← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 81 OF 86

Sashe 81

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

KHUBRA ce kwance saman gado na majinyata masu haihuwa sai juya kai take gefe wasu nurse's na turawa daga kusa da kanta kuma BB ne yana ta faman shafa mata kai yana jera mata sannu cike da tashin hankali,har aka shiga da ita labour room en,sannan aka kulle yana waje bakin d'akin sai safa da marwa yake.
Tun yana kallon mintuna da suke shud'ewa kuma yana kallon k'ofar d'akin da aka shiga da ita,har hour guda yayi ba tare da an fito da itaba,daga hour d'aya aka tafi da rabi,sannan biyu,uku,hud'u,ganin abun bana k'are bane kuma hankalinsa na kanta gaba d'aya nutsuwa tayi masa k'aura,burinsa bai wuce sanin halin da take cikiba.
Wata nurse ce ta lek'o,jin an bud'e k'ofar yasa shi nufar gurin da sauri.
"Kaine JAAN ko waye nema ohooo...?"
Bai bata amsaba ya janyeta gefe had'e da shigewa,kallo ta bishi da shi ganin ya shige babu magana,bakin gadon ya nufa ganin cikin awanni hud'u da shigowarsu babu wani abu daya canja,duk ta gama galabaita,hannunta ya rik'o cikin nasa,idanunsa lokaci guda ganin halin da take ciki har sun gama sauyawa zuwa jaa,su kuma nurse's en sai faman damunta suke kan tayi nishi amma ina babu k'arfin yin hakan a tare da ita,gaba d'ayama sun gama bashi haushi kan tsayawa da sukayi suna b'ata lokaci tun d'azun kuma har lokacin babu sauyin da aka samu tun da suka shigo da ita,hannun long sleeve ensa ya nad'e cikin b'acin rai yace su bashi guri tunda basu san aikin suba,cikin ya shiga d'an dannawa a hankali kamar dai yadda akema masu ciki idan zasu haihu,yana kuma fad'a mata kalmomin da zasu bata k'warin guiwa,matsawa ya sake yi dai² bakinta ya sanya nashi ganin yadda take kwance tana sauke numfashi da kyar,iska ya shiga hura mata hannunsa d'aya na kan cikin yana ci gaba da daddanawa a hankali.
Cikin y'an mintuna da shigowarsa ta samu d'an k'warin jiki,nishi mai k'arfi yayi escafe a tare da ita,wanda ya bawa kan jaririnta damar fara fitowa,da sauri nurse's en suka matso,da taimakon Allah sannan da nasu taimakon suka janyo jaririn,cikin y'an mintuna ta sake sabon yunk'urin wani nak'udan take wani sabon jaririn ya sake kunno kai,a tak'aice dai sai da aka zaro jarirai uku daga jikin KHUBRA.
Ko ta kan jariran bai biba,in da matarsa take ya nufa yana jera mata sannu da Santa mata albarka,itako sai maida numfashi take da kyar Dan da ganinta ko ba a fad'a ba kasan ta sha wahala,duk jikinta yayi sweat en wahala,mouth to mouth ya shiga sake mata ko dan ta samu daidaituwar numfashi.............

*COMMENT FOR MORE PAGE'S.......* 💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S [email protected]

*©®2018*
*10/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

6⃣4⃣

*SECOND TO THE LAST.*

*BIGGY* kuwa tun bayan daya samu aiki a revenue office,wato ofision tattara haraji,ya daina wani aiki da yake a baya,wanda ba k'aramin mamakinsa yaransa suka yiba na ganin chanji lokaci d'aya a tare da shi,da farko sun ci gaba da zama cikin gidan nasa sai dai kuma daga baya lokacin da zai yi aure kuma har lokacin akwai wasu halayya nasu da basu dainaba,dalili kenan daya sashi yanke shawaran rabuwa da su dan kada wata rana su janyo masa bala'in daya fi k'arfinsa.
Wata rana bayan ya zaunar dasu a parlour nan ya shiga yi musu nasiha yana janyo musu ayoyi da hadisai cikin abunda Allah ya sanar da shi na daga ilimi,jin ruwan ayoyin daya ke janyowa wanda suke tsoratarwa zuwa ga masu aikata halaye irin nasu dama wasunsu da kuma narkon azaba da aka tanada ga mai aikin yasa su kuka,basu tashi a gurinba sai da sukayi masa alk'awarin in sha Allah suma sun daina,yayi farin ciki sosai da hakan ya faru,nan yake shaida musu zaiyi aure nan bada jimawaba suka masa fatan sanyawar alkhairi,tun daga nan ya sallamesu da kud'ad'en da yasan idan har sun rabu cikin su babu wanda zuciyarsa zata kawo masa d'aukan abun wani ko kuma su koma irin waccan rayuwar.Tun da suka yi sallama da shi a lokacin ya musu fatan alkhairi shi kenan basu sake had'uwa ba,shima bayan sun bar gidan ya shiga parking kayansa,dillallai ya samu sukayi cinikin gidan da kayan gidan gaba d'aya,take ko ya sai da shi da komai daga shi sai kayan jikinsa ya fito daga gidan,ko bayan ya bar gidan ya d'an kwana biyu a hotel sannan daga baya ya samu wasu dillallan suka samo masa gida a wani unguwan daban,nan BIGGY ya koma da rayuwarsa,wanda kuma nan ne aka kai masa amaryarsa wato ASHNA wacce a yanzun take MAMA ga d'ansu MUHAMMAD AL'MUSTAPHA....

《《》》

*INA LABARIN BOKA...??*
BOKA kuwa tun bayan da LADIYO ta masa wannan gani a ranar da MALAM BUBA yayi musu mugun kamu bai sake dawowa gurinta ba dalilin da yasa kuwa hakan ta faru shi ne,a lokacin bayan ya bar gidan LADIYO daga nan wani gari ya wuce wanda a wannan garin akwai wani malami mahaddacin al-k'ur'ani,tun da Allah yasa wannan bawan Allah yayi aure da matarsa d'aya wacce take fitinanniya tun tana yarinya kamar su LADIYO,tun bayan aurensu data ga ba irin wanda za tayiwa duk abunda ranta ke so bane yasa ta shiga bin malamai y'an tsubbu da bokaye duk akan tana neman abunda zata malakke shi,sai daifa hak'anta yak'i cimma ruwa sakamakon shi wannan bawan Allah ako da yaushe zaka tarar da shi cikin alwala kuma yana tilawar al-k'ur'ani,a biye-biyenta ne suka had'u da BOKAN su LADIYO,wanda a ranar da MALAM BUBA ya gansu bayan ya bar nan bai zame ko ina ba sai gidan wannan malami daya fita sallar asubah kasancewarsa limamin garin nasu,kamar ko wane lokaci bayan an idar ya zauna tilawa nan a k'ofar gidan nasa yana cikin karatu,almajiransa da sauran datijjan garin masu sha'awar neman karatu suna zaune nan gaba gare shi a haka har gari yayi haske sosai..

Can ko a gidan MALAM lokacin matarsa na tsaka da bacci gari har yayi haske tana ta faman bacci bata saniba bare ta tashi ta gaida mahalicci,zuwan bokan shi ya tasheta wanda tana yin arba da shi tayi dariya kasancewar dama sun saba,haka suka shiga aikin gabansu kamar kowane lokaci.K'arfi,mu'ujiza da girman kalmomin da ake karantawa k'ofar gida suka fara tasiri cikin gidan malamin wanda suka yi sanadiyyar daya janyo jikin boka cikin lokaci k'ank'ani ya fara hayak'i,faruwar hakan ke da wuya matar malam ta daka tsalle had'e da ingije shi daga kanta ta fice a guje daga d'akin,a tsakar gida ta tsaya tana raba ido tunawa da irin hukuncin da za a mata a garin idan har aka san abun da ta aikata yasa ta fashewa da kuka dan kam muddin malam ya sani tofa lallai ne jefeta za ayi da ranta har sai ta daina motsi kuma mutane salihai ba za su mata jana'iza ba,wannan dalili yasa ta k'ara k'arfin kukan nata,babu b'ata lokaci ta jaa mayafinta ta fice da gudu a gidan saboda wani tunani da tayi na bar in garin tun kafin asirinta ya kaiga tonuwa,mutanen dake k'ofar gidan da suka ganta a haka suka bita da kallo ganin yadda take gudu iya k'arfinta,mamaki duk ya cika musu zuk'ata,tana cikin gudun ne kuma Allah ya kawo wani mai akori kura take ya banketa,dalili kenan da ko shurawa ba tayiba nan take rai yayi halinsa tace ga garinku nan sanadiyyar fashewa da kanta yayi wannan shi ya zama k'arshenta.

Shi ko boka a k'alla sai daya kwana biyu cikin d'aki ba asan ya mutu ba jikinsa har ya fara tsutsa,mugun warin da malam yaji shi yasa shi nufar d'akin sai dai warin ya wuce tunaninsa,da k'yar dai aka samu aka bud'e d'akin wanda aka fito da gawar boka dake kwance kan gadon matar malam,had'awa akayi da katifar gaba d'aya aka fito da ita,sai a lokacin mutane da dama suka fuskanci dalilin daya sa matar malam take gudu waccan ranar,tasan abunda ta aikata shi yasa ta nemi guduwa,to yanzun dai ga abunda Allah ya nufa dasu duka babu wanda yake raye...
_Wannan kenan,su boka an tafi ga kuma yanda Allah yayi k'arshensa ya kasance dama wasu daga magoya bayansa...Allah ya karemu daga mummunan k'arshe._

《《》》

*INA LABARIN TABAWA K'AWAR LADIYO...???*

Tun bayan da LADIYO tayita zuwa gidanta akan tana neman taimakonta lokacin da take son neman MA'U a waya,a wani yammaci bayan zuwanta gidan lokacin suna zaune tsakar gida sai ga mijin TABAWA nan ya shigo,kamar ko wane lokaci nan TABAWA ta bud'e ido da murya iya k'arfinta zata fara zuba masa rash in mutunci Lamar yadda ta saba,take bata ko k'arasa fad'in abunda tayi niyyaba ya d'auke mata fuska da mari ganin yadda taci kwalarsa sannan ya shiga kora musu daga ita har LADIYO'N,kuma ya k'ara da cewa daga ranar kada ya kuskura ya k'ara ganin k'afar LADIYO a gidansa,duk kuwa ranar daya sake ganinta to ko shi kad'ai yasan me zai musu.
Tun daga ranar LADIYO bata sake yunk'urin zuwanba,dan dama mijin na TABAWA mugun masifaffe ne,dalilin sakkowar tasama kuwa ya had'u da k'arfin asirine.
Bayan tafiyar LADIYO ya zauna ya wanke TABAWA tsaf sannan ya k'ara mata da cewa zai yi aure idan kuma har ta sake ko da kallon banza tayi wa matarsa to ta kuka da kanta.

Ko bayan da yayi aurenma,ko kad'an TABAWA bata da wani power a gidan,hasalima ko k'ofar gida ya hanata zuwa bare ta shiga mak'ota,rayuwa tayiwa TABAWA k'unci a gidan mijin nasu,wanda ta koma tamkar baiwa a gurin uban gidanta,haka ta koma duk wani aiki na cikin gidan ya dawo kanta bata da sauran katab'us....
_Hattara ga masu hali irin nasu TABAWA,LADIYO,MA'U,BOKA,MATAR MALAM da sauransu,kunga dai yadda k'arshensu ya koma mask iron wannan hali tun kafin damar Ku ta kufce ya kamata kuyiwa kanku fad'a had'e da gyara tsakaninku da mahalicci dan duk Wanda ya mutu a haka Allah kad'ai ya barwa kansa sanin iron hukuncin da zai maka,Allah ya tsare my kuma ya tsare mana imaninmu..Ameen._

《《》》
Chapter 81 · 0% Book details