← Book details Duk Karfin Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 80

Sashe 40

Duk Karfin Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

chike da bada umarni Ammi ta nuna Aryan da hannu ba tare da ta buɗe ido ba ta chigaba da magana "yanzu Khadijah ta zama nauyinka hakkine a kanka ka nema mata lfy sai ka shirya ya je ka nema mata magani idan kuma zaka iya zama da ita to zaɓi ya rage gareka" chikin sanyin murya Aryan yace "amma ya akayi ka kirata da Khadijah ba diyana ba ko dai har yanzu aljanin na nan ne bai fita ba kuma shine mai suna Khadijah" "ai Khadijah ne sunan ta ba diyana ba, da sunan Khadijah aka yanka mata rago, Khadijah na da bukatar abubuwa da dama daga gareka kayi amfani da matsayin da kake da shi ka nemo mata wasu ɓangarori na rayuwar ta" chikin sauri Aryan yace ban fahimta ba ɓangarori na yaruwar ta kuma kamar me kenan? Shiru sukaji Ammi ba ta sake magana ba sai ma wani attishawa da ta buga mai karfin gaske, shikenan sai barchi mai nauyi ya ɗauke ta

"Tirkashi to Aryan ka dai ji aikin da ke gaban ka ko" chewar Abba shiru Aryan ya ɗanyi kafin yace "Abba amma ya akayi sunan yarinyar nan ya sauya? ba tare da sanin kowa ba kuma ya akayi ko ita kanta bata san sunan ta ba? kuma wani ɓangarori yake magana kenan? ina son sanin asalin tushen yaran nan" miƙewa Abba yayi yana faɗin "sai dai ka nemi sanin asalin su ta fannin ma haifiyar su bata mahaifin su ba ta mahaifin su kam su Safras ne tushen su dan idan ba Aisha ba Bappan su bai da wasu yan uwa" shiru Aryan yayi na ɗan mintuna kafin ya miƙe ya saɓi diyana a saman kafatar sa ya fice da ita ya nufi part nashi, umarnin Abba ya bawa su Aunty Amarya akan su wuce ɗakin duba marasa lfy Aryan zai zo ya duba su, ba musu Aunty Amarya da Haidar suka wuce Omar dake sume kuwa Aryan ne bayan ya kai diyana ya dawo ya ɗauke sa, Abba da Ummi suna zaune kusa da Ammi suna jiran ta farfaɗo.

Uk

fitowa yayi daga ɗakin computers nashi bayan ya gama kallon su Ammi kai tsaye wajen hutawar sa na ɗaki ya nufa yana tafiya yana latsa wayar sa, zaune take a saman ɗaya daga chikin kujerun wajen sanin ba wanda yake zuwa wajen ne ya sanya tayi baje warata dan duk tunanin ta baya nan kuma ba zai dawo yanzu ba sai dare, sanye take chikin wasu shegun riga da wando sun matse ta sosai rigar yana da babban wuya kusan rabin tula tulan boobs nata awaje gashi ko breziya bata sanya ba hips nata kamar zasu fasa wandon ta baza gashin kan nan nata ko ɗan kwali bata sanya ba yau kam bare hijab dan tasan ba wanda zaizo wajen,ba karamin kyau tayi ba kamar yar india,tana riƙe da wayar ta tana buga game, ga wani haɗaɗen cofin glass dake saman table ɗin kusa da ita ta zuba ruwa mai sanyi a chiki idan tayi game ta gaji ta ɗau ruwa ta sha.

Jin tayi gaba ɗaya ta tsargu kamar wani yana kallon ta, slowly chikin tsoron abun da zata gani ta ɗago blue eyes nata, karaf idon ta ya sauka chikin nashi yana tsaye wajen ɗan karamin pool dake wajen ya harɗe hannu a kirji ya zuba mata ido, a tsorace ta miƙe jiki na kerma tazo ta raɓa gefen sa zata wuce hannu ya sanya ya damko gashin kanta da karfi ya jawota baya ya dawo da ita ta gaban sa suna fuskantar juna, tsuke fuska tayi dan ba karamin zafi jan gashin ta da yayi ya mata ba calmly da sexy Voice na shi ya fara magana "me ya kawoki nan? Bakin ta har bari yake lips nata sai kakkarwa suke tace "kayi hakuri yaya Prince bazan.... Bata karisa maganar ba ya ɗaura yatsa ɗaya a saman lallausan lips nata yace "shiiiiiii" shiru tayi shima yayi shiru ya zubawa tsoratachiyar face nata ido ita kuwa ganin ba zata iya kallon chikin gwayar idon sa bane ya sanya ta runtse idon ta, Almost 3mins suna tsaye a haka da kyar ta iya buɗe baki lips nata sai kerma yake tace "yaya Prince dan Allah kayi hakuri wlh zafin gashin yake min" kasa kasa yace "open your eyes now" chikin sauri ta waro blue eyes nata a kan face na shi tana jiran taji me zai che da ita "wai me nake miki ne da kike yawan kirana da mugu? Kara zaro idon ta waje tayi tana mamakin yaushe yaji tana zagin sa kuma "ba dake nake magana bane" da sauri tace "kayi hakuri yaya Prince ba zan sake ba"
"Nifa ba chewa nayi zaki sake ko baza ki sake ba chewa nayi me nake miki da har kike kirana da mugu kuma kika tsaneni" runtse ido tayi chikin tsoro hukuncin da zai mata idan ta faÉ—a masa ta fara magana

"kana kyamata kace baka sona baka son ganina komai na taɓa baka so,baka kaunar hanya ta haɗa ka da ni ma bare har jikin mu ya haɗu, ban san me na maka ba kamin irin wanan muguwar tsana duk da tsanar da kamin hakan bai hanani in sauke hankin ka dake kai na ba,hakan baya hanani kyautata maka amma komai nayi maka ba dai dai nayi ba....bata kai karshen maganar ba ya jawota ta faɗa saman faffaɗar kirjin sa da murya kamar mai raɗa yace "shikenan abun da ya sanya kike chemin mugu?har kike ikirarin kin tsaneni? Kasa magana tayi dan ji take kamar ba aduniya take ba,chi gaba yayi da magana "ok yanzu mun haɗa jiki kuma bana kyamar ki sai ki dai na kirana da mugu, because kalmar batamin daɗi" nan ma ahiru tayi ta kasa magana,hannu ya sanya ya ɗago habarta ya zubawa face nata ido, idon ta a lumshe dan gaba ɗaya kunyar sa take ji "open your eyes" slowly ta buɗe idon nata a kan face na shi "what is your name? Chikin sanyin murya tace "hiyana"shiru yayi bai sake magana ba sai hannun sa da ya ɗago ya ɗaura saman kanta a hankali ya shiga shafa lallausan bakin gashin kan ta, ya zagayo da ɗayan hannun sa ta bayan ta ya ɗaura saman kugun ta, kwantar da kai hiyana tayi saman kirjin sa ta lafe tana tunanin anya ba aljanin bane wannan ɗayan bangaren zuchiyar tane ya bata amsa da chewa idan ma aljani ne yau dai ba kin kwanta saman kirjin aljani mai kama da mutumin da kika fi so a rayuwar ki ba,tuna haka yasa ta kara lafewa a jikin sa tana shakar daddaɗar kamshin perfume na shi almost 10mins suna tsaye haka, kasa jure tsayuwar hiyana tayi dan ta lura Bgs ko shekara zasuyi a tsaye ba zai damu ba, kokarin zamewa take kasa dan kafofin ta sun gaji jin hakan ya sanya ya sunkucheta da hannu ɗaya ya koma da ita wajen kujerun dake rufar wajen, kwanchiya yayi da ita a saman faffaɗar kirjin sa kwantar da kanta tayi saman kirjin na shi tana ɓoye fuska,chi gaba da shafa lallausan bakin gashin kanta yayi, lokacin guda ya fara fita hayyacin sa dan daman shi mutun ne mai tsananin sha'awa, shi ya sanya dan ya kare kansa daga faɗawa neman matan banza yake allura,

ɗayan hannun sa ya ɗaura saman bayan ta yana shafawa a hankali, mutuwar kwance hiyana tayi ita har yanzu ganin abun take tamkar mafarki ne ko kuma aljanine yazo mata a suffar yaya Prince, tayi nisa chikin tunani bata ankara ba sai gani tayi ya juya da ita ta koma saman sofar shi kuma ya mata runfa da faffaɗar kirjin sa, waro blue eyes nata tayi waje ba shiri, tana kallon sa, lokaci guda tsoron sa ya dira mata a rai ganin yadda idon sa suka sauya zuwa jaa sosai chikin tsoro lips nata na kerma tace "yaya Prince in tafi ɗaki? Bai yi magana ba sai ma haɗe fuskar su yayi waje ɗaya a hankali ya kamo lips nata na kasa ya fara kissing, gaba ɗaya duk wani kofa da iska ke shiga a jikin ta ya buɗe domin ansan sakon da yaya Prince ke aika mata duk wani jini dake gudu a jikin ta sai da ya tsaya chan,ya baiwa sakon yaya Prince hanya ya wuce, sosai yake kissing nata tare da shafa gashin kan ta da hannu ɗaya, almost 10mins yana kissing nata kafin ya sake ta tare da miƙewa zaune chikin da sarke war murya yace "jeki kawomin abinci" tun bai kai karshen maganar ba ta miƙe da gudu ta barwajen

Masu karatu sai mun haÉ—u gobe idan mai dukka ya kaimu

💖The Talent Troupe Writer's 💖

💖Story And Written💖
⬇️
*Star lady*

Wanna page É—in nakine Hauwa'u jidda maman Abba ina godiya da comments naki ina matikar farinciki da jin daÉ—i Allah ya bar zumunci

Book 2

Page 20

_______A gigice hiyana ta farka daga nauyayyar barchin da ya take juyawa tayi tana yan waige waige hannu ta sanya a saman lips nata da ɗan karfi tace "daman duk wanan kiss da yaya Prince yamin ma farki ne,ina ma wanna daɗɗaɗar mafarkin ya zama gaskiya ya Allah ka nunamin ranar da yaya Prince zai min kiss" ɗago ido tayi tana bin ɗakin da kallon chikin sauri ta diro kasa daga saman gadon dan tana tabbacin yanzu yaya Prince ya dawo, lallaɓawa tayi ta leƙa wajen hutawar sa chan ta hangosa zaune ya manna waya a kunne da alama waya yake chikin sauri ta juyo ta dawo chikin ɗakin ta ɗauki hijabin ta ta sanya ta fice waje ta nufi kitchen, dan shirya masa abinci
Chapter 40 · 0% Book details