← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 86

Sashe 69

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ohh! kina nufin abunki ba nawa bane ko..?"

"Ehh en inda naka ne ai da bakamin abunda kayiminba da dare..."

Murmushi ya sake yi mai sauti dai-dai fuskarta ya sunkuya yana fad'in
"Ki gama gayamin magana son ranki anjima na kamaki sai nayi miki fiye da haka...Kin san wani abuma kuwa...to bazan barki kiyi bacci ba yau,kwana zamuyi ina sauke miki gajiyan dake jikinki...Kin gane ko..?"

"Tabbb wollahi ba dani kake ba,sai kace wata inji..."
Da sauri ta toshe bakinta,tana dad'a k'udundunewa cikin duvet,sanin babu komai jikinta daga ita sai towel,shima gaba d'aya ya gama nad'ewa zuwa can saman cinyoyinta wanda kad'an ya rage aga komai na daga halittanta.
Bata ankaraba taji ya d'age duvet en,ihu ta saki tana k'ok'arin ja shima yana ja,kukan shagwab'a tasa masa tana fad'in
"Dan Allah YAYA ka bari kagafa babu komai jikina..."

"Ehh dama ai banson ganinki da komai,yanzunma ina son checking enki ne naga babu matsala...."
Dai-dai kunnenta ya rad'a mata cikin murya da yake kashe jikin mai sauraro
"Kinga dole na dubaki saboda anjima da dare bana son wani abu yamin shamaki daga d'and'anon zumanki..."
Hannu tasa ta rufe kunnenta duka shi kuma ya fice yana mata dariya,da kyar ta bud'e idanunta sai lokacinma ta tuna da ZUHRA ta kirata bata d'aukaba ta biye masa,tana dubawa ko taga cikin rashin sani ashe ta d'auka daga can gefen da aka ji batayi maganaba aka kashe,har fiye da mintuna uku,da sauri ta dafe kai a fili take fad'in
"Wayyoo Allah na Allah yasa baki ji komai ba"
Kiranta ta shiga yi cikin shak'iyanci ZUHRA take fad'in
"Amarya bakya laifi....ko da kin kashe d'an masu gida.."

Cike da tsiwa KHUBRA ta tari numfashinta tana fad'in
"Ai wollahi babu abunda zaki fad'amin...Yanzun ace harda had'in bakinki acikin wannan abun dake faruwa,ko ba komai ai na wuce haka a gurinki,amma shi ne kin san wannan maganar kiyi min shiru...babu komai na gode tunda kin san BB'N naki ba sona yake ba Amma kika wani yi shiru aka had'ani da shi,shi kuma YAH KHALEEL dama yaudarana yake ban saniba ashe.."

"A'a CWEETY kada kiyi saurin yanke hukunci kan abunda baki saniba,ki bari kiji komai da yadda al'amura suka wakana,na tabbata ke da kanki zaki fuskanci abubuwan da suka faru a baya..."
A tak'aice ta bawa KHUBRA labarin yadda BB ke sonta tunma kafin a saceta,har zuwa yadda aka shirya komai duk dan asa shi ya fito fili ya nuna da kansa,amma abu yaci tura,wanda daga k'arshe kuma hakan ya kaishi ga fad'awa mummunan yanayi,idonta ta runtse cike da tausayin irin halin da ya shiga akanta,ashe dama akwai lokacin da zata samu wanda zai sota har haka? ita kam ta tabbatar dalilin daya sata sakin jiki da shi a kwanakin nan ba komai bane illah tsoron fad'awa fushin ubangiji da kuma tsinuwar mala'iku,dalili kenan daya sata take k'ok'arin dasama zuciyarta soyayyarsa ko ta wane hali,sai gashi ta tsinci dami a akala,shi tunima ya gama macewa a soyayyarta Wanda bata saniba sai yanzun,lallai ko babu abunda zata yi masa a wannan hali face biyayya sau da k'afa...
Hawayen da suka biyo fuskarta ta shiga gogewa dai-dai ZUHRA na mata tsiyar hiran da suke d'azun da BB,sai gashi ya dawo hannunsa d'auke da d'an k'aramin tray samansa kuma thick tea ne da toasted bread,hangota tana goge fuska hannunta dafe da phone enta dake jikin kunnenta har lokacin ya tabbatar da kuka take,da sauri ya k'araso wayan ya zare daga hannunta yakai kunnensa yana fad'in
"Heyy! MADAM me kika fad'awa matata take kuka cikin wannan safiyar...? idan kinsan kuka zaki dunga samin ita idan kin kirata to a hak'ura da kiran kin gane ko...?"
Yana gama fad'an abunda ke bakinsa ya kashe dai-dai lokacin kuma yana zama kusa da ita,d'agota yayi ya jinginata a jikinsa,dad'a narkewa tayi a jikinsa tana fashewa da sabon kuka,kansa ya dafe yana fad'in
"Ya salaam..!"
patting bayanta ya shiga yi,yana hura mata iska cikin kunnenta,nan da nan tayi shiru jin gaba d'aya vains nata sun soma saki,ta koma sakin ajiyar zuciya
"Watoo abunda ta kira tamin kenan..ta saminke kuka hankalinta ya kwanta,zan gamu da ita tabbas sai na sab'a mata..."
Da sauri ta rufe masa baki da hannunta tana girgiza masa kai cikin sanyi take fad'in
"A'a YAYANAH...ko kad'an kada ka mata haka..ni nasan ba dan haka tayi ba,sai dan wata manufa ta daban...ko kad'an ba abunda kake tunani bane,dalilin kukana ba yana nufin abunda ta kira tayi ba kenan,hasalima ta kirani ne dan ta sanar dani wani muhimmin sak'o da ni kaina ban san dashiba...
Kayi hak'uri YAYANAH sam ban san abunda ya faruba kenan,kuma ko da wasa babu wanda ya sanar dani,ina...ina...so...so..n...ka...nima fiye da yadda kake tunani...tun tasowata na rayune da soyayyarka,da ita na girma..tun ban san kaina ba har nazo na mallaki hankali..sai dai ko kad'an ban tab'a nunawa kowaba,gudun abunda zai faru.."
Shiru tayi tana maida numfashi d'aya da d'aya,matar dake kunyar bud'e ido ta kalleshi sai gata idanunta cikin nasa tana falassa asirin zuciyarta..
Mamakin kalamanta yake sosai saboda baiyi tunanin faruwar hakanba,sai gashi tana sanar masa da soyayyarsa ta rayu..Yana tunanin ta katse shi dai-dai lokacin data ci gaba da fad'in
"A lokacin da nake rayuwa cikin k'unci da tsanani soyayyarka ce kad'ai abunda ke k'aramin k'arfin guiwar ci gaba da rayuwa,badan hakaba da tabbas ban kawo yanzu'n ba,a lokacin da bani da kowa bani da komai sai zallar soyayyarka dake gudu cikin jinina,bana tare da kowa nawa amma idan na tuna da soyayyarka sai naji na zama mai cikakken gata,ina jina a matsayin wacce take da kowa...Dan Allah YAYANAH kaci gaba da sona har k'arshen numfashi,kada ka nunamin halin maza..."
Ta k'arasa tana sake rungumeshi had'e da sakin sabon kuka mai tsuma zuciya,gaba d'aya ilahirin jikinsa ya saki jin irin maganganun dake fitowa daga bakinta kamar a mafarki,komai sai zuwa masa yake da sauk'i ba kamar yadda yayi tunaniba,ajiyan zuciya yayi yana fad'in
"It's ok baby me,bana son kukan nan naki,ina jinsa ne har k'asan zuciyana..."
Da sauri ta shiga gogewa tana girgiza masa kai had'e da murmushi mai burgewa.Murmushin shima ya saki yana janyo tray en dake kan bedside drower,babu musu ya shiga bata tana amsa,sai dai kuma fuskarta da take yamutsawa kamar mai had'iyan magani,duk wani abu da tayi shi kam burgeshi take had'e kuma da k'ara masa kyau.Duk duniya babu abunda yake so sama da ita,tausayi da kuma soyayyanta da suke dad'a taso masa daga can k'asan zuciyarsa su suke dad'a tasiri a lokacin a kansa.
A haka har ya gama bata tea en da toasted bread,murmushi tayi masa tana shafa gefen fuskarsa ta furta
"Na gode YAYANAH..."
Hannunsa yasa saman bakinta ya rufe yana girgiza mata kai,cikin sanyin murya ya furta mata
"Babu godiya acikin abunda ya zama wajibina..."
Har ya mik'e zai fita ya juyo yana fad'in
"Baby get ready idan na dawo zan miki wanka...."
Ta gane dalilin da yasa ya fad'i haka duba da yadda ya mata winking,fuskarta tayi saurin b'oyewa,cikin sauri ya fice da tray en a hannunsa yana dariya,itama dariya tayi tana jin zuciyarta wasai,dawowarsa cikin d'akin tayi saurin b'oyewa cikin duvet har kanta tana tuna abunda zai mata yanzun kuma dan kam ta tabbata sai ya aikata abunda ya fad'a
"Ehheem! MR'S KHALEED SAFWAN kin shirya ko kuwa yanzunma babu k'aton da zai miki wankan...?"

Dariya tayi mai sauti tana fad'in
"Ehhh! babu..."
Kafin ta k'arasa ya sureta yayi hanyan toilet yana fad'in
"Haba yarinya....zancen babu wani k'ato da zai miki wankama ai bai tasoba,tunda anyi abunda yafi wanka ko....?"

B'oye fuskarta tayi cikin jikinsa sukayi dariya dukansu.ko a toilet enma shiriritarsu suka tsaya yi,sai da suka b'ata lokaci a ciki ana gumurzu tsakaninta da BB,shi yana wani aikin daban ita kuma tana masa raki haka suka fito,sai daifa akwai tarin tambayoyi a zuciyar BB da yake son yi mata kan maganarta na d'azun...................

*COMMENT FOR MORE PAGE'S.........* 💃💃💃💃💃💃

*~#TEAM KHUBRA-KHALEED.~*

*_®єαl $mαѕhєr._* 😉
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/

*©®2018*
*3/ɑմցմՏԵ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

5⃣8⃣

*K* o bayan da suka fito daga wankan tsokanarta yayi tayi,burinsa bai wuce ta dad'a sakin jiki da shi sosai ,suyi rayuwa mai cike da tsafta da k'aunar juna cikin ko wane hali zasu kasance,duk yadda ta sanar da shi irin son da take masa tunma kafin wannan lokacin,amma kuma yana da burin jin labarin yadda ta rayu da soyayyarsa a lokacin da basu tab'a tozali da junan suba,cikin dabara ya shiryata sannan ya shirya kansa,kamar jaririya haka ta zame masa shi kuma duk abunda take yi ko kad'an bai ganin laifinta bare ya damu hasalima burgeshi take.
Parlour suka fito tana jikinsa a lafe kamar mage,dama KHUBRA ba baya bace gurin son jiki yanzun kuma ta samu shi yasa ta dad'a manne masa,cikin kunnenta yake rad'a mata
"Baby baki bani labarin yadda kika rayu da soyayyana ba kamar yadda kika fad'a.."
Idanunta a rufe tana kwance kan chest ensa,tana ta faman zuba murmushi,abunda ya fad'a yasa ta sake duk'unk'unewa a jikinsa tana fad'in
"Nima ai baka fad'amin labarin soyayyana ba.."
Murmushi yayi mai sauti sannan ya d'ago fuskarta
"Kina son ji ne...?"
Kai ta d'aga masa,cikin zolaya yace
"Oyyahhh! idan kina son na baki labari sai kin kalleni tukun kuma yanzun.."
Dad'a sinne kai tayi a jikinsa tana fad'in
"Tabbb! wollahi a'a ban iyawa.."
"Shi kenan to tunda bakya son labarin sai a hak'ura"
Da sauri ta katse shi tana fad'in
"A'a a'a ni ka bani a haka,so kake kasa nayi ta jin kunyarka kenanma ko...?"

"A'a ta yaya zan saki jin kunya,ni da nake sonma ki dena jin kunyana gaba d'aya.."

"Ehhh! ammafa cewa kayi saina wani kalleka sannan zaka fad'amin.."
Chapter 69 · 0% Book details