kana kira nayi maza naje na same shi. Munyi sa'a yace sai nan da sati biyar za'a fara zuwa karatu. Amma kafin nan akwai takardu da zan baka kaje ka cike su sai kasa suka hannu. Sauran bayani dai zaiyi maka tunda zamu je wurinsa"
Dadi ya kama Dahiru jin cewa bai makara ba. Bayan ya duba takardun da kudin da zai biya jikinsa yayi sanyi. Da gani wannan karatu za'aji jiki. Ga Bilya ba wani abin kirki gareshi ba shima ta kansa yake ga 'ya'ya biyu.
Ganin yayi shiru Bilya ya karbe takardun "kaga malam tunani ba naka bane. Tashi zaka yi muje wurin shi Oga Sani nayi masa maganar bamu da kudin karatunka sai ka nemi abin yi. Yace zai san yadda za'ayi idan ka zo"
A raunane Dahiru yace "Yayanmu Bilya ni kam me zan ce maka. Ka gama min komai nagode sosai"
"Me zaka ce kuwa da ya wuce idan an sami aikin ka rike amanar iyayen gidanka sannan kayi karatu sosai ka 'yan mana arzikin bokon a gaba. Kuma fa karatun injinniya yace ka samu saboda ya ga ka kware a lissafi. Baka ga dadin da naji ba" yayi maganar yana masa dariya.
Matar Bilya mai suna Furaira ta zo bayan Dahiru ya gama cin abinci tana masa tambayoyi kamar 'yar jarida game da Mawadda.
"Amma dai ka fasa aurenta ko?"
"In sha Allahu aure yana nan kamar yadda aka tsara tun farko"
"Kai kuwa me zaka yi da ita kamar dole"
"Ke!!! Ban fada miki ki rike bakinki akan maganar nan ba? Ina ruwanki idan yace zai aureta" Bilya ya daka mata tsawa.
Murguda baki tayi ta mike "gaskiya ce bakwa son fada masa. Allah na tuba wa ya sani ma ko 'yan ciwukan zamanin nan ta kwaso zai aura a hada shi da jafa'i"
Dahiru bai ce komai ba ya tashi ya saka takalmi. Yana jiyo hayaniyar Bilya da Furaira bayan ya bita dakin. Kaya ya chanja ya fito suka fita tare.
Garejin da Bilya yake aikin gyaran mota a bakin titin unguwar suka je. Sunyi rashin sa'a Oga Sani bai zo ba. Gefe Dahiru ya samu ya zauna yayin da Bilya ya sauya kaya zuwa kayan aiki ya shiga cikin abokan aikinsa kowa ya kama aikinsa.
Sai wurin karfe uku Oga Sani ya iso. Mutum ne na mutane mai faram-faram da jama'a da sanin hakkin na kasa dashi. Bisa wannan dalilin ne ma wata rana yaji Bilya yana fadawa wani abokin aikinsa burinsa Dahiru yayi karatu tunda yaci jarabawar shiga jami'a. Jin haka ya taimaka masa da kudi wanda da shi ne Bilya ya biya wa Dahiru yayi JAMB. Bai kuma tsaya haka ba ya kara da kaiwa yayansa da yake aiki a matsayin darakta a BUK din takardun gashi anyi sa'a ya sami gurbin karatu zai karanta Computer Engineering.
Yana fitowa daga motarsa gaban Dahiru yaje yana murmushi "wannan dai ko ba'a fada ba nasan kaina kanin Bilya mayen honda"
Dahiru yayi 'yar dariya yana kallon Bilya da ya taho wurin "Yayanmu sunanka kenan ashe"
Oga Sani yace "ashe bai fada muku ba. To ai idan kazo wurin nan ba ka ce Mayen Honda ba da wuya a gane shi. Kunyi kama sosai amma dai ka dan fishi kyau"
Shi dai Bilya sai murmushi. Sallah suka yi Oga Sani ya daukesu a mota yace ya yiwa yayansa bayani ga dukkan alamu Dahiru zai sami aiki a gidansa.
*****
A can asibiti kuma sun gama hada kayansu an basu takarda da zasu nuna mai dauke da duk wani bayani dangane da Mawadda.
Kafin Baba ya dawo su ma sun taho tunda zaman babu amfani. Jin tana fama da lalurar rashin rike fitsari ba karamin dagawa 'yan uwanta hankali yayi ba. Haka suka tafi dai kowa rai babu dadi.
Daga bakin titi da suka sauka daga bus har zuwa gida idanu da kananun maganganu suna biye dasu. Mawadda rufe fuskarta tayi gabadaya saboda yadda ake binta da kallo. Duk bakin Iya bata ce komai ba saboda kunya. Iyalin Baffa ne suka sha zagi tas a wurinta na Dahiru ya ma fi na kowa bayan sun isa can gidansu Malam da Innar Fatihu. Lokacin duk sauran 'yan uwan Ade da na Baba kowa yana gidan.
Sun tausayawa Mawadda sosai yawancin matan harda kuka. Shirin tafiya Kano suka hau yi 'yan uwa kowa da ya mika abinda Allah Ya hore masa a matsayin tasu gudummawa saboda basu san yaya zata kaya ba.
*****
Katon gida ne suka je a Sharada housing estate. Dahiru bakon birni sai bude baki yake bai taba ganin gida irin wannan ba.
Gida ne mai kyau ga filawoyi sun kawata shi. Can gefe kuma motoci ne wurin shida masu kyau da gani zasuyi tsada shine tunanin Dahiru.
A wajen maigadi Oga Sani ya barsu ya shiga ciki. Bai wani jima ba ya dawo ya kira su. Wata mata ce ta fito a daidai bakin kofa ta tsaya su kuma suna daga gefen matattakalar da za'a taka mai gudu shida ya isa inda take tsaye. Gaisheta suka yi a mutumce ta amsa tana faman yatsina.
"Sani wanne ne zaiyi aikin a cikinsu?"
Dahiru ya dan dago kai yayin da Oga Sani ya dafa kafadarsa "wannan ne sunansa Dahiru"
Kallonsa tayi ta dan tabe baki "Aikin share farfajiyar gidan nan da gyara flower zaka yi. Sai kuma duk asabar zaka rinka yi mana wanki nawa da na yaran gidan. Ranar lahadi ka goge ko babu wuta za'a tayar da inji. Idan aikin yayi maka albashinka dubu ashirin"
Tsabar murna Dahiru bai san lokacin da yace "ahirin???" ba.
Wata irin dariya suka ji an kwashe da ita daga bayansu. Yarinya ce budurwa ta fito daga cikin motar da take a kunne tun zuwansu taci ado sosai.
Dariya take har tana rankwafawa ta kalli Dahiru "yaya sunanka?"
"Dahiru" ya bata amsa a takaice.
Tana dariya tace "Sannu Dashiru"
"Dahiru ne sunan" ya gyara mata a zatonsa bata ji bane sosai.
"To Malam Dashiru mai ahirin" ta sake kyalkyalewa da dariya.
Ransa in yayi dubu to ya gama baci. Hatta Bilya shima fuskarsa ta sauya.
"Kawu Sani ina ka samo mana 'yan ahirin?"
Hade fuska yayi sosai "bana son wannan shirmen naki Qariba"
Mamanta ta bata rai itama jin anyi mata tsawa "kai fa Sani idan kazo gidan nan to yaran nan basu da sauran sukuni"
"Yara ko magidanta? Kin ajiye dika-dikan yara saboda boko kunyi yi musu aure. Kuma kina kallo nazo da bako tana yi masa dariya don rainin hankali"
"Bakon naka ba me aikin gidansu zai zama ba? Kai kudin yayi maka zaka iya?"
A sanyaye Dahiru yace eh. Ya ma isa yace bazai iya ba tashi daya dubu ashirin a wata me ya manta.
Sunyi sallama da matar bayan an daidaita zai fara zuwa ranar litinin nan da kwana hudu kenan. Batun karatunsa wanda Oga Sani ya fada mata tace zasu daidaita idan an fara karatun a tsara yadda zai rinka aikin.
Sun juya zasu tafi Qariba ta daga murya tace "Malam Dahiru me ahirin sai monday" dariya ta rinka yi har ta shige cikin gidan.
Oga Sani yace masa sai yayi hakuri sosai da yaran dan uwansa. Shi maigidan Dr. Auwal rikakken dan boko ne wanda yake taba kasuwancin sayar da motoci yayin da matarsa Dr. Tani likita ce tana da asibitinta mai zaman kansa. Yaransu hudu maza uku sai Qariba mace kuma ita ce ta uku. Sangarta ta wuce tunani da gata yaran sun tashi dashi shiyasa zama dasu sai an kai zuciya nesa.
[08/01 : *GUMIN HALAK...*💰6
*Batul Mamman*💖
"Baffa anya ba zanje gidansu Mawadda ba da kaina?" Cewar Inna tana kallonsa ya zurfafa a tunani.
Dan guntun tsaki yayi "kije kice kinzo bada hakuri saboda 'yarki bakinta bashi da linzami ko"
"To naga ka kasa komawa kuma ance sun dawo. Danlami yace tun daga bakin titi ake binsu da kallo nasan surutun ma sai anyi"
Takaici ne kawai yake cinsa a rai. Idan ya fita an rinka zundensa kenan ko shine Mal Fatihu sai haka. Wasu har cewa suke Dahiru ne ma yayi mata fyaden. Wasu kuma suna ganin bai kyauta ba sun tonawa surukansu asiri saboda tsautsayi ya fadawa yarinyar. Yanzu ta yaya zai dawo da mutumcinsa a gari? Tashi yayi ya zura takalmansa yayi waje Inna na kiransa bai ko saurareta ba ya fita.
Baba ta cewa ya koma gida akwai tumakinta uku da awaki biyar ya kama duka ya kai kasuwa.
"Ayi haka Iya gabadaya?" Yace a kunyace.
"Don kaniyarka ko ban haifi uwar Mawadda ba kai din ba dana bane? Ko matsayin nawa zaka nuna min eyee?"
Murmushi yayi yana bata hakuri. Ade ma tace kudaden da take tarawa na bikin Mawadda zata fito dasu idan yaso gobe da sassafe sai su wuce Kano.
*****
Da wuri Dahiru ya isa Kano saboda sammako da yayi. Rijiyar zaki ya nufa gidan Bilya. Da yake yasan da zuwansa dama yana gida yana jiransa. Abinci ya fara ci sannan suka zauna tattaunawa da dan uwan nasa.
Bilya ya nuna alhinin wannan al'amari bayan Dahiru ya gama bashi labari. Sannan suka koma batun gurbin karatu da ya samu.
"Kasan na fada maka yayan ubangidana na garejin mu ne ya sama maka adimishon din. To Alhamdulillahi jiya kana kira nayi maza naje na same shi. Munyi sa'a yace sai nan da sati biyar za'a fara zuwa karatu. Amma kafin nan akwai takardu da zan baka kaje ka cike su sai kasa suka hannu. Sauran bayani dai zaiyi maka tunda zamu je wurinsa"
Dadi ya kama Dahiru jin cewa bai makara ba. Bayan ya duba takardun da kudin da zai biya jikinsa yayi sanyi. Da gani wannan karatu za'aji jiki. Ga Bilya ba wani abin kirki gareshi ba shima ta kansa yake ga 'ya'ya biyu.
Ganin yayi shiru Bilya ya karbe takardun "kaga malam tunani ba naka bane. Tashi zaka yi muje wurin shi Oga Sani nayi masa maganar bamu da kudin karatunka sai ka nemi abin yi. Yace zai san yadda za'ayi idan ka zo"
A raunane Dahiru yace "Yayanmu Bilya ni kam me zan ce maka. Ka gama min komai nagode sosai"
"Me zaka ce kuwa da ya wuce idan an sami aikin ka rike amanar iyayen gidanka sannan kayi karatu sosai ka 'yan mana arzikin bokon a gaba. Kuma fa karatun injinniya yace ka samu saboda ya ga ka kware a lissafi. Baka ga dadin da naji ba" yayi maganar yana masa dariya.
Matar Bilya mai suna Furaira ta zo bayan Dahiru ya gama cin abinci tana masa tambayoyi kamar 'yar jarida game da Mawadda.
"Amma dai ka fasa aurenta ko?"
"In sha Allahu aure yana nan kamar yadda aka tsara tun farko"
"Kai kuwa me zaka yi da ita kamar dole"
"Ke!!! Ban fada miki ki rike bakinki akan maganar nan ba? Ina ruwanki idan yace zai aureta" Bilya ya daka mata tsawa.
Murguda baki tayi ta mike "gaskiya ce bakwa son fada masa. Allah na tuba wa ya sani ma ko 'yan ciwukan zamanin nan ta kwaso zai aura a hada shi da jafa'i"
Dahiru bai ce komai ba ya tashi ya saka takalmi. Yana jiyo hayaniyar Bilya da Furaira bayan ya bita dakin. Kaya ya chanja ya fito suka fita tare.
Garejin da Bilya yake aikin gyaran mota a bakin titin unguwar suka je. Sunyi rashin sa'a Oga Sani bai zo ba. Gefe Dahiru ya samu ya zauna yayin da Bilya ya sauya kaya zuwa kayan aiki ya shiga cikin abokan aikinsa kowa ya kama aikinsa.
Sai wurin karfe uku Oga Sani ya iso. Mutum ne na mutane mai faram-faram da jama'a da sanin hakkin na kasa dashi. Bisa wannan dalilin ne ma wata rana yaji Bilya yana fadawa wani abokin aikinsa burinsa Dahiru yayi karatu tunda yaci jarabawar shiga jami'a. Jin haka ya taimaka masa da kudi wanda da shi ne Bilya ya biya wa Dahiru yayi JAMB. Bai kuma tsaya haka ba ya kara da kaiwa yayansa da yake aiki a matsayin darakta a BUK din takardun gashi anyi sa'a ya sami gurbin karatu zai karanta Computer Engineering.
Yana fitowa daga motarsa gaban Dahiru yaje yana murmushi "wannan dai ko ba'a fada ba nasan kaina kanin Bilya mayen honda"
Dahiru yayi 'yar dariya yana kallon Bilya da ya taho wurin "Yayanmu sunanka kenan ashe"
Oga Sani yace "ashe bai fada muku ba. To ai idan kazo wurin nan ba ka ce Mayen Honda ba da wuya a gane shi. Kunyi kama sosai amma dai ka dan fishi kyau"
Shi dai Bilya sai murmushi. Sallah suka yi Oga Sani ya daukesu a mota yace ya yiwa yayansa bayani ga dukkan alamu Dahiru zai sami aiki a gidansa.
*****
A can asibiti kuma sun gama hada kayansu an basu takarda da zasu nuna mai dauke da duk wani bayani dangane da Mawadda.
Kafin Baba ya dawo su ma sun taho tunda zaman babu amfani. Jin tana fama da lalurar rashin rike fitsari ba karamin dagawa 'yan uwanta hankali yayi ba. Haka suka tafi dai kowa rai babu dadi.
Daga bakin titi da suka sauka daga bus har zuwa gida idanu da kananun maganganu suna biye dasu. Mawadda rufe fuskarta tayi gabadaya saboda yadda ake binta da kallo. Duk bakin Iya bata ce komai ba saboda kunya. Iyalin Baffa ne suka sha zagi tas a wurinta na Dahiru ya ma fi na kowa bayan sun isa can gidansu Malam da Innar Fatihu. Lokacin duk sauran 'yan uwan Ade da na Baba kowa yana gidan.
Sun tausayawa Mawadda sosai yawancin matan harda kuka. Shirin tafiya Kano suka hau yi 'yan uwa kowa da ya mika abinda Allah Ya hore masa a matsayin tasu gudummawa saboda basu san yaya zata kaya ba.
*****
Katon gida ne suka je a Sharada housing estate. Dahiru bakon birni sai bude baki yake bai taba ganin gida irin wannan ba.
Gida ne mai kyau ga filawoyi sun kawata shi. Can gefe kuma motoci ne wurin shida masu kyau da gani zasuyi tsada shine tunanin Dahiru.
A wajen maigadi Oga Sani ya barsu ya shiga ciki. Bai wani jima ba ya dawo ya kira su. Wata mata ce ta fito a daidai bakin kofa ta tsaya su kuma suna daga gefen matattakalar da za'a taka mai gudu shida ya isa inda take tsaye. Gaisheta suka yi a mutumce ta amsa tana faman yatsina.
"Sani wanne ne zaiyi aikin a cikinsu?"
Dahiru ya dan dago kai yayin da Oga Sani ya dafa kafadarsa "wannan ne sunansa Dahiru"
Kallonsa tayi ta dan tabe baki "Aikin share farfajiyar gidan nan da gyara flower zaka yi. Sai kuma duk asabar zaka rinka yi mana wanki nawa da na yaran gidan. Ranar lahadi ka goge ko babu wuta za'a tayar da inji. Idan aikin yayi maka albashinka dubu ashirin"
Tsabar murna Dahiru bai san lokacin da yace "ahirin???" ba.
Wata irin dariya suka ji an kwashe da ita daga bayansu. Yarinya ce budurwa ta fito daga cikin motar da take a kunne tun zuwansu taci ado sosai.
Dariya take har tana rankwafawa ta kalli Dahiru "yaya sunanka?"
"Dahiru" ya bata amsa a takaice.
Tana dariya tace "Sannu Dashiru"
"Dahiru ne sunan" ya gyara mata a zatonsa bata ji bane sosai.
"To Malam Dashiru mai ahirin" ta sake kyalkyalewa da dariya.
Ransa in yayi dubu to ya gama baci. Hatta Bilya shima fuskarsa ta sauya.
"Kawu Sani ina ka samo mana 'yan ahirin?"
Hade fuska yayi sosai "bana son wannan shirmen naki Qariba"
Mamanta ta bata rai itama jin anyi mata tsawa "kai fa Sani idan kazo gidan nan to yaran nan basu da sauran sukuni"
"Yara ko magidanta? Kin ajiye dika-dikan yara saboda boko kunyi yi musu aure. Kuma kina kallo nazo da bako tana yi masa dariya don rainin hankali"
"Bakon naka ba me aikin gidansu zai zama ba? Kai kudin yayi maka zaka iya?"
A sanyaye Dahiru yace eh. Ya ma isa yace bazai iya ba tashi daya dubu ashirin a wata me ya manta.
Sunyi sallama da matar bayan an daidaita zai fara zuwa ranar litinin nan da kwana hudu kenan. Batun karatunsa wanda Oga Sani ya fada mata tace zasu daidaita idan an fara karatun a tsara yadda zai rinka aikin.
Sun juya zasu tafi Qariba ta daga murya tace "Malam Dahiru me ahirin sai monday" dariya ta rinka yi har ta shige cikin gidan.
Oga Sani yace masa sai yayi hakuri sosai da yaran dan uwansa. Shi maigidan Dr. Auwal rikakken dan boko ne wanda yake taba kasuwancin sayar da motoci yayin da matarsa Dr. Tani likita ce tana da asibitinta mai zaman kansa. Yaransu hudu maza uku sai Qariba mace kuma ita ce ta uku. Sangarta ta wuce tunani da gata yaran sun tashi dashi shiyasa zama dasu sai an kai zuciya nesa.
[08/01 : *GUMIN HALAK...*💰6
*Batul Mamman*💖
"Baffa anya ba zanje gidansu Mawadda ba da kaina?" Cewar Inna tana kallonsa ya zurfafa a tunani.
Dan guntun tsaki yayi "kije kice kinzo bada hakuri saboda 'yarki bakinta bashi da linzami ko"
"To naga ka kasa komawa kuma ance sun dawo. Danlami yace tun daga bakin titi ake binsu da kallo nasan surutun ma sai anyi"
Takaici ne kawai yake cinsa a rai. Idan ya fita an rinka zundensa kenan ko shine Mal Fatihu sai haka. Wasu har cewa suke Dahiru ne ma yayi mata fyaden. Wasu kuma suna ganin bai kyauta ba sun tonawa surukansu asiri saboda tsautsayi ya fadawa yarinyar. Yanzu ta yaya zai dawo da mutumcinsa a gari? Tashi yayi ya zura takalmansa yayi waje Inna na kiransa bai ko saurareta ba ya fita.