← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 83 OF 86

Sashe 83

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Abunda ta fad'a kenan ta mik'e ta shige ciki,y'an mintuna da basu haura talatinba ta fito rik'e da hannun KHUBRA data sha ado cikin wani rantsatstsen less mai kalar sea green sai yarfan duwatsu kalar gold,tana ta fana shek'a k'amshi,fuskarta tasha light make-up tana zuba murmushi ta cikin mayafinta daya rufe mata fuska,dan dama a ranar kam tun da yazo UMMI bata bari ya ganta ba,sai dai y'ay'ansa da yaketa faman yiwa wasa,idan ya d'auki wannan ya ajiye ya d'auka wannan,sai dai da gani kasan LITTLE KHUBRA ta musamman ce a gurinsa...
Fuskarta a lullub'e da mayafinta kalar duwatsun kayanta da plat shoe a k'afarta,a hankali har suka iso gabansa,idanunsa tun da suka fito yake kansu bakinsa yak'i rufuwa saboda tsanamin farin ciki har tsaye ya mik'e bai saniba,hannunsa UMMI ta kama ta d'ora na KHUBRA aciki ta damk'e a nata,cikin sanyi ta d'an yi musu tak'aitacciyar nasiha sannan ta k'ara da fad'in cikin zolaya tana dariya
"To SON ga matar ka nan na baka....Allah yasa ba a soma fushi daniba.."
Dariyar shima yayi sannan ya rungume UMMI yana fad'in
"Na gode sosai UMMI'NMU Allah ya biyaki da mafificin alkhairin sakamako.."
Duka suka amsa da amin,sannan ya d'auki yaransa biyu UMMI ta d'auko LITTLE har bakin mota ta rakasu,inda KHUBRA ta zauna sannan UMMI ta d'ora mata LITTLE kan cinyanta tana fad'in
"To Allah ya tsare hanya,ya kuma karemin ku daga sharrin abun cutarwa...Sannan kuma idan Allah ya kaimu cikin satin nan zansa a nemo y'ar dattijuwar da zata na taimaka miki...Kinji ko DOUGHTER..?"
Godiya suka mata sosai mayafin KHUBRA lullub'e har lokacin a saman fuskarta,tana tallafe da y'arsu dake bacci sai k'amshi na musamman yaran keta zubawa kamar iyayensu.Sai da taga tafiyarsu sannan ta koma cike da farin ciki a zuciyarta mara misaltuwa.
Suna fita a get en gidan yayi parking gefe,jin ya tsaya yasa KHUBRA murmushi dan kam tasan Ogan nata yau sai yadda Allah yayi da su,tasan babu batun hak'uri a lamarinsa yau kam.Tana cikin tunani taji ya d'age mayafin kanta,da sauri ta kulle idanunta tana murmushi,murmushin shima yayi sannan ya d'auke LITTLE daga saman cinyanta,kanta ta jinginar jikin kujeran tana sauke numfashi a hankali,kusa da y'an uwanta ya kwantar da ita a back seat,sannan ya janyo KHUBRA dake mak'ale jikin kujera kamar idol.
Idanunta dake kulle ya kalla yana sakin murmushinsa mai tsada kamar idon nata a bud'e yake,kissing pore head enta yayi sannan idanunta,a hankali ya gangaro saman lips enta,sun jima a haka inda ta samu ta k'waci kanta da k'yar tana mai da numfashin wahala,shi kansa gogan da k'yar ya samu ya daidaita gudun numfashinsa lokacin kad'an har ya tsinci kansa cikin wani duniya na daban,fizgar kan motar yayi yana ta faman murmushin da na kasa gane ma'a narsa......

《《》》

*GIDAN KHALEEL.*

Tun a wayewar garin ranar da KHUBRA take da kwanaki arba'in da haihuwa ZUHRA ta tashi da matsanancin zazzab'i mai zafin gaske,hankalin KHALEEL idan yayi dubu ya tashi saboda yadda jikinta yake ga amai da taketa fama da shi,yini guda har ta fita a hayyacinta,tausayinta duk ya cika KHALEEL,yana nan zaune rik'e da ita a jikinsa DR yazo,ko bayan da aka dubata DR ya gama y'an bicikensa nan ya tabbatarwa da KHALEEL tana da shigar ciki na kimanin wata uku da sati guda,murna gurin KHALEEL kamar zaiyi me dan dad'i.
Sai dai kuma wani abu cikin na ZUHRA da alamun mai wahalarwa ne,dalilin daya sa KHALEEL ya yanke shawarar tattara musu y'an kayan da zasu buk'ata,ya tattara ta suka nufi gidan UMMI..

Tafiyar su KHUBRA kenan babu jimawa motarsu ta kunno kai gidan,lokacin har UMMI ta gama shirin kwanciya kenan sallamarsu tasa ta fito.
Ganinsu a lokacin harda luggage's ta saki baki tana kallonsu.Bayan sun gaisa KHALEEL ya mata bayanin komai,murna gurin UMMI harda taka rawa saboda zata sake jin kukan jinjiri daga tsatsonta a karo na biyu duk da a yau ta rabu da wasu jariran sai dai fa wannan na musamman ne a gareta...
_Toh ZUHRA fatan Allah ya raba lafiya..._

《《》》

*INA LABARIN HAJIYA LAURA....??*

Nasan da yawa kuna da son jin yaya ta kasance a b'angaren HAJIYA LAURA....
Tun bayan da ta san illar abunda ta aikatawa HAJIYA MURJA da labari ya iskota da kuma rashin lafiyar ita HAJIYA MURJA'N,nanfa ta ttara inata-inata ta,duk wani abu na kud'i ta sai da shi da yake dama gidan na HAJIYA MURJA ne cikin abunda ABBA ya bari kafin ya bar k'asar,ta fice ta bar gidan da shirin tserewa k'auyensu,tana cikin tafiya da y'an kayanta cikin wata jaka,har Allah ya kawo ta tasha,cikin ikon Allah,tsautsayin ya afka mata a lokacin da take k'ok'in tsallaka titi,tana tafiya ba tare da ta kula da tahowar motarba,shi kuma mai motar shima baiga lokacin data shigo ba,take ko ya kad'eta kuma ba tare da ya tsayaba kasancewar a lokacin danja ta bawa gefensa hannu ya manni motarsa,suma HAJIYA LAURA tayi yashe a gurin wanda mutane suka samu suka maidata gefen hanya,taimakon gaggawa suka fara bata.Kafin daga bisani akayi asibiti da ita wanda likitoci suka shafe tsayin lokaci suna bata taimako.
Tsawon kwanaki biyu ta shafe a sume ba tare da tasan halin da take cikiba,sannan a kwana na uku ta farfad'o tana ta fana surutai kamar zararriya,da kyar likitoci suka samu suka shawo kan matsalar tata,sai dai fa wani abu HAJIYA LAURA duk k'ok'arin likitocin sun kasa hanyan da zasu tashi k'afarta,wanda a sakamakon had'arin HAJIYA LAURA ta rasa k'afarta d'aya da hannu.
Wannan abu ba k'aramin tada mata hankali yayi ba lokacin data koma hayyacinta,tayi kukan har hawayenta sun dena zuba,sai daifa tana nan da damuwa fal a ranta na rushewar lamarinta,haka dai take ci gaba da karb'ar kulawa daga malama'n asibitin kasancewar na gwamnati ne,batun magani kuwa sai dai idan Allah yasa sun samu kud'in dubiya daga gurin masu zuwa ziyara,idan kuma Allah yasa ta samu en sai ta samu ta fanshi magani da shi Wanda shima jimawa zai k'are....Abinci kuwa ba a maganarsa ma saboda bata da wanda zaiji k'anta ya d'auki d'awainiyar bata ko wane lokaci,bare kuma ayi maganar d'an jinya,wani lokacin sai dai ko a nan gadajen kusa da ita da suke tausaya mata su sanmata,a haka har Allah yasa ta shafe tsawon shekara guda a asibitin Wanda ba tare da an sallameta ba ta tsere.
Bakin danja ta samu nan take bara ta samu abunda za taci,tana yawo da sanda wanda ke taimaka mata tana tafiya,tayi bak'i ta rame bayaga kod'ewa da tayi wahala kullum k'aruwa take a kanta,kullum ta tuna abunda ya faru da ita sanadin rasa k'afar da tayi sai tayi kuka,ga dukiyar data tattara zata gudu tun da tayi had'arin bata sake ganin jakar tataba...
A kullum burinta a yanzun bai wuce zuwa neman gafarar HAJIYA MURJA ba sai dai tsoro ya hanata tunkarar gidan hajiyar.A haka har aka sake shafe shekara guda da fitowarta daga asibitin,kuma har wannan lokaci bata tara kud'in da a ganinta ta wannan hanyar zasu tarunba.K'ark'arinta ta samu abunda zata sai abinci ta ci.Gurin kwana ko ya zame mata abu mafi wuya ya kasance yanzun HAJIYA LAURA dake da d'akunan bacci iri daban daban yanzun sai dai bin rumfunan kasuwa........

*Alhaki kuikuyo kenan jama'a ga dai yadda k'arshen HAJIYA LAURA ya kasance,ta manta a sanadiyyarta ta jefa y'ay'a da dama cikin halin da yafi nata muni,tasa su kwana bakin kasuwa,da yawon neman abunda zasu rufawa kawunansu asiri tamkar mabarata,cikin garin da basu da kowa kuma basu da komai,ta manta da had'arin dake cikin bar in y'ay'ata mata a gaban iyayensu,wanda hakan dai² yake da siyan lasisin tarwatsa musu rayuwa..Duk ta manta da haka ta kuma toshe kunnuwanta a lokacin... Huh!!...Allah ya k'ara rufa mana asiri duniya da lahira..ameen...*

*COMMENT FOR MORE PAGE'S..........* 💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S [email protected]

*©®2018*
*11/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

6⃣5⃣

*LAST PAGE.*
Chapter 83 · 0% Book details