← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 86

Sashe 75

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Allah sarki y'ar uwa ta gari wallahi ki bari ke dai,ai ban baki labari ba,kwana biyu ne sai a slow wollah duk dare da wani irin zazzab'i nake kwana,shi nefa ogana yace lallai sai munje asibiti to ni nake k'in zuwa sai nace masa makaranta,shi nefa jiya na tashi da shi aiko shi ne yace mu tafi asibiti dana ce makaranta baki ga yadda yamin fad'aba har yana cewa lafiya ita ke gaba da komai.."
"Kai amma naji dad'i daya miki haka banda abunki ai oga gaskiya ya fad'a..."

"Ke dai bari kawai ai kuwa munje hankalinsa ya kwanta.."

"To ya jikin hope komai normal...?"

"Uhmm! ke dai bari inafa normal.."
Da sauri KHUBRA ta kalleta tana fad'in
"Kamar yaya kenan?"

"Babu komaifa da wasa nake miki,da sauk'i sosai sai dai kun samu k'aruwa.."
Wani ihu KHUBRA tayi tana rik'eta
"Wayyoo! kice min ciwon kenan dama.....To Allah ya raba lafiya,ubangiji ya kawo mana su masu alkarka.."

Wata y'ar class ensu ce ta lek'o da yake ta iya gulma da munafurci a makarantar coz idan kana neman expert ta munafukai ka samota to ka gama,nan take fad'in
*"AUFANA* lafiya kuke ihu da wannan safiyar..?"

Wani kallon k'asan ido KHUBRA ta mata tana fad'in
"Lafiya k'alau ko kinji ance miki ba lau bane..?"

"Au too..."
Ta fad'a tana barin gurin,yadda AUFANA taga KHUBRA tayi da fuska yasa ta yin dariya tana fad'in
"Kai CWEET SIS ki d'an saki fuska mana irin wannan had'e rai haka kamar wata BOSS.."
Dariya dukansu sukayi AUFANA ta furta
"Allah sarki harna tuna da wata mak'ociyata mai suna *JIDDAH* da take bani labarin yadda mijinta yake a da kafin a musu aure,wallahi ko da take fad'amin ita da sister enta *MEINERH LITTLE* sun sha wahalarsa shi yasa suke ce masa *YAH BOSS* amma kuma kafin aurensu da bayan sunyi aure data fuskanci halinsa shi kenan wai shi raini ne baya so shi yasa ya dinga musu haka..
Kuma yanzun haka wallahi idan kika ga yadda suke zuba luv sai kinyi mamaki,ammafa suna da kirki wollah musamman suka had'u su uku da wata sister en tasu mai suna *HUBBEEY* gaskiya ranar duk da suka zo har bana son mu rabu saboda y'an chapter ne.."

"Allah sarki Allah ya bar musu zumuncinsu.."
Inji KHUBRA dake k'ok'arin bud'e littafi don tana son yin nazari kafin malamin ya shigo

"Ameen ya Allah...aiko wata rana Allah ya kawoki suna nan wallahi zaki ji dad'in kasancewa da su...yini d'aya idan kukayi da su wallahi ji za kiyi kamar kun shekara da su,Allah dai ya had'aku nasan zaki k'aru da zaman da za kiyi da su sosai.."
Murmushi kawai KHUBRA tayi lokacin da take mai da hankalinta kan littafinta,itama AUFANA nan ta d'auko nata tana fad'in
"Yawwa teacher KHUBRA yau kece malamata dan kinga jiya ban zoba saboda haka amin bayanin lesson en jiya,nasan dai kam YAYA'N ki bazai barki ba sai yayi miki karatu na musamman.."
Dariya suka sake yi duka,can kuma suka tsunduma cikin karatu...

Suna zaune suna karatunsu,wani malami ya taho zai wuce bayansa da wata d'aliba itanma dai baza ta wuce tsaransuba a shekaru kallon-kallo suka yi da ita,kafin suka ci gaba da abunda suke yi,har malamin ya gota su,sai kuma ya dawo yana tambayarsu wane class suke,fad'a masa suka yi ya juya ya kalli wannan d'alibar yana fad'in
"Yawwa to kinga ga y'an uwa nan kin samu class enku d'aya da su,ki rik'esu su zasu baki masauki tunda sun jima a nan..."
Godiya ta masa sannan ta musu sallama suka gaisa a mutunce ta nemi guri ta zauna kusa dasu tana sauraron yadda KHUBRA ke zubo bayani kamar wata lecturer.Saboda yadda take bayanin karatun ko malamin nasu yaji dole ne ya sara mata saboda wani abun ma bai bud'a musu bayaninsa kamar yadda take yiba yanzun,sai da suka gama sannan AUFANA ta kalli bak'uwar tasu tana fad'in
"Sannu dai y'ar uwa..."
A mutunce itama ta amsa mata tana murmushi,saboda itama ba dai arhar dariya ba..

AUFANA tace
"Ni suna na AMINA UMAR FANA amma zaki iya kirana da AUFANA saboda sauk'ak'awa ma'anarsa kuma AU na farkon AUFANA yana nufin AMINA UMAR,shi ne idan kika had'a shi da FANA zai baki cikakken sunan,ita kuma y'ar uwata sunanta KHADIJA ABUBAKAR SA'AD,amma ana kiranta da KHUBRA."
Murmushi ta sakeyi tana fad'in
"Na gode sosai da amsata da kukayi...ni kuma sunana *MARYAM HAROUN SULAIMAN* amma ana kirana da *JANNAT*..."
Hira suka d'an tab'a kafin suka koma class saboda ganin teacher na tahowa...

Watanni sun sake zuwa har sun shud'e inda har sukayi jarabawoyi da dama wanda yanzun gashi har sun sake samun ci gaba na changing class..
Wata rana suna zaune suna hira su uku kasancewar yanzun sun zama su uku kuma k'awancensu babu algus cikinsa,suna ta hira a wata ziyara da suka kaiwa AUFANA da cikinta ya soma tsufa...
AUFANA ce ta kalli KHUBRA da JANNAT tana fad'in
"Sisters ena niko zanso jin labarinku da dalilin daya sa bakuyi karatu da wuriba musamman yadda naga Allah ya rufa muku asiri gidajenku da family enku babu talaka cikinku.."
Kallonta sukayi duka suna murmushi saboda irin shak'uwar da sukayi da juna yasa suka san da wasu sirrika na junansu,KHUBRA ce tayi gyaran murya tana fad'in
"Ai kuwa dai kam ya kamata musan dalilin dayasa mu duka haka ta faru damu,amma kafin naku bari kuji nawa...."
Gyara zama sukayi dukansu,nan ta shiga basu labarin gwagwarmayar da tayi fama da shi a rayuwarta,sai dai kamar wancan lokacin data b'oyewa BABA ZUWAIRA farkon had'uwarsu haka suma ta b'oye musu da sa hannun MAMA a saceta,da kuma wasu abubuwa da suka faru a matsayinta na wacce bata son aga laifin iyaye da danginta..Bayan ta k'are su duka hawaye ne kwance a fuskokinsu suna jinjina labarin nata da tayiwa lak'abi da *Y'AR GARUWA..*

"Lallai kin sha wahala sister amma haka Allah ya kaddara mana rayuwarmu...Badan lokaci daya k'ure ba dana baku nawa labarin sark'ak'iyata wanda nayiwa lak'abi da *"BAMBANCIN AL'ADU"* (My upcoming novel) amma ku biyo ni nan gaba in sha Allah duk ranar da muka sake samun sukuni zan baku labarina..."
JANNAT ta fad'a,cike da alhini suka rabu ranar da tausayawa halin da KHUBRA ta shiga wanda har ya kaita ga fad'awa sana'ar *GARUWA*..............

*COMMENT FOR MORE PAGE'S.........* 💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/
SMASHER,HUBBEEY,DIDEEYLOV & GENTLE NOVEL'S [email protected]

*©®2018*
*7/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~___________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

6⃣1⃣

*R* ayuwa nata dad'a tsayi zaman takewa na dad'a kawo shak'uwa da sabo baya ga k'imar juna da mutuntawa babu abunda ke yawo cikin wannan zuri'a ta *MALAM ABDU MAI ALMAJIRAI* wato *KAKA* duk wanda ya rab'esu ko to tabbas rabuwarsu bata zuwa face sun cika shi da d'umbin alkhairai.
A b'angaren zaman aure zuwa mu'amala ko duka yaran nasu kawunansu a had'e yake,ko da surukin gidan wato SADEEQ BIGGY ba lallai ne mutum ya ganeshi a matsayin suruki ba sai dai d'a saboda yadda su ABBA suka d'aukeshi,hankali da nutsuwa ko a gurinsa duk wanda ya sanshi a baya idan ya kalleshi a yanzun ba zai iya shaida shi ba saboda nutsuwa da yayi,shi da kanshi wani lokacin idan ya zauna yana tuna rayuwarsa ta baya sai dai kaga yana zubda hawaye,yasan ba kowa ya sashi yin irin wannan rayuwar ba face kishiyar mahaifiya,ba dan yana da ilimin addini dana zamani ba da yanzun kam yasan rayuwarsa ta gama wulak'anta,dalili kenan da idan ya tuna sai yayi k'walla.
Yaronsu ko AL'MUSTAPHA yanzun duk wanda ya kalle shi sai yayi mamakin girmansa saboda kulawa da ya samu cikin d'an lokaci yayi k'ato da shi.

Soyayyar KHALEEL da ZUHRA a wannan lokaci kuwa kamar zasu had'iye juna musamman da idan suna hiran rayuwarsu na baya,baya ga kasancewar a bayan ba wani luv sukayi ba a matsayinsu na b'oyayyun masoya ga BB da KHUBRA,idan kaga suna exchanging words na soyayya to tabbata a waya ne ko suna chat da junansu,yanzun kuma da suka samu dama sai abun nasu ya k'etare sanin mai sani.

Sosai KHUBRA ta maida hankali gurin karatu duk da dai kunsan rayuwar makaranta yau dad'i gobe akasin haka,amma a haka aka ci gaba da jalalla rayuwar da dad'i ko babu.
Cikin shekara guda da rabi da aurensu ta dad'a girma na ban mamaki duk da a gurin shi gogan har yau idan hira ya kawo su kan maganar girma yakan fad'a mata bata girma ba,wannan maganafa ta BB tana hasala KHUBRA a duk lokacin da yayi ta,shiganta makaranta da had'uwa da sababbin k'awayen nata yasa ta k'ara wayewa da gogewa,ta wani b'angaren kam takan yiwa Allah godiya bisa ga ni'imomi da yayi mata.
Yau tun da asubah da suka idar da sallah suka sake komawa cikin duvet,bacci mai dad'in gaske yayi gaba da su mak'ale da juna,sai wajen 10am sannan suka tashi cike da nishad'in zasu kasance tare a weekend en,su da kansu sun san zasu huta daga zurga-zurgan gurin aiki da skul.Sunyi wanka tare sannan suka had'a break fast kamar ko wane weekend suna cikin parlour zaune k'asa kan rug ya mik'e k'afafunsa,ita kuma tayi pillow da laps nasa,hiransu kamar kowane lokaci zuwa can maganar girma ya sake shigowa,cikin dariya da zolaya BB ya kalleta yana fad'in
"Babu wani nan nifa har yanzun baki girma ba a gurina..."
Kallonsa tayi k'asa-k'asa tana tab'e baki ba tare da ta kula shiba,shi kuma yaci gaba da tsokanarta
"Bayan har yau komai ni nake miki ke ko gwadawa baki tab'a yi ai ko in dai haka ne babu ranar da zaki girma ko JODI na.....?"

Kallonsa kawai ta sake yi tare da yin k'wafa yadda take rains mata hankali a ranta take fad'in
"Yau kam zan baka mamaki YAYANAH....Amma barin ga iya naka gudun ruwan.."
A hankali ta mik'e tana tafiya ta nufi hanyan bed room ensu,bata yi magana ba sai da taje dai² zata shige yace
"Baby ina zaki je ne..Babu ko neman rakiya...?"
Chapter 75 · 0% Book details