Sashe 82
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Kasa fita yayi daga labour room en yana nan rik'e da matarsa,inda yabar yaran hannun nurse's suna gyara su,cikin wahalalliyar murya na mutumin daya galabaita ta kalleshi da idanunta dake lumshewa suna bud'ewa,murmushi kawai yake zuba mata.
"JAAN MAMA fa da UMMA...?"
Ido ya fiddo waje dan sam yama manta da batun ya sanar musu,kansa ya dafe yana birkita gashinsa,alamun data gani kenan a tare da shi ta gane babu wanda ya sanarma.
"JODI...Basu saniba,ni kuma na manta ma da ya kamata ace na sanar musu.."
'Dan murmushin k'arfin hali ta masa ta sake lumshe idanunta,aljihunsa ya laluba da niyyan d'aukan waya ya kira su,sai dai wayam babu wayan,sai a lokacin ya tuna da bai d'aukoba,lower lip nasa ya cije tunawa da kayan dake shirye cikin d'an akwatin kawai ya d'auko shima kuma suna motan bayan su kuma bai d'auko wani abuba.
"Ya Allah...! Komai ma na manta daya kamata nayi..JODI wait a minute....I will be back right now.."
Yana fad'in haka ya mik'e had'e da bata fake a cheeks enta na dama,cikin sauri ya fice ya nufi mota,kayan ya d'auko ya dawo had'e da bawa nurse's en ya shaida musu zai dawo nan bada jimawa ba in sha Allah,daga haka ya fice cike da sauri yayi starting motan,direct daga nan gidan UMMA ya fara zuwa wato HAJIYA ZUWAIRA,tana ganin yana yinsa ta fahimci da akawai abunda yake faruwa,ganinsa sai murmushi yake zubawa yasa ta itama tayi murmushin tana fad'in
"Kada dai ka ce KHUBRA ta haihu...?"
Aiko dariya ya sake yana fad'in
"Haka ne UMMA'NMU...Yanzun ma na barota hospital,so saboda ba waya a jikina yasa ban samu na kira kowaba,yanzunma gida zanje na koma.."
Da murna sosai take godiya ga Allah bisa ni'imar da yayi musu,sallama yayi mata ya fice ita kuma nan ta d'auka waya tana kira ABBA ta shaida masa,a lokacin ko suna tare a office d'in ABBA SAFWAN suna tattaunawa akan wasu kaya da zasu fitar sak'on ya iske su,cike da farin ciki ta sanar masa,aiko shi kansa tasa murnar kasa b'oyuwa tayi dan yadda sak'on yazo masa a lokacin sai yaji kamar lokacin IYA ke sanar masa da k'aruwar KHUBRA da ya samu,wasu hawayen farin ciki ya goge inda yake tambayarta me aka samu.Shiru tayi tana fad'in
"Tabbb! kaga kuwa abunda ban tambayaba kenan,kuma har ya tafi dan sauri yake lokacin daya zo,ya sanarmin ita kad'ai ce sai likitocin daya bari suna gyara su..."
Murmushi yayi na farin ciki sosai ya furta
"To babu damuwa in sha Allah yanzun driver zaizo gida sai kije gurinta kafin mu k'araso.."
Daga haka suka yi sallama ya kashe,yana kuma shaidawa su ABBA dake jiran ya gama,sun ga yana goge hawaye d'azun,ko da ya basu labarin abunda ya faru,su kansu murnansu da farin cikinsu kasa b'oyuwa yayi,tattara duk abunda suke sukayi da niyyan tafiya asibiti ganin jikokin nasu da basu san me aka haifa ba har lokacin..
Cikin d'an lokaci kad'an har labari ya gama zagaye dangin na haihuwar KHUBRA a yinin ranar ta jumu'ah.
Kafin wani lokaci mai tsawo har d'akin asibitin ya gama cika da iyaye da y'ay'a na gidan,kowa ka kalla kasan yana cike da farin cikin k'aruwar da aka samu na yara har uku sukutum a ranar.Maijego kuwa duk wannan budurin da ake bata sani ba tana ta faman baccin wahala dan kam ta galabaita ba kad'an ba,yara da suka zo da farin jini kowa burinsa ya d'auke su.
Daga KHUBRA har yaranta sun sha addu'ah a bakin y'an uwa da abokan arziki,haka mai jego taci gaba da samun kulawa a nan asibitin saboda k'in sallamarta suka yi duba da irin wahalar data sha kafin haihuwar,kwananta biyu aka sallameta inda UMMI ta tafi da ita dan bata kulawa ita da jariranta uku,biyu maza d'aya mace kuma ita ce k'arama cikinsu.
Gidan UMMI ya koma gurin zuwan BB kullum yana can mak'ale da yaransa da kuma y'ar matarsa,wani lokaci har sai UMMI ta gaji da shi ta kora shi dan kam ba wata kunyar UMMI yake jiba kuma dalilin daya sa aka maido da KHUBRA gidan sun san idan a gidan MAMA take zai iya komawa gidan ya tare.Sai dai kuma nan enma bata canza zaniba,kullum nan yake yini,da k'yar UMMI take korashi idan ko ya fice tofa bashi da gurin zuwa sai dai ya wuce gurin aikin nasu data tashi kuma nan zai dawo ya sake rashewa,a haka har aka shafe tsawon kwanaki shida,wanda zuwa ranar yara sun riga da sun amsa sunansu,HASSAN ya amsa sunan ABDULLAH suna kiransa da ABDUL,sa HUSSAIN da aka rad'awa ABUBAKAR shi kuma suna kiransa da SADDIQ ensa,ita kuma macen da take k'arama ta amsa sunan KHADIJATUL-KHUBRA wato sunan mahaifiyarta,kowa tambayar BB dalilin yin hakan yake,shi ko gogan cewa kawai yake haka yaga dama coz shi ba shi da niyyan sa sunan iyayensu,salon haka kawai wata rana a gaban idonsa a kira masa sunan iyayensa a zaga,KHUBRA kuma da aka tambayi dalilin da yasa ya sanya sunanta murmushi yayi sannan ya basu amsa da cewar
"Itace wacce nafi k'auna...Shi yasa na maida sunanta akan y'armu ta fari,kuma ko bayan haka sunan matar Manzon Allah ce ta fari (S.A.W)..."
Haka aka ci gaba da shirin hidimomin da aza gudanar a gobe na suna idan Allah ya nufa....
*RANAR SUNA...*
Tun da asuba bayan an idar da sallah aka sake jadadda sunayen yara kamar yadda suke,ABDULLAH,ABUBAKAR AS-SADDIQ sai kuma NANA KHADIJATU.
FATAHIYYA zaune ta tasa yaran a gaba dan tun da aka dawo da KHUBRA gidan UMMI itama ta dawo nan ta tare cikin shekaru biyu duk wanda ya kalleta sai yayi mamakin girman data k'ara ga class na musamman ba kamar daba da ba wani wayewa gareta ba.
Anyi taro lafiya wanda ya amsa sunan taro ba wai taron da yake na muna taroba,inda a ranar BB sai daya bawa mutane mamaki kan irin bajinta da yayi na kyaututtuka daya dinga bajewa ga abar k'aunarsa,duk kuma kan irin farin cikin data sashi a zamansu,haka taron suna ya watse da kyaututtukan da aula samu daga gurin y'an uwa da abokan arziki,haka taro ya watse inda aka bar mai jego da yaran hannun UMMI suna sake karb'ar gyara da kulawa....
Agogo juyi yake inda a kowane motsawar second sai kaga ci gaba ta wani bigire na daban a rayuwa,cikin kwanaki arba'in da haihuwar KHUBRA yara sun dad'a wayo musamman mazan da dama tun a haihuwarsu sunfi LITTLE KHUBRA girma.
Tun da safe a ranar kwana na arba'in en ne,BB ya kafa ya tsare a gidan UMMI jira kawai yake UMMI ta bashi approval na tafiya da iyalinsa,tun data ganshi tasan abunda yake nufi,nan ko ta had'e girar sama dana k'asa ta kuma k'i ce masa komai,tun safe har dare yana nan,ganin babu magana makamanciyar ya d'aukesu su tafi yasa ya bawa kansa hak'uri,kallon agogo yayi yaga yadda dare yayi cikin sanyi murya yace
"UMMI zan tafi..."
Bud'ar bakin UMMI tace masa
"To ka gaida gida ko..."
Shiru yayi kansa a k'asa ya rasa me zai ce mata,ita kuma tana kallonsa duk abunda yake sai dai bata k'ara maganaba daga haka,kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa,cikin sanyin jiki ya mik'e ya mata sallama fuskarsa cike da damuwa ya tasamma hanyar fita daga parlour'n,har ya isa bakin k'ofa sai kuma ya bata tausayi tasan dai ita da kanta yayi hak'uri tunda bai tab'a tambayarta akan zai tafi da ita ko makamancin hakaba,dakatar dashi tayi tana kiransa,dawowa yayi kansa a k'asa dan ji yake kamar yayita kurma mata ihu ko Allah zaisa ta bashi matarsa,hak'uri kam yayi shi har yana neman ya gagare shi.
"Zauna nan...Ina zuwa.."
"JAAN MAMA fa da UMMA...?"
Ido ya fiddo waje dan sam yama manta da batun ya sanar musu,kansa ya dafe yana birkita gashinsa,alamun data gani kenan a tare da shi ta gane babu wanda ya sanarma.
"JODI...Basu saniba,ni kuma na manta ma da ya kamata ace na sanar musu.."
'Dan murmushin k'arfin hali ta masa ta sake lumshe idanunta,aljihunsa ya laluba da niyyan d'aukan waya ya kira su,sai dai wayam babu wayan,sai a lokacin ya tuna da bai d'aukoba,lower lip nasa ya cije tunawa da kayan dake shirye cikin d'an akwatin kawai ya d'auko shima kuma suna motan bayan su kuma bai d'auko wani abuba.
"Ya Allah...! Komai ma na manta daya kamata nayi..JODI wait a minute....I will be back right now.."
Yana fad'in haka ya mik'e had'e da bata fake a cheeks enta na dama,cikin sauri ya fice ya nufi mota,kayan ya d'auko ya dawo had'e da bawa nurse's en ya shaida musu zai dawo nan bada jimawa ba in sha Allah,daga haka ya fice cike da sauri yayi starting motan,direct daga nan gidan UMMA ya fara zuwa wato HAJIYA ZUWAIRA,tana ganin yana yinsa ta fahimci da akawai abunda yake faruwa,ganinsa sai murmushi yake zubawa yasa ta itama tayi murmushin tana fad'in
"Kada dai ka ce KHUBRA ta haihu...?"
Aiko dariya ya sake yana fad'in
"Haka ne UMMA'NMU...Yanzun ma na barota hospital,so saboda ba waya a jikina yasa ban samu na kira kowaba,yanzunma gida zanje na koma.."
Da murna sosai take godiya ga Allah bisa ni'imar da yayi musu,sallama yayi mata ya fice ita kuma nan ta d'auka waya tana kira ABBA ta shaida masa,a lokacin ko suna tare a office d'in ABBA SAFWAN suna tattaunawa akan wasu kaya da zasu fitar sak'on ya iske su,cike da farin ciki ta sanar masa,aiko shi kansa tasa murnar kasa b'oyuwa tayi dan yadda sak'on yazo masa a lokacin sai yaji kamar lokacin IYA ke sanar masa da k'aruwar KHUBRA da ya samu,wasu hawayen farin ciki ya goge inda yake tambayarta me aka samu.Shiru tayi tana fad'in
"Tabbb! kaga kuwa abunda ban tambayaba kenan,kuma har ya tafi dan sauri yake lokacin daya zo,ya sanarmin ita kad'ai ce sai likitocin daya bari suna gyara su..."
Murmushi yayi na farin ciki sosai ya furta
"To babu damuwa in sha Allah yanzun driver zaizo gida sai kije gurinta kafin mu k'araso.."
Daga haka suka yi sallama ya kashe,yana kuma shaidawa su ABBA dake jiran ya gama,sun ga yana goge hawaye d'azun,ko da ya basu labarin abunda ya faru,su kansu murnansu da farin cikinsu kasa b'oyuwa yayi,tattara duk abunda suke sukayi da niyyan tafiya asibiti ganin jikokin nasu da basu san me aka haifa ba har lokacin..
Cikin d'an lokaci kad'an har labari ya gama zagaye dangin na haihuwar KHUBRA a yinin ranar ta jumu'ah.
Kafin wani lokaci mai tsawo har d'akin asibitin ya gama cika da iyaye da y'ay'a na gidan,kowa ka kalla kasan yana cike da farin cikin k'aruwar da aka samu na yara har uku sukutum a ranar.Maijego kuwa duk wannan budurin da ake bata sani ba tana ta faman baccin wahala dan kam ta galabaita ba kad'an ba,yara da suka zo da farin jini kowa burinsa ya d'auke su.
Daga KHUBRA har yaranta sun sha addu'ah a bakin y'an uwa da abokan arziki,haka mai jego taci gaba da samun kulawa a nan asibitin saboda k'in sallamarta suka yi duba da irin wahalar data sha kafin haihuwar,kwananta biyu aka sallameta inda UMMI ta tafi da ita dan bata kulawa ita da jariranta uku,biyu maza d'aya mace kuma ita ce k'arama cikinsu.
Gidan UMMI ya koma gurin zuwan BB kullum yana can mak'ale da yaransa da kuma y'ar matarsa,wani lokaci har sai UMMI ta gaji da shi ta kora shi dan kam ba wata kunyar UMMI yake jiba kuma dalilin daya sa aka maido da KHUBRA gidan sun san idan a gidan MAMA take zai iya komawa gidan ya tare.Sai dai kuma nan enma bata canza zaniba,kullum nan yake yini,da k'yar UMMI take korashi idan ko ya fice tofa bashi da gurin zuwa sai dai ya wuce gurin aikin nasu data tashi kuma nan zai dawo ya sake rashewa,a haka har aka shafe tsawon kwanaki shida,wanda zuwa ranar yara sun riga da sun amsa sunansu,HASSAN ya amsa sunan ABDULLAH suna kiransa da ABDUL,sa HUSSAIN da aka rad'awa ABUBAKAR shi kuma suna kiransa da SADDIQ ensa,ita kuma macen da take k'arama ta amsa sunan KHADIJATUL-KHUBRA wato sunan mahaifiyarta,kowa tambayar BB dalilin yin hakan yake,shi ko gogan cewa kawai yake haka yaga dama coz shi ba shi da niyyan sa sunan iyayensu,salon haka kawai wata rana a gaban idonsa a kira masa sunan iyayensa a zaga,KHUBRA kuma da aka tambayi dalilin da yasa ya sanya sunanta murmushi yayi sannan ya basu amsa da cewar
"Itace wacce nafi k'auna...Shi yasa na maida sunanta akan y'armu ta fari,kuma ko bayan haka sunan matar Manzon Allah ce ta fari (S.A.W)..."
Haka aka ci gaba da shirin hidimomin da aza gudanar a gobe na suna idan Allah ya nufa....
*RANAR SUNA...*
Tun da asuba bayan an idar da sallah aka sake jadadda sunayen yara kamar yadda suke,ABDULLAH,ABUBAKAR AS-SADDIQ sai kuma NANA KHADIJATU.
FATAHIYYA zaune ta tasa yaran a gaba dan tun da aka dawo da KHUBRA gidan UMMI itama ta dawo nan ta tare cikin shekaru biyu duk wanda ya kalleta sai yayi mamakin girman data k'ara ga class na musamman ba kamar daba da ba wani wayewa gareta ba.
Anyi taro lafiya wanda ya amsa sunan taro ba wai taron da yake na muna taroba,inda a ranar BB sai daya bawa mutane mamaki kan irin bajinta da yayi na kyaututtuka daya dinga bajewa ga abar k'aunarsa,duk kuma kan irin farin cikin data sashi a zamansu,haka taron suna ya watse da kyaututtukan da aula samu daga gurin y'an uwa da abokan arziki,haka taro ya watse inda aka bar mai jego da yaran hannun UMMI suna sake karb'ar gyara da kulawa....
Agogo juyi yake inda a kowane motsawar second sai kaga ci gaba ta wani bigire na daban a rayuwa,cikin kwanaki arba'in da haihuwar KHUBRA yara sun dad'a wayo musamman mazan da dama tun a haihuwarsu sunfi LITTLE KHUBRA girma.
Tun da safe a ranar kwana na arba'in en ne,BB ya kafa ya tsare a gidan UMMI jira kawai yake UMMI ta bashi approval na tafiya da iyalinsa,tun data ganshi tasan abunda yake nufi,nan ko ta had'e girar sama dana k'asa ta kuma k'i ce masa komai,tun safe har dare yana nan,ganin babu magana makamanciyar ya d'aukesu su tafi yasa ya bawa kansa hak'uri,kallon agogo yayi yaga yadda dare yayi cikin sanyi murya yace
"UMMI zan tafi..."
Bud'ar bakin UMMI tace masa
"To ka gaida gida ko..."
Shiru yayi kansa a k'asa ya rasa me zai ce mata,ita kuma tana kallonsa duk abunda yake sai dai bata k'ara maganaba daga haka,kamar zaiyi magana kuma sai ya fasa,cikin sanyin jiki ya mik'e ya mata sallama fuskarsa cike da damuwa ya tasamma hanyar fita daga parlour'n,har ya isa bakin k'ofa sai kuma ya bata tausayi tasan dai ita da kanta yayi hak'uri tunda bai tab'a tambayarta akan zai tafi da ita ko makamancin hakaba,dakatar dashi tayi tana kiransa,dawowa yayi kansa a k'asa dan ji yake kamar yayita kurma mata ihu ko Allah zaisa ta bashi matarsa,hak'uri kam yayi shi har yana neman ya gagare shi.
"Zauna nan...Ina zuwa.."