Sashe 40
Gumin Halak Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bin bayansa ta yi tana ta cewa ba'a yiwa Qareeba fyade ba yayi tafiyarsa ya kyaleta. Da ta koma tsareta Dr Auwal yayi tana kuka take bashi labarin komai tun daga zuwan Mawadda asibitin har yadda suka yi da Haj Mara da shigarsu kotu.
Qareeba tana ji tayi ta kuka saboda ita mahaifiyarta ta bada shaidar zur ta batawa wata rayuwa. Batun Alh Munzali kuma alkalin da ya yi shari'ar Justice Dawud ashe kanin abokinsa ne bata sani ba. Ta manta wani lokaci da rashin haihuwa ya damesu Alh Munzali ne yayi sanadiyar hadata da matarsa har aka dace. Ranar da taje kotun bada shaida bata gane shi ba. Shine ya tuna ta har yake fadawa dan uwansa ya ga likitan nan yau a kotunsu wanda Alh Munzalin yaji labarin a wurinsa. Baiyi kasa a gwiwa ba har gida yaje ya sameta saboda ya bincika ya gane shine wanda aka ce zai auri Qareeba a lokacin. Dr Tani ta shafawa idonta toka tace karya ne kuma ta kula dukkansu 'yan uwan nata basa son yaranta su cigaba. Yayi bakinciki sosai a lokacin yace mata taje da sannu duniya zata bayyana mata halin yaron domin yayi bincike a kansa ya kuma tabbatar bashi da tarbiyya. Gashi kuwa ta gani zahiri.
Dr Auwal ransa yayi matukar baci "shine kika boye min abu mai girma irin wannan saboda kina son 'yarki tayi aure? To gashi nan kin bada shaida an sake shi yazo ya lalata miki taki 'yar. Auren da ki ka so tayi kuma bai yiwu ba."
Hakuri ta shiga bashi yana rike da hannun Qareeba yaki kallonta " Kuma bai sami nasarar yi mata fyaden ba mu ka je dakin"
"Da gaskiyar Alh Munzali tunda asibitinki ne nan nayi imanin zaki yi duk yadda zaki iya ki rufe maganar "
"Daddy zan gyara al'amarin nan wallahi ko zan rasa aikina sai na kulle Marakisiyya da danta. Amma ku yarda Allah bai bashi dama akanta ba"
Tana ta magana bai sake ce mata komai ba har 'yan uwansu 'yan ganin kwaf su ka fara taruwa zance ya bazu kamar gobara an yiwa Qareeba fyade.
*****
BB da ya bar gidansu Qareeba wani abokin shashancinsa ya nema yazo ya dauke shi saboda ya kasa tuki. Hanci jini baki jini jikinsa ya bugu sosai Dahiru ya tara masa gajiya.
Kashe wayarsa yayi don yasan Haj Mara zata kira. Shi kuwa burinsa ya cika wannan wawiyar Qareeban yanzu ko giya iyayenta ke sha dole su sarara masa. Takaicinsa daya da bai samu ya karasa ba sai kuma tunanin waye wannan mutumin da yazo har ya dake shi haka. Ko bacci ya kasa yi saboda rashin sanin mutumin da sunansa. Ya sawa ransa don sun fado masa a bazata ne amma ranar da zai sake haduwa dashi sai ya nuna masa shi BB ba'a ja dashi.
******
'Yan uwan Mawadda su Rafia duk suna gidan yau ana ta tsare tsaren biki. Jinsu take yi wai ita ce zata yi aure abin kamar almara. Gani tayi har azahar ta wuce yau Dahiru bai kirata ba ta tashi ta barsu a tsakar gida taje ta kira shi.
Yana zaune a falon Baba Prof ana masa gyaran targade. Hannunsa na dama garin dukan BB ya sami targade bai sani ba sai cikin dare wurin babban yatsansa ya kumbura ya soma damunsa da ciwo. Abu harda su zazzabi karfe takwas ya kira Attahir shine ya taho dashi gidan. A hanya kafin su zo yake bashi labarin abinda ya faru.
"Ina ma tare muke wallahi bayan munyi masa duka mu dandake matsiyaci. Irinsu fa kamata yayi a mayar dasu huhulahu ta yadda ko sun ga mace nan gaba iyakar su da ita ido"
"Gara da baka gani ba Bro, da abin na kwana a raina ya dameni matuka. Da shi da wanda ya yiwa Mawadda jiya na tsine musu yafi a kirga."
Ana gyara hannun yana gumin wahala ta kira har sau biyu. Attahir ne ya dauki wayar a kira na uku yace mata ana masa gyara zai kira idan an gama.
Tunda taji haka hankalinta ya kasa kwanciya ko hirar ta kasa da yayyenta. Bayan minti goma ta sake kira Attahir ya kuma dauka.
" 'Yar uwarmu an gama amma kinsan mutumin nawa rago ne kuka yake yi shiyasa na karbe wayar"
Dahiru ya tashi yana cewa ya bashi ya hana. Yadda yaji ta damu sosai yace ta kwantar da hankalinta zai kawo mata shi yanzu.
"Baka tausayina zaka ce na fita yanzu" Dahiru yace yana karbe wayarsa.
"Naji kamar tana kuka ne" ya zolaye shi.
"Waye ma yace ka daukar min waya?"
Sai da ya huta yaci abinci sannan suka tafi da Attahir din. Da ya kirata yace suna waje cewa tayi su shigo ciki.
Shi kadai ta samu a zaune ta tambaye shi ina Attahir tana kallon hannun.
"Na kora shi waje"
"Yaya hannun?" Tace da damuwa.
"Ni fushi nake tun safe baki neme ni ba"
"Yayanmu kaine fa jiyan nan..."
Yayi murmushi "me nayi jiyan?"
"Babu komai"
"Ashe dai kina sona Attahir yace kinyi kuka da ya fada miki"
"Ba wani nan kaine yace kayi kukan. Naso in gani sai na tara bokiti"
"Kinci bashi yarinya. Bari na tashi zazzabi nake ji. Hankali ya kwanta kin ganni ko" yace da dariya.
Ita ma tace "Kai naka bai kwanta ba da ka ganni?"
"Sosai kuwa Mawaddatan wa Rahma. Saura kwana 8 kina tayani kirge kuwa?"
Dariya tayi suka mike tare tana masa Allah Ya kara sauki.
Ya karkace kai yana kallonta "kina jindadinki"
"Me kuma nayi?"
"Nine mara lafiya, ni na kawo miki kaina ki dubani sannan ko rakiya babu."
Murmushi tayi masa "Allah Ya baka hakuri muje"
Tare suka fito waje suna yiwa juna murmushi Attahir yana hira da tasa masoyiyar Nawal ya hango su sun burge shi.
Daga bayan motar babban yaron Garwashi ne Danmani ya saitasu ya dauke su hoto a kofar gidan. Dariyar mugunta yayi shi kadai. Garwashi kwatancen karya ya yiwa BB duk da sun gano ainihin gidan harda batun aurenta da za'ayi. Batare da bata lokaci ba BB ya turo musu kudin wanda suka raba su bakwai. Shine Danmani ya zagaye shi kadai ya dauko hoton duk da baisan waye Dahiru a gareta ba. Burinsa ya dauketa a kofar gidansu dama. Wayarsa ya tura a aljihu ya nufi titi yana fito zai je ya saidawa BB a farashi mai tsada.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰16
*Batul Mamman*💖
Baba ya kalli Attahir da tausayin Dahiru ya tsinka masa zuciya "samari yaya sunanka?"
Amsa masa yayi jiki a sanyaye. Baba yace ya tafi da Dahiru gida don ya sami nutsuwa shima ciki zai koma ya duba Mawadda.
Sai da ya fita Attahir ya kwashe wayoyinsu ya dago Dahiru. Ko kofa basu kai ba aka soma kiran sallar Magrib. Marwanu ne ya fito cikin sauri yace Baba yace su jira shi zai fito suje masallaci kafin su tafi.
A ciki dakin su Inna aka kwantar da Mawadda. Kuka take yi sosai mai cin rai su Yaya suna rarrashinta amma ta kasa shiru. Rabonta da irin wannan firgicin anfi shekara. Tun wata rana da tana cikin adaidaita sahu suka tsaya a danja. Gefe da gefe maza ne akan babura sun matsi adaidaitan. Abinka da 'yan tasha suka fara yi mata zantukan banza bata san lokacin da ta fara ihu ba. Abu ya kaita da suma ranar ne ta fara haduwa da Dr Imran.
Yau kuwa kukan bakincikin nakasa ta da BB yayi take yi. Wannan abu ya kara tabbatar mata aure bai kamaceta ba domin da wahala matuka ta iya rayuwa da miji. Bata jin akwai wata soyayya da zata sa namiji ya iya hakuri da matar da bazata iya kebewa dashi ba batare da tsoro da fargabar kada ya tabata ba.
Ade tun tana rarrashinta itama har ta soma fada karshe ta fashe da kuka. Tashi tayi ta fita daga dakin ta barsu da Yaya. Zuciyarta bata iya jurewa kukan Mawadda don tasan yarinyar ta ga rayuwa.
Kuma a haka ma don tana da dauriya ne.
Bayan sun dawo hakuri Baba ya sake basu Dahiru ko uffan bai iya cewa har suka tafi. Gani yayi Attahir ya dauke hanya alamun gidan Baba Prof zasu koma yace ya kaishi gida baya jindadi.
Idonsa akan titi yace "nasan baka jindadin shiyasa bazan bari ka kwana kai kadai ba yau."
"Attahir please" yace da kyar.
"Sai dai kayi hakuri idan ba haka ba zan sanar da Baba halin da ake ciki.Kuma ka manta motarka na can?"
Taga ya koma kallo bai kara magana ba sai tunane-tunane. Suna zuwa dakin Attahir din ya wuce ya kwanta. Shima sai ya rabu dashi don yasan yana cikin damuwa.
Sai bayan isha ya matsa masa suci abinci yace ya koshi.
"Sannu baban soyayya abin kuma harda hora kai da yunwa? Dadin abin gidansu Anti Qareeba babu nisa..."
Saurin kallonsa Dahiru yayi shi kuma yayi dariya sannan yace "na rantse ko kaci ta dadin rai ko kuma naje gidansu na kirawota. Nasan zata zo kaga sai a nunawa su Haj Mama"
Tsaki Dahiru yaja sannan ya dauki cokali kamar shine ya bata masa rai ya rinka tura abincin da kyar.
Can dare bacci ya gaza daukarsa. Tunaninsa bai wuce wane hali Mawadda take ciki ba. Da abin ya isheshi alwala ya dauro ya soma nafila da addu'o'i a nan kan abin sallah bacci ya dauke shi.
*****
Wayarsa ce take kara alamun kira ya bude idanu da kyar. Karfe goma da rabi ya gani ya tashi yana dafe kansa dake matsanancin ciwo. Da kyar yayi sallar asuba ma saboda ciwon kan. Bilya ne ya kira shi Baffa da Inna sun zo suna gidansa. Amma Baffa yace bazai kwana a Kano ba saboda haka yayi sauri ya zo ya kaisu gidan Mal Fatihu.
Da sauri ya mike yayi sa'a ba ranar aiki bace. Attahir ne ya shigo ya ganshi yana saka kaya cikin sauri.
"Sai ina koma Baban soyayya? Yaya kan naka"
Dube dube yake da sauri sauri "Attahir ina mukullin mota ta? Jiya sai da nace ka kaini gida gashi su Baffa sunzo ina nan"
Kafadunsa Attahir din ya rike "dakata mana, ni bansan ka da wannan garajen ba. Me yake faruwa?"
Qareeba tana ji tayi ta kuka saboda ita mahaifiyarta ta bada shaidar zur ta batawa wata rayuwa. Batun Alh Munzali kuma alkalin da ya yi shari'ar Justice Dawud ashe kanin abokinsa ne bata sani ba. Ta manta wani lokaci da rashin haihuwa ya damesu Alh Munzali ne yayi sanadiyar hadata da matarsa har aka dace. Ranar da taje kotun bada shaida bata gane shi ba. Shine ya tuna ta har yake fadawa dan uwansa ya ga likitan nan yau a kotunsu wanda Alh Munzalin yaji labarin a wurinsa. Baiyi kasa a gwiwa ba har gida yaje ya sameta saboda ya bincika ya gane shine wanda aka ce zai auri Qareeba a lokacin. Dr Tani ta shafawa idonta toka tace karya ne kuma ta kula dukkansu 'yan uwan nata basa son yaranta su cigaba. Yayi bakinciki sosai a lokacin yace mata taje da sannu duniya zata bayyana mata halin yaron domin yayi bincike a kansa ya kuma tabbatar bashi da tarbiyya. Gashi kuwa ta gani zahiri.
Dr Auwal ransa yayi matukar baci "shine kika boye min abu mai girma irin wannan saboda kina son 'yarki tayi aure? To gashi nan kin bada shaida an sake shi yazo ya lalata miki taki 'yar. Auren da ki ka so tayi kuma bai yiwu ba."
Hakuri ta shiga bashi yana rike da hannun Qareeba yaki kallonta " Kuma bai sami nasarar yi mata fyaden ba mu ka je dakin"
"Da gaskiyar Alh Munzali tunda asibitinki ne nan nayi imanin zaki yi duk yadda zaki iya ki rufe maganar "
"Daddy zan gyara al'amarin nan wallahi ko zan rasa aikina sai na kulle Marakisiyya da danta. Amma ku yarda Allah bai bashi dama akanta ba"
Tana ta magana bai sake ce mata komai ba har 'yan uwansu 'yan ganin kwaf su ka fara taruwa zance ya bazu kamar gobara an yiwa Qareeba fyade.
*****
BB da ya bar gidansu Qareeba wani abokin shashancinsa ya nema yazo ya dauke shi saboda ya kasa tuki. Hanci jini baki jini jikinsa ya bugu sosai Dahiru ya tara masa gajiya.
Kashe wayarsa yayi don yasan Haj Mara zata kira. Shi kuwa burinsa ya cika wannan wawiyar Qareeban yanzu ko giya iyayenta ke sha dole su sarara masa. Takaicinsa daya da bai samu ya karasa ba sai kuma tunanin waye wannan mutumin da yazo har ya dake shi haka. Ko bacci ya kasa yi saboda rashin sanin mutumin da sunansa. Ya sawa ransa don sun fado masa a bazata ne amma ranar da zai sake haduwa dashi sai ya nuna masa shi BB ba'a ja dashi.
******
'Yan uwan Mawadda su Rafia duk suna gidan yau ana ta tsare tsaren biki. Jinsu take yi wai ita ce zata yi aure abin kamar almara. Gani tayi har azahar ta wuce yau Dahiru bai kirata ba ta tashi ta barsu a tsakar gida taje ta kira shi.
Yana zaune a falon Baba Prof ana masa gyaran targade. Hannunsa na dama garin dukan BB ya sami targade bai sani ba sai cikin dare wurin babban yatsansa ya kumbura ya soma damunsa da ciwo. Abu harda su zazzabi karfe takwas ya kira Attahir shine ya taho dashi gidan. A hanya kafin su zo yake bashi labarin abinda ya faru.
"Ina ma tare muke wallahi bayan munyi masa duka mu dandake matsiyaci. Irinsu fa kamata yayi a mayar dasu huhulahu ta yadda ko sun ga mace nan gaba iyakar su da ita ido"
"Gara da baka gani ba Bro, da abin na kwana a raina ya dameni matuka. Da shi da wanda ya yiwa Mawadda jiya na tsine musu yafi a kirga."
Ana gyara hannun yana gumin wahala ta kira har sau biyu. Attahir ne ya dauki wayar a kira na uku yace mata ana masa gyara zai kira idan an gama.
Tunda taji haka hankalinta ya kasa kwanciya ko hirar ta kasa da yayyenta. Bayan minti goma ta sake kira Attahir ya kuma dauka.
" 'Yar uwarmu an gama amma kinsan mutumin nawa rago ne kuka yake yi shiyasa na karbe wayar"
Dahiru ya tashi yana cewa ya bashi ya hana. Yadda yaji ta damu sosai yace ta kwantar da hankalinta zai kawo mata shi yanzu.
"Baka tausayina zaka ce na fita yanzu" Dahiru yace yana karbe wayarsa.
"Naji kamar tana kuka ne" ya zolaye shi.
"Waye ma yace ka daukar min waya?"
Sai da ya huta yaci abinci sannan suka tafi da Attahir din. Da ya kirata yace suna waje cewa tayi su shigo ciki.
Shi kadai ta samu a zaune ta tambaye shi ina Attahir tana kallon hannun.
"Na kora shi waje"
"Yaya hannun?" Tace da damuwa.
"Ni fushi nake tun safe baki neme ni ba"
"Yayanmu kaine fa jiyan nan..."
Yayi murmushi "me nayi jiyan?"
"Babu komai"
"Ashe dai kina sona Attahir yace kinyi kuka da ya fada miki"
"Ba wani nan kaine yace kayi kukan. Naso in gani sai na tara bokiti"
"Kinci bashi yarinya. Bari na tashi zazzabi nake ji. Hankali ya kwanta kin ganni ko" yace da dariya.
Ita ma tace "Kai naka bai kwanta ba da ka ganni?"
"Sosai kuwa Mawaddatan wa Rahma. Saura kwana 8 kina tayani kirge kuwa?"
Dariya tayi suka mike tare tana masa Allah Ya kara sauki.
Ya karkace kai yana kallonta "kina jindadinki"
"Me kuma nayi?"
"Nine mara lafiya, ni na kawo miki kaina ki dubani sannan ko rakiya babu."
Murmushi tayi masa "Allah Ya baka hakuri muje"
Tare suka fito waje suna yiwa juna murmushi Attahir yana hira da tasa masoyiyar Nawal ya hango su sun burge shi.
Daga bayan motar babban yaron Garwashi ne Danmani ya saitasu ya dauke su hoto a kofar gidan. Dariyar mugunta yayi shi kadai. Garwashi kwatancen karya ya yiwa BB duk da sun gano ainihin gidan harda batun aurenta da za'ayi. Batare da bata lokaci ba BB ya turo musu kudin wanda suka raba su bakwai. Shine Danmani ya zagaye shi kadai ya dauko hoton duk da baisan waye Dahiru a gareta ba. Burinsa ya dauketa a kofar gidansu dama. Wayarsa ya tura a aljihu ya nufi titi yana fito zai je ya saidawa BB a farashi mai tsada.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰16
*Batul Mamman*💖
Baba ya kalli Attahir da tausayin Dahiru ya tsinka masa zuciya "samari yaya sunanka?"
Amsa masa yayi jiki a sanyaye. Baba yace ya tafi da Dahiru gida don ya sami nutsuwa shima ciki zai koma ya duba Mawadda.
Sai da ya fita Attahir ya kwashe wayoyinsu ya dago Dahiru. Ko kofa basu kai ba aka soma kiran sallar Magrib. Marwanu ne ya fito cikin sauri yace Baba yace su jira shi zai fito suje masallaci kafin su tafi.
A ciki dakin su Inna aka kwantar da Mawadda. Kuka take yi sosai mai cin rai su Yaya suna rarrashinta amma ta kasa shiru. Rabonta da irin wannan firgicin anfi shekara. Tun wata rana da tana cikin adaidaita sahu suka tsaya a danja. Gefe da gefe maza ne akan babura sun matsi adaidaitan. Abinka da 'yan tasha suka fara yi mata zantukan banza bata san lokacin da ta fara ihu ba. Abu ya kaita da suma ranar ne ta fara haduwa da Dr Imran.
Yau kuwa kukan bakincikin nakasa ta da BB yayi take yi. Wannan abu ya kara tabbatar mata aure bai kamaceta ba domin da wahala matuka ta iya rayuwa da miji. Bata jin akwai wata soyayya da zata sa namiji ya iya hakuri da matar da bazata iya kebewa dashi ba batare da tsoro da fargabar kada ya tabata ba.
Ade tun tana rarrashinta itama har ta soma fada karshe ta fashe da kuka. Tashi tayi ta fita daga dakin ta barsu da Yaya. Zuciyarta bata iya jurewa kukan Mawadda don tasan yarinyar ta ga rayuwa.
Kuma a haka ma don tana da dauriya ne.
Bayan sun dawo hakuri Baba ya sake basu Dahiru ko uffan bai iya cewa har suka tafi. Gani yayi Attahir ya dauke hanya alamun gidan Baba Prof zasu koma yace ya kaishi gida baya jindadi.
Idonsa akan titi yace "nasan baka jindadin shiyasa bazan bari ka kwana kai kadai ba yau."
"Attahir please" yace da kyar.
"Sai dai kayi hakuri idan ba haka ba zan sanar da Baba halin da ake ciki.Kuma ka manta motarka na can?"
Taga ya koma kallo bai kara magana ba sai tunane-tunane. Suna zuwa dakin Attahir din ya wuce ya kwanta. Shima sai ya rabu dashi don yasan yana cikin damuwa.
Sai bayan isha ya matsa masa suci abinci yace ya koshi.
"Sannu baban soyayya abin kuma harda hora kai da yunwa? Dadin abin gidansu Anti Qareeba babu nisa..."
Saurin kallonsa Dahiru yayi shi kuma yayi dariya sannan yace "na rantse ko kaci ta dadin rai ko kuma naje gidansu na kirawota. Nasan zata zo kaga sai a nunawa su Haj Mama"
Tsaki Dahiru yaja sannan ya dauki cokali kamar shine ya bata masa rai ya rinka tura abincin da kyar.
Can dare bacci ya gaza daukarsa. Tunaninsa bai wuce wane hali Mawadda take ciki ba. Da abin ya isheshi alwala ya dauro ya soma nafila da addu'o'i a nan kan abin sallah bacci ya dauke shi.
*****
Wayarsa ce take kara alamun kira ya bude idanu da kyar. Karfe goma da rabi ya gani ya tashi yana dafe kansa dake matsanancin ciwo. Da kyar yayi sallar asuba ma saboda ciwon kan. Bilya ne ya kira shi Baffa da Inna sun zo suna gidansa. Amma Baffa yace bazai kwana a Kano ba saboda haka yayi sauri ya zo ya kaisu gidan Mal Fatihu.
Da sauri ya mike yayi sa'a ba ranar aiki bace. Attahir ne ya shigo ya ganshi yana saka kaya cikin sauri.
"Sai ina koma Baban soyayya? Yaya kan naka"
Dube dube yake da sauri sauri "Attahir ina mukullin mota ta? Jiya sai da nace ka kaini gida gashi su Baffa sunzo ina nan"
Kafadunsa Attahir din ya rike "dakata mana, ni bansan ka da wannan garajen ba. Me yake faruwa?"