Sashe 41
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tsuke fuska ASHNA tayi tana kallonsa da mugun haushi d'auke cikin idanunta kan yadda taga duk ya wani kafeta da ido.
"MALAM lafiya kake min irin wannan kallon?
Nifa kaga banson irin wannan kallon k'urillan haka kawai duk ka gano munin mutum,to gaskiya ya isheka haka"
Cike da tsiwa take maganar tana zabga masa wata uwar harara,dariya yayi mata wanda yasa farare tas en hak'oransa suka bayyana,dariyan da yayi shi ya bawa beauty point dake gefen kumatunsa lotsawa,take kuwa ASHNA ta saki baki tana kallon ikon Allah
"Ammafa GUY en ba laifi,duk da kasancewarsa bak'i,da wad'annan jajayen idanun nasa amma ai yana da hanci ga beauty point,wow inama ba cikin mugayen nan yake ba,kuma kyau ace yayi boko,omg ya zai kasance?"
Kanta ta d'an d'age tana son tuna ya wannan GUY en zai kasance,sai dai tayi murmushi had'e da fad'in
"Kaiiiii ammafa wollahi da ba k'aramin HANDSOME za ayiba"
Gintse fuska ta dad'a yi ganin yadda yake sake kallonta
"MALAM nafa ce maka ka denamin irin wannan kallon ko? har da wani yimin murmushi,ka rik'e abunka bance maka ina soba ai
Yanzu kawai ka fad'amin zaka mai dani gidanmu?"
"A'a BEAUTY bazan iya mai daki ba yanzu"
"Da Allah ni ka dena wani cemin BEAUTY tunda ba maidani za kayiba,kawai ka tashi ka bani guri"
Ko rufe bakinta bata yiba taga ya mik'e yana shirin barin d'akin,baki ta dad'a b'arewa tasa masa kuka.
Daf da bakin k'ofan ya tsaya had'e da rufe idanunsa lokacin da take kukan,da sauri kuma ya fice daga d'akin tare da rufe d'akin...
Fitowansa daga d'akin ya tsaya nan cikin corridor en,number HAJIYA LAURA ya shiga kira,bayan ta d'auka ya shiga labarta mata abunda suka yi ASHNA yanzun.
Ko gama rufe bakinsa baiba HAJIYA LAURA cikin tsawa ta dakatar da shi
"Nooo!BIGGY kadama ka kuskura ka tafka wannan d'anyen aikin,taya zaka biyewa wannan y'ar mitsitsiyar yarinyar
Baka gudun abunda zai je ya dawo ne hala idan ka maidata gida?
Ko kuwa baka tunanin gane fuskarka da tayi zai jawo mu fad'a hannun hukuma to gaskiya tun wurima ka kama kanka da wannan maganar
Sam hakan ba mai yiwuwa bane ina fatan ka gane"
Jiki a sanyaye yayi mata sallama ya kashe,nanfa BIGGY ya jingina jikin ginin gurin ya rufe idanunsa yana tuna irin yadda yarinyar ke nuna damuwarta da son ta koma gida ko don sanin halin da mahaifiyarta ke ciki.
Tambayoyi ya shiga yima kansa
"Shin mema yasa muke irin wannan aikin ga wasu mutanen da babu tausayi a zuk'atansu?ko don na rasa iyayena ne tun ina yaro shi yasa na biyewa irin wad'an nan mutanen suna sani aiki irin wannan,shin bana gudun ranar da Allah zai tashi kamani? Dame zanje masa wanda zan kare kaina a gurinsa?
Gaskiya ya kamata na nutsu.....Ina buk'atar shawara daga gurin wani......Ina buk'atar canja halayena.....To amma wa zan tunkara da wannan maganar?
Shi kad'ai yana ta magana da zuciyarsa,rashin samun maka yasa shi saita kansa sannan ya bar gurin jikinsa duk yayi sanyi saboda tunanin da yayi.
《《》》
Shigowar dattijon gidan kenan da sallama sai dai babu kowa tsakar gidan,hakan ne yasa shi tunkaran d'akinsa ya sanya d'an k'aramin key en ya murza tare da bud'e k'ofar yana mai kunna kai cikin d'aki.
Kan y'ar lank'wamammiyar katifan ya kwanta duk abun duniya ya dame shi,zuciyarsa duk babu dad'i haka yake jinta,haka dai ya juya ya kwanta cike da damuwa da ya rasa ta mene ne.
Lek'e ta shiga yi ta saman dangar karan dake kewaye da gidan duk burinta bai wuce ta hango cikin gidanba,k'ofar d'akin MALAM en ta hango a bud'e da alama ya dawo kenan.
A hankali cikin sand'a ta shigo gidan,wuf tayi ta shige d'akinta da ganin yadda take tafiya kasan babu gaskiya wai akace "awo a d'aka".
Wuf tayi ta afka cikin d'aki tana dafe k'irjinta had'e da fad'in
"Waii Allah ya taimakeni MALAM bai kamani ina wannan sand'arba da yau kam ina da tabbacin komai zai iya faruwa"
Wata irin dariya ta tsinkayo a bayanta data sata saurin juyowa tana bin inda taji dariyan da kallo
Zaune saman gadonta na k'arfe ta hangoshi ya hard'e k'afafu kamar a fada
Tsoro ne ya cika mata zuciya,duk da tasan waye hakan bai rage mata tsoron da take cikiba.
Da k'yar take had'iyan yahu dan ta san ko me ya kawoshi a wannan lokacin,haka LADIYO ta shiga jan jiki har ta k'arasa gurinsa dan ta san bata isa ta bijireba,ko dan tsoron da take ciki,hakan ba maganin komai zai mataba.
A dai² lokacin da LADIYO suke tsaka da shek'e ayarsu da HATSABIBIN BOKA'N nasu ne shi kuma ABBA'N KHUBRA yake bacci mai cike da mafarkai da ya saba yinsu ko wane dare.
Cikin duhun dare cikin wani irin k'ungurmin daji da babu komai cikinsa face koke-koken tsun-tsaye da wasu halittun marasa dad'in ji.
Kamar daga sama ya tsinkayo muryar yarinyar tana kuka
"ABBA ka taimakeni....Wayyoo Allah ABBA zasu kashe ni....ABBA kada ka bari su cutar dani dan Allah"
Abunda ya iya jiyowa kenan shima cikin wani irin sauti da yake nuna ta gama galabaita ne take masa magana.
Yunk'uri yayi domin ya taimaka mata sai dai me ya kasa ko da taku d'aya saboda yadda yake d'aure jikin wani k'aton dutse,hannu da k'afafunsa duk suna sanye cikin ank'wa,wacce baya tunanin zai iya tsira daga gareta.
Hankalinsa a tashe saboda ganin yarinyar da yayi wasu irin mutane da baya iya hango fuskokinsu bare yasan su waye,sun rik'eta suna tunkarar wani k'aton rami da wuta ke ci a ciki da nufin jefata,ita kuma sai turjewa take tana waigowa tana kiransa kan neman taimako daga gare shi.
'Dagata sukayi da niyyan jefata,kafin su ida nufinsu suka fara jiyo gudu had'e da haniniyar dawaki,samari ne su biyu sun ratso ta cikin jejin haye bisa dawakai fuskokinsu rufe da k'yalle,iya k'arfinsu suka bud'e baki suna furta
"Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn"
Fad'ar wannan kalmar babu b'ata lokaci yarinyar da ake k'ok'arin jefawa wuta,ta shiga maimaitawa cikin k'arfin hali da bud'e murya iyakar iyawarta.
Wutar dake ci cikin ramin tayi wani irin tasowa kamar an hurota,harshen wutan da yayiwo wajensu take ya laso su wutan ta kama jikinsu suka kama da wuta,sakinta suka yi a k'asa,sai dai abun mamaki wutan ko kad'an ita bai sametaba.
Cikin sauri d'aya daga cikin mahayan ya sauko tare da d'aukanta ya aza saman dokinsa ya haye shima.
Da gudu suka bar jejin inda take a nan shi kuma ya dena ganinsu sun b'ace b'at kamar iska.
B'acewan nasu ya dad'a jefa zuciyarsa cikin tsananin tsoro da fargaba,kamar daga sama yaji yo muryan yarinyar lokacin da take maimaita abunda taji wad'annan mahayan sun ambata.
Yunk'urin fad'a ya shiga yi shima,inda yana maimaitawa yaji ank'wan dake d'aure jikinsa ta zube k'asa,juyawa yayi ya kalli jejin gaba da baya sannan ya shiga shek'a gudu iya k'arfinsa ta hanyar da yaga sunbi,yana cikin gudun ya fara hangosu can nesa da shi,sosai yake gudun kamar wanda ya hau takalmin taya sai da ya kusa cimma mahayan duk da kasancewar suna kan abin hawa shi kuma yana k'asa,har ya fara murna kawai sai ji yayi ya daki wani irin dutse a gabansa da ya sashi fad'uwa a gurin,kansa ne ya daku da dutsen take idanunsa suka soma k'ank'ancewa saboda azaba...
A firgice ya farka jikinsa duk ya had'a zufa duk kuwa da yanda garin yake cike da iska saboda hadirin daya had'u a d'azun sai dai iska kawai ya bayar mai sanyin dad'i,amma shi gare shi duk ya jik'e da gumi.
Tunanin mafarkin da yayi ya tsaya yi,yana mamaki had'e da al'ajabin mene ne had'inshi da mafarkin?
K'wak'walwarsa ta dawo masa da maganganun yarinyar da yayi mafarki da ita,take ya tsinci kansa da fad'in
"Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn"
Maimaitawa yayi tayi cikin zuciyarsa,wanda k'arshe har kalmomin suka bayyana a fili.
Jiki a sanyaye ya mik'e daga gurin yayi hanyan fita daga d'akin zuciyarsa wasai babu zafi da kuma rad'ad'in da yake ji a baya.
Har ya d'auki buta zai shiga bayan gida ya dawo tare da ajiyewa a gefen randa,k'ofar d'akin LADIYO ya tunkara,kasancewar yasan su kad'ai ne a gidan ba tare da ya k'wank'wasaba ya kunna kai ciki da y'ar torchlight ensa da yake haska hanya da ita.
Mugun gamon da yayi yasa shi dafa bango saboda wani jiri da yake neman d'ibansa,cikin sauri kuma ya juya ya fice daga d'akin zuciyarsa na k'una.......
Tashin hankali kenan wanda ba a sa masa rana...
《《》》
Misalin k'arfe 1:40pm motan ta kunno kai cikin haraban gidan,har lokacin KHUBRA na lafe jikin BABA ZUWAIRA,baiwar Allah tana zaune sai kalle-kallen cikin gari take,har suka k'araso cikin gidin wanda had'uwa da tsarin gidan yasa take bin ko'ina da mamakin yadda akayi KHUBRA ta iya rayuwa a wannan k'ungurmin k'auyen nasu kuma har ta iya jurar wannan wahalar.
KHALEEL dake driven yayi parking sannan ya fita,inda BB shima ya mara masa baya yana fitowa ya ja k'ofan baya inda su KHUBRA suke,cikin taushin murya ya furta
"Bismillah"
Had'e kuma da nuna musu hanya suka fito KHUBRA rik'e da hannun BABA ZUWAIRA suka bi bayansa,KHALEEL a gaba BB biye da shi sai kuma su KHUBRA dake bi masa.
Ummi tsaye cikin kitchen tana gyara zaman warmer's en akan tire da take son fita dashi,gefe kuma basket ne shima da wasu had'ad'd'un Flak's,tana shirin fitowa sallaman su ta kawo kunnenta.
Da sauri ta fita tana fad'in
"Lale marhaban da Y'AY'ANA,gaskiyafa kunsha hanya"
Turus ta tsaya tana kallonsu ganin ba su kad'ai suke tafeba..
"A'aa da bak'i kuke tafe ashe,amma ya akayi baka sanar da niba da kayimin waya?"
Ta kalli KHALEEL cike da tuhuma,kunnensa ya d'an rik'e alaman ban hak'uri,murmushi tayi tare da fad'in
"Ai kaikam ka iya bada hak'uri idan kayiwa mutum laifi"
Kallon BB tayi da ya riga ya zauna tana k'arasawa dinning lokacin da ta ajiye tiren hannunta, sannan ta dawo cikin parlor
"Sannu SON kun sha hanya"
"Wallahi kuwa UMMI mun sha hanya,amma ai duk ga wanda ya jaa muka kawo yanzu bamu isoba,ya wani tsaya drive'n kamar d'an koyo"
"Oooo!nikam naga ranar da zaka fara drive'n a hankali,wato kaii dai kawai kafi son ayita shek'a gudu ko?"
"Yawwa UMMI ai haka shi ne magana"
"Uhmm Allah ya kyauta muku"
"Ameen UMMI'NMU"
Ya fad'a yana sakin murmushinsa mai kyau..
"MALAM lafiya kake min irin wannan kallon?
Nifa kaga banson irin wannan kallon k'urillan haka kawai duk ka gano munin mutum,to gaskiya ya isheka haka"
Cike da tsiwa take maganar tana zabga masa wata uwar harara,dariya yayi mata wanda yasa farare tas en hak'oransa suka bayyana,dariyan da yayi shi ya bawa beauty point dake gefen kumatunsa lotsawa,take kuwa ASHNA ta saki baki tana kallon ikon Allah
"Ammafa GUY en ba laifi,duk da kasancewarsa bak'i,da wad'annan jajayen idanun nasa amma ai yana da hanci ga beauty point,wow inama ba cikin mugayen nan yake ba,kuma kyau ace yayi boko,omg ya zai kasance?"
Kanta ta d'an d'age tana son tuna ya wannan GUY en zai kasance,sai dai tayi murmushi had'e da fad'in
"Kaiiiii ammafa wollahi da ba k'aramin HANDSOME za ayiba"
Gintse fuska ta dad'a yi ganin yadda yake sake kallonta
"MALAM nafa ce maka ka denamin irin wannan kallon ko? har da wani yimin murmushi,ka rik'e abunka bance maka ina soba ai
Yanzu kawai ka fad'amin zaka mai dani gidanmu?"
"A'a BEAUTY bazan iya mai daki ba yanzu"
"Da Allah ni ka dena wani cemin BEAUTY tunda ba maidani za kayiba,kawai ka tashi ka bani guri"
Ko rufe bakinta bata yiba taga ya mik'e yana shirin barin d'akin,baki ta dad'a b'arewa tasa masa kuka.
Daf da bakin k'ofan ya tsaya had'e da rufe idanunsa lokacin da take kukan,da sauri kuma ya fice daga d'akin tare da rufe d'akin...
Fitowansa daga d'akin ya tsaya nan cikin corridor en,number HAJIYA LAURA ya shiga kira,bayan ta d'auka ya shiga labarta mata abunda suka yi ASHNA yanzun.
Ko gama rufe bakinsa baiba HAJIYA LAURA cikin tsawa ta dakatar da shi
"Nooo!BIGGY kadama ka kuskura ka tafka wannan d'anyen aikin,taya zaka biyewa wannan y'ar mitsitsiyar yarinyar
Baka gudun abunda zai je ya dawo ne hala idan ka maidata gida?
Ko kuwa baka tunanin gane fuskarka da tayi zai jawo mu fad'a hannun hukuma to gaskiya tun wurima ka kama kanka da wannan maganar
Sam hakan ba mai yiwuwa bane ina fatan ka gane"
Jiki a sanyaye yayi mata sallama ya kashe,nanfa BIGGY ya jingina jikin ginin gurin ya rufe idanunsa yana tuna irin yadda yarinyar ke nuna damuwarta da son ta koma gida ko don sanin halin da mahaifiyarta ke ciki.
Tambayoyi ya shiga yima kansa
"Shin mema yasa muke irin wannan aikin ga wasu mutanen da babu tausayi a zuk'atansu?ko don na rasa iyayena ne tun ina yaro shi yasa na biyewa irin wad'an nan mutanen suna sani aiki irin wannan,shin bana gudun ranar da Allah zai tashi kamani? Dame zanje masa wanda zan kare kaina a gurinsa?
Gaskiya ya kamata na nutsu.....Ina buk'atar shawara daga gurin wani......Ina buk'atar canja halayena.....To amma wa zan tunkara da wannan maganar?
Shi kad'ai yana ta magana da zuciyarsa,rashin samun maka yasa shi saita kansa sannan ya bar gurin jikinsa duk yayi sanyi saboda tunanin da yayi.
《《》》
Shigowar dattijon gidan kenan da sallama sai dai babu kowa tsakar gidan,hakan ne yasa shi tunkaran d'akinsa ya sanya d'an k'aramin key en ya murza tare da bud'e k'ofar yana mai kunna kai cikin d'aki.
Kan y'ar lank'wamammiyar katifan ya kwanta duk abun duniya ya dame shi,zuciyarsa duk babu dad'i haka yake jinta,haka dai ya juya ya kwanta cike da damuwa da ya rasa ta mene ne.
Lek'e ta shiga yi ta saman dangar karan dake kewaye da gidan duk burinta bai wuce ta hango cikin gidanba,k'ofar d'akin MALAM en ta hango a bud'e da alama ya dawo kenan.
A hankali cikin sand'a ta shigo gidan,wuf tayi ta shige d'akinta da ganin yadda take tafiya kasan babu gaskiya wai akace "awo a d'aka".
Wuf tayi ta afka cikin d'aki tana dafe k'irjinta had'e da fad'in
"Waii Allah ya taimakeni MALAM bai kamani ina wannan sand'arba da yau kam ina da tabbacin komai zai iya faruwa"
Wata irin dariya ta tsinkayo a bayanta data sata saurin juyowa tana bin inda taji dariyan da kallo
Zaune saman gadonta na k'arfe ta hangoshi ya hard'e k'afafu kamar a fada
Tsoro ne ya cika mata zuciya,duk da tasan waye hakan bai rage mata tsoron da take cikiba.
Da k'yar take had'iyan yahu dan ta san ko me ya kawoshi a wannan lokacin,haka LADIYO ta shiga jan jiki har ta k'arasa gurinsa dan ta san bata isa ta bijireba,ko dan tsoron da take ciki,hakan ba maganin komai zai mataba.
A dai² lokacin da LADIYO suke tsaka da shek'e ayarsu da HATSABIBIN BOKA'N nasu ne shi kuma ABBA'N KHUBRA yake bacci mai cike da mafarkai da ya saba yinsu ko wane dare.
Cikin duhun dare cikin wani irin k'ungurmin daji da babu komai cikinsa face koke-koken tsun-tsaye da wasu halittun marasa dad'in ji.
Kamar daga sama ya tsinkayo muryar yarinyar tana kuka
"ABBA ka taimakeni....Wayyoo Allah ABBA zasu kashe ni....ABBA kada ka bari su cutar dani dan Allah"
Abunda ya iya jiyowa kenan shima cikin wani irin sauti da yake nuna ta gama galabaita ne take masa magana.
Yunk'uri yayi domin ya taimaka mata sai dai me ya kasa ko da taku d'aya saboda yadda yake d'aure jikin wani k'aton dutse,hannu da k'afafunsa duk suna sanye cikin ank'wa,wacce baya tunanin zai iya tsira daga gareta.
Hankalinsa a tashe saboda ganin yarinyar da yayi wasu irin mutane da baya iya hango fuskokinsu bare yasan su waye,sun rik'eta suna tunkarar wani k'aton rami da wuta ke ci a ciki da nufin jefata,ita kuma sai turjewa take tana waigowa tana kiransa kan neman taimako daga gare shi.
'Dagata sukayi da niyyan jefata,kafin su ida nufinsu suka fara jiyo gudu had'e da haniniyar dawaki,samari ne su biyu sun ratso ta cikin jejin haye bisa dawakai fuskokinsu rufe da k'yalle,iya k'arfinsu suka bud'e baki suna furta
"Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn"
Fad'ar wannan kalmar babu b'ata lokaci yarinyar da ake k'ok'arin jefawa wuta,ta shiga maimaitawa cikin k'arfin hali da bud'e murya iyakar iyawarta.
Wutar dake ci cikin ramin tayi wani irin tasowa kamar an hurota,harshen wutan da yayiwo wajensu take ya laso su wutan ta kama jikinsu suka kama da wuta,sakinta suka yi a k'asa,sai dai abun mamaki wutan ko kad'an ita bai sametaba.
Cikin sauri d'aya daga cikin mahayan ya sauko tare da d'aukanta ya aza saman dokinsa ya haye shima.
Da gudu suka bar jejin inda take a nan shi kuma ya dena ganinsu sun b'ace b'at kamar iska.
B'acewan nasu ya dad'a jefa zuciyarsa cikin tsananin tsoro da fargaba,kamar daga sama yaji yo muryan yarinyar lokacin da take maimaita abunda taji wad'annan mahayan sun ambata.
Yunk'urin fad'a ya shiga yi shima,inda yana maimaitawa yaji ank'wan dake d'aure jikinsa ta zube k'asa,juyawa yayi ya kalli jejin gaba da baya sannan ya shiga shek'a gudu iya k'arfinsa ta hanyar da yaga sunbi,yana cikin gudun ya fara hangosu can nesa da shi,sosai yake gudun kamar wanda ya hau takalmin taya sai da ya kusa cimma mahayan duk da kasancewar suna kan abin hawa shi kuma yana k'asa,har ya fara murna kawai sai ji yayi ya daki wani irin dutse a gabansa da ya sashi fad'uwa a gurin,kansa ne ya daku da dutsen take idanunsa suka soma k'ank'ancewa saboda azaba...
A firgice ya farka jikinsa duk ya had'a zufa duk kuwa da yanda garin yake cike da iska saboda hadirin daya had'u a d'azun sai dai iska kawai ya bayar mai sanyin dad'i,amma shi gare shi duk ya jik'e da gumi.
Tunanin mafarkin da yayi ya tsaya yi,yana mamaki had'e da al'ajabin mene ne had'inshi da mafarkin?
K'wak'walwarsa ta dawo masa da maganganun yarinyar da yayi mafarki da ita,take ya tsinci kansa da fad'in
"Laa-ilaha'illa anta subhanaka inniiy kuntu minaz-zalimiiyn"
Maimaitawa yayi tayi cikin zuciyarsa,wanda k'arshe har kalmomin suka bayyana a fili.
Jiki a sanyaye ya mik'e daga gurin yayi hanyan fita daga d'akin zuciyarsa wasai babu zafi da kuma rad'ad'in da yake ji a baya.
Har ya d'auki buta zai shiga bayan gida ya dawo tare da ajiyewa a gefen randa,k'ofar d'akin LADIYO ya tunkara,kasancewar yasan su kad'ai ne a gidan ba tare da ya k'wank'wasaba ya kunna kai ciki da y'ar torchlight ensa da yake haska hanya da ita.
Mugun gamon da yayi yasa shi dafa bango saboda wani jiri da yake neman d'ibansa,cikin sauri kuma ya juya ya fice daga d'akin zuciyarsa na k'una.......
Tashin hankali kenan wanda ba a sa masa rana...
《《》》
Misalin k'arfe 1:40pm motan ta kunno kai cikin haraban gidan,har lokacin KHUBRA na lafe jikin BABA ZUWAIRA,baiwar Allah tana zaune sai kalle-kallen cikin gari take,har suka k'araso cikin gidin wanda had'uwa da tsarin gidan yasa take bin ko'ina da mamakin yadda akayi KHUBRA ta iya rayuwa a wannan k'ungurmin k'auyen nasu kuma har ta iya jurar wannan wahalar.
KHALEEL dake driven yayi parking sannan ya fita,inda BB shima ya mara masa baya yana fitowa ya ja k'ofan baya inda su KHUBRA suke,cikin taushin murya ya furta
"Bismillah"
Had'e kuma da nuna musu hanya suka fito KHUBRA rik'e da hannun BABA ZUWAIRA suka bi bayansa,KHALEEL a gaba BB biye da shi sai kuma su KHUBRA dake bi masa.
Ummi tsaye cikin kitchen tana gyara zaman warmer's en akan tire da take son fita dashi,gefe kuma basket ne shima da wasu had'ad'd'un Flak's,tana shirin fitowa sallaman su ta kawo kunnenta.
Da sauri ta fita tana fad'in
"Lale marhaban da Y'AY'ANA,gaskiyafa kunsha hanya"
Turus ta tsaya tana kallonsu ganin ba su kad'ai suke tafeba..
"A'aa da bak'i kuke tafe ashe,amma ya akayi baka sanar da niba da kayimin waya?"
Ta kalli KHALEEL cike da tuhuma,kunnensa ya d'an rik'e alaman ban hak'uri,murmushi tayi tare da fad'in
"Ai kaikam ka iya bada hak'uri idan kayiwa mutum laifi"
Kallon BB tayi da ya riga ya zauna tana k'arasawa dinning lokacin da ta ajiye tiren hannunta, sannan ta dawo cikin parlor
"Sannu SON kun sha hanya"
"Wallahi kuwa UMMI mun sha hanya,amma ai duk ga wanda ya jaa muka kawo yanzu bamu isoba,ya wani tsaya drive'n kamar d'an koyo"
"Oooo!nikam naga ranar da zaka fara drive'n a hankali,wato kaii dai kawai kafi son ayita shek'a gudu ko?"
"Yawwa UMMI ai haka shi ne magana"
"Uhmm Allah ya kyauta muku"
"Ameen UMMI'NMU"
Ya fad'a yana sakin murmushinsa mai kyau..