Sashe 51
Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hawaye ne suka shiga tsere akan fuskarta babu k'ak'k'autawa murya na rawa ta bud'e baki za tayi magana,da sauri ya d'aga mata hannu alaman bai son tace komai,daga haka ya juya tare da bin corridor,jikinta a sanyaye ta goge fuskarta sannan ta kalli BB dake tsaye yana murmushi,ta cikin idanunsa kana iya hango kyallin hawaye da yaketa k'ok'arin dannewa dan ganin baiyi kuka'nba.
Murmushi tayi masa itama lokacin da wasu hawayen suka sake biyo baya,da sauri tabi bayan ABBA daya riga ya shige,a bed room enta ta tarar da shi har lokacin yana tsaye bai zaunaba,k'arasowa tayi kanta a k'asa ta sark'e hannayenta,cikin wani irin murya mai cike da nadama da dana sanin abunda ta aikata a baya ta nufi inda yake,kan gwiwoyinta ta zube hannuna rik'e da k'afarsa,hawaye sai ambaliya suke a fuskar MAMA cikin kuka take fad'in
"Ka gafartamin abunda nayi maka tsayin wad'annan shekaru,duk da nasan ni mai laifi ce wanda bata cancanci hakan daga gare kaba,amma ba zan gusheba ina neman yafiyarka saboda abunda na aikata maka....Na yarda wallahi ko da mata uku zaka kawo bayana....bazan ce maka a'a ba,na amince...duk duniya bani da burin da ya wuce kace ka yafemin...."
Kukane yaci k'arfinta daya sata dole tayi shiru tana shashshek'ar kuka,hannu ya mik'a ya d'agota sai da ya goge mata fuskanta tukun yayi murmushi
"Indai har dan wannan ne to kisa a ranki na riga da na jima da yafe miki,fatan ubangiji ya yafe mana baki d'aya,nima kuma ina neman afuwarku na tafiya da nayi na barku tsayin wad'annan shekaru,na yanke hukunci cikin fushi..."
Murmushin tayi tana kallonsa sannan a hankali ta furta
"Duk laifi nane dana biyewa zuga da rud'in zamani,badan na biyewa son zuciyaba da duk haka bai faruba...."
"K'warai kuwa amma tunda yanzun kin gane laifinki komai ai ya wuce....ba kuma nason ki sake taso da wannan maganmaganara kinji ko....?"
'Dan mirmushi tayi hanunta akan fuskarsa take fad'in
"Har yanzun kana nan kamar yadda kake.....Zuciyarka mai kyauce da ba kowane ke da irinta ba,na godewa Allah daya bani miji irinka mai saurin yafiya da kuma tausayi,sannan kuma na godema mijina daya yafe min laifin da na aikata masa baka rik'e niba....."
Wasu hawayen ne suka kuma gangarowa,da sauri ya girgiza mata kai fuskarsa kuma ya d'an had'eta alama'n baya so.
Hannu tasa tayi saurin gogewa tana k'irk'irar murmushi
"Ina yarana suke sam banji alamunsu ba"
"Ka huta tukun kafin nan sai na kirawo maka su......"
"A'a bana son jin wannan magana sam...yanzun nake son ganin sanyin idaniyata maza a kiramin su,yanzun zan fito mu gana dasu"
Murmushi tayi
"An gama ranka shi dad'e..."
Tana fad'in haka tayi hanyan fita daga d'akin kuma tana waiwayensa.....
《《》》
Da sauri UMMI ta fito daga bedroom tana kiran KHUBRA da ZUHRA,Fitowa sukayi daga kitchen suna amsawa.
"Yawwa y'an albarka maza kuyi sauri ku shirya mana breakfast UNCLE yana hanya,yanzun ya kirani yake fad'amin ya kusa k'arasowa gida....UNCLE yayi mana zuwan bazata wollahi..."
"UMMI ai har mun jima da kammalawa ma"
Kallonsu tayi tana murmushi
"Da kyau y'an matana Allah yayi muku albarka"
Amsawa sukayi da ameen,kafun su juya wani kiran ya dad'a shigowa wayan dake hannunta,kallon wayan tayi da sauri kuma ta d'aga ganin MAMA ce,kafin tayi magana har ta rigata ko gaisawa ba suyiba ta ji MAMA'N tana fad'in
"UMMI'N YARA dan Allah ki turomin su ZUHRA yanzun KHALEEL ya kawosu...."
"To Allah dai yasa lafiya kike nemansu da wannan farar safiyar"
"Lafiya k'alau wallahi....ai da labari amma sai mun had'u...."
Yanda tayi magana ya tabbatar mata da abunda ta fad'a wani abune na farin ciki yake shirin faruwa koma ya faru.
"To Allah ya sadamu da alkhairi..."
Da sauri MAMA ta amsa da ameen tana y'ar dariya,ita dai UMMI sai mamaki take kome ya faru haka MAMA take neman yaran da wannan safiyar ohoooo,sai dai sun had'un kamar yadda ta fad'a taji koma mene...
"Kuna ina kuma.....?"
Da sauri suka lek'o daga kitchen
"Yawwa tunda kun gama maza kuzo ku shirya zaku je gidan MAMA..."
Tsalle sukayi suka rik'e juna kamar wad'anda suka jima basu jeba..
"Bari na tashi YAYA'NKU sai ya kaiku...saura idan kun shiga d'aki kada kuyi sauri ku fito kunji....kun dai san halinsa..."
Tsere suka shiga yi suna dariya,itama UMMI murmushi tayi tana binsu da kallon sha'awa..
*SOME HOUR'S LEFT.*
Suka shigo cikin parlor'n mutanen gidan gaba d'aya suna parlor,abun mamaki kamar ana wani taro na musamman,shigowa suka yi suna kalle-kalle sannan suka gaida MAMA dake zaune kusa da ABBA ta sha ado,idan ba wanda yasan MAMA ba a wannan lokacin babu tabbas ya ganeta saboda yanda ta koma kamar wata basarakiya..
Fuskarta cike da annuri take kallonsu
Kusa da ASHNA suka zauna cikin rad'a ZUHRA tace
"ASHNA bak'o mukayi ne kuma yau?"
Tana dariya tace
"Ke dillah ABBA ne ya dawofa baki gane shiba ne?"
Ido ta zaro tana fad'in
"ABBA fa kikace....dan Allah da gaske ko wasa?"
Hararar wasa tayi mata sannan ta dad'a sunkuyowa a hankali ta furta
"Banda abunki idan ba ABBA bane to wane zai zauna kusa da MAMA haka wanda ba muharraminta ba...."
"Ehhh to kumafa hakane...."
Bakinta a bud'e ta d'ago
"ABBA barka da dawowa"
Gaba d'aya parlor'n aka sa mata dariya,kallonsu tayi d'aya bayan d'aya tana sunk'e kai jikin KHUBRA dake mata dariya itama
"Sai da kika tambaya sannan kika gane ni kenan"
Dariya tayi bata iya yin maganaba,hannu ya bud'e mata a hankali kuwa ta mik'e ta nufi gurinsa,alama yayiwa KHUBRA da tazo saboda MAMA tayi masa bayaninta tun kafin ya ganta,sai dai kuma ganinta yasa shi jin wani abu game da itan,rungumesu yayi gaba d'aya ko sukayi luf a jikinsa dama ZUHRA ma ba bayaba ce gurin son jiki da ita da KHUBRA shi yasa amintar tasu tazo d'aya..
Nan a parlor suka shiririce ranar idan kaga sun motsa daga gurin to sallah zasuyi sai ko cin abinci abunda ke tashinsu kenan.
Wajejen bayan salla'n Asr motan su KHALEEL ta dad'a kunno kai,dan dama daya kawo su bai shigaba ya koma gida,sai yanzun da ABBA'NSA yasa shi kawosu shi da UMMI...
Anyi gaishe-gaishe UNCLE na shirin yin magana ABBA ya dakatar dashi ta hanyar yi masa inkiya..
Hira sosai ta yaushe rabo ake tsakaninsu duk wanda ya kallesu sai sun bashi sha'awa ganin yadda family biyu suka had'e kamar guda d'aya.
Sai dare suka shirya komawa gida,ZUHRA da KHUBRA na shirin bin UMMI ta daka tar dasu,gefe ta jasu saboda tana son yin magana da su
"Kunga yau ABBA ya dawo ko? to abunda nake so da ku,ku zauna kuyi masa wannan girke-girken naku shima kunji ko?....idan ya so bayan kun gama yi masa barka da dawowa da kaina zan dawo na d'aukeku kunji ko y'an albarka..."
Cike da murna ko dan dama kawai sunyi hakan ne dan kada ace sunyi ba dai-daba,sallama suka mata sannan suka juya..
UNCLE rik'e da hannun ABBA suma suna gefe UNCLE en ya furta
"Bansan dalilin da yasa kak'i yarda ayi maganar abunda ya faru ba.....ko mene ne ma'anar hanawan da kayi?"
"Uhmmm!kasan shi sha'ani irin wannan ba a buk'atar tado shi,sannan ba a buk'atar yaro ya sanshi saboda zai jima yana kallonka a matsayin mai laifi....Bayan hakama bana son yin abunda yarana zasu tsaneni.."
Jinjina kai UNCLE yayi sannan sukayi musabiha tare da sallama da juna suka d'auki hanyan komawa gida suna d'agama juna hannu cike da farin ciki mara misaltuwa...
Tun daga ranar da ABBA ya dawo su KHUBRA ke aikin dafawa da saukewa har tsayin kwanaki bakwai,a ranar ne kuma suke sa ran zuwan UMMI don komawa gida,sosai ABBA ke jinjina musu namijin k'ok'arin da suke,sboda duk girkin da za ayi a gidan idan ya tambaya amsar bata wuce ta kullum wato *KHUBRA da *ZURA* ,idan ko akace ABBA na zaune a parlor haka zasu kewayeshi kowa na bashi labari har rasa na wa zai saurara yake saboda hayaniyansu bata bari yaji labaran nasu,su kuma bazasu bari wani ya bada nashi sannan wanima yayiba,a'a sai dai suce duka zai saurara....
《《》》
A b'angarensu KHALEEL kuwa tun da ABBA'NSA ya dawo bashi da wani abokin hira ko shawara daya wuce ABBA'NSA.
Zuwa yanzun ABBA'N yasan da maganar KHALEEL,yanzun hakama maganar tafiya neman aurenta ake wanda ABBA ya sanar da ABBA'NSU BB zuwansu,da suka gama yanke shawaran zuwa nemo aurenta gurin mahaifinta...
Koda ABBA yasa MAMA ta tambayi KHUBRA yadda zasu samu ganin mahaifinta kuka tasa mata,sai da MAMA tayi aikin lallashi da taimakon ZUHRA da kuma banbaki sannan tayi shiru.
"Ni bansan me zanceba akan haka...."
Abunda ya fito daga bakin KHUBRA kenan fuskarta a had'e
Kallonta kawai ZUHRA tayi
"To banda abunki SISTER sumafa iyaye suna da hakki akanki ko dan sanin inda kike rayuwa da sanin matsayin rayuwarki....yanzun duk son da kikewa ABBA zaki so barinsa?ko kuwa zaki so barinsa cikin mawuyacin hali?
Yanzu baza kiso ganin saba da sanin yana raye ko kuwa akasin haka ba?"
A tsorace ta kalli ZUHRA dake magana,ita kuma ganin yanayinta yasa tace
"Ehhhh!ko kina so ace haka ya faru da ABBA'N?....."
Kaita girgiza da sauri hawaye yana sakkowa kan fuskarta jin ta ambaci mutuwa
"Nooo!bafa kuka za kiyiba....idan har kina son ganinsa to kiyi k'ok'arin bada address na gidanku kinji sister'na"
Cikin sheshshek'ar kuka ta fara magana
"Bazan iya bada kwatance ba....."
Zaro ido ZUHRA tayi MAMA kuma tana gefe tana jinsu tak'i magana
"To sai me kenan?"
"Zan iya gane gidan da kaina amma bazan iya bada kwatance ba"
Sai lokacin suka gane abunda take nufi,aiko cike da jin dad'i ZUHRA ta furata
"MAMA idan zasu tafi nima zan bisu...Kinji?"
Dan tasan abunda ABBA zai ce kenan wato a tafi da KHUBRA..
Nan ko ASHNA ma tace
"Nima haka MAMA....."
FATAHIYYA ta kallesu
"Nima kinji MAMA zani..."
Dariya MAMA tayi
"To shi kenan...kuje ku fad'awa ABBA idan ya amince sai ku bisu......"
Kafin ta rufe baki har FATAHIYYA ta fice dan tambayan ABBA....
*********
Murmushi tayi masa itama lokacin da wasu hawayen suka sake biyo baya,da sauri tabi bayan ABBA daya riga ya shige,a bed room enta ta tarar da shi har lokacin yana tsaye bai zaunaba,k'arasowa tayi kanta a k'asa ta sark'e hannayenta,cikin wani irin murya mai cike da nadama da dana sanin abunda ta aikata a baya ta nufi inda yake,kan gwiwoyinta ta zube hannuna rik'e da k'afarsa,hawaye sai ambaliya suke a fuskar MAMA cikin kuka take fad'in
"Ka gafartamin abunda nayi maka tsayin wad'annan shekaru,duk da nasan ni mai laifi ce wanda bata cancanci hakan daga gare kaba,amma ba zan gusheba ina neman yafiyarka saboda abunda na aikata maka....Na yarda wallahi ko da mata uku zaka kawo bayana....bazan ce maka a'a ba,na amince...duk duniya bani da burin da ya wuce kace ka yafemin...."
Kukane yaci k'arfinta daya sata dole tayi shiru tana shashshek'ar kuka,hannu ya mik'a ya d'agota sai da ya goge mata fuskanta tukun yayi murmushi
"Indai har dan wannan ne to kisa a ranki na riga da na jima da yafe miki,fatan ubangiji ya yafe mana baki d'aya,nima kuma ina neman afuwarku na tafiya da nayi na barku tsayin wad'annan shekaru,na yanke hukunci cikin fushi..."
Murmushin tayi tana kallonsa sannan a hankali ta furta
"Duk laifi nane dana biyewa zuga da rud'in zamani,badan na biyewa son zuciyaba da duk haka bai faruba...."
"K'warai kuwa amma tunda yanzun kin gane laifinki komai ai ya wuce....ba kuma nason ki sake taso da wannan maganmaganara kinji ko....?"
'Dan mirmushi tayi hanunta akan fuskarsa take fad'in
"Har yanzun kana nan kamar yadda kake.....Zuciyarka mai kyauce da ba kowane ke da irinta ba,na godewa Allah daya bani miji irinka mai saurin yafiya da kuma tausayi,sannan kuma na godema mijina daya yafe min laifin da na aikata masa baka rik'e niba....."
Wasu hawayen ne suka kuma gangarowa,da sauri ya girgiza mata kai fuskarsa kuma ya d'an had'eta alama'n baya so.
Hannu tasa tayi saurin gogewa tana k'irk'irar murmushi
"Ina yarana suke sam banji alamunsu ba"
"Ka huta tukun kafin nan sai na kirawo maka su......"
"A'a bana son jin wannan magana sam...yanzun nake son ganin sanyin idaniyata maza a kiramin su,yanzun zan fito mu gana dasu"
Murmushi tayi
"An gama ranka shi dad'e..."
Tana fad'in haka tayi hanyan fita daga d'akin kuma tana waiwayensa.....
《《》》
Da sauri UMMI ta fito daga bedroom tana kiran KHUBRA da ZUHRA,Fitowa sukayi daga kitchen suna amsawa.
"Yawwa y'an albarka maza kuyi sauri ku shirya mana breakfast UNCLE yana hanya,yanzun ya kirani yake fad'amin ya kusa k'arasowa gida....UNCLE yayi mana zuwan bazata wollahi..."
"UMMI ai har mun jima da kammalawa ma"
Kallonsu tayi tana murmushi
"Da kyau y'an matana Allah yayi muku albarka"
Amsawa sukayi da ameen,kafun su juya wani kiran ya dad'a shigowa wayan dake hannunta,kallon wayan tayi da sauri kuma ta d'aga ganin MAMA ce,kafin tayi magana har ta rigata ko gaisawa ba suyiba ta ji MAMA'N tana fad'in
"UMMI'N YARA dan Allah ki turomin su ZUHRA yanzun KHALEEL ya kawosu...."
"To Allah dai yasa lafiya kike nemansu da wannan farar safiyar"
"Lafiya k'alau wallahi....ai da labari amma sai mun had'u...."
Yanda tayi magana ya tabbatar mata da abunda ta fad'a wani abune na farin ciki yake shirin faruwa koma ya faru.
"To Allah ya sadamu da alkhairi..."
Da sauri MAMA ta amsa da ameen tana y'ar dariya,ita dai UMMI sai mamaki take kome ya faru haka MAMA take neman yaran da wannan safiyar ohoooo,sai dai sun had'un kamar yadda ta fad'a taji koma mene...
"Kuna ina kuma.....?"
Da sauri suka lek'o daga kitchen
"Yawwa tunda kun gama maza kuzo ku shirya zaku je gidan MAMA..."
Tsalle sukayi suka rik'e juna kamar wad'anda suka jima basu jeba..
"Bari na tashi YAYA'NKU sai ya kaiku...saura idan kun shiga d'aki kada kuyi sauri ku fito kunji....kun dai san halinsa..."
Tsere suka shiga yi suna dariya,itama UMMI murmushi tayi tana binsu da kallon sha'awa..
*SOME HOUR'S LEFT.*
Suka shigo cikin parlor'n mutanen gidan gaba d'aya suna parlor,abun mamaki kamar ana wani taro na musamman,shigowa suka yi suna kalle-kalle sannan suka gaida MAMA dake zaune kusa da ABBA ta sha ado,idan ba wanda yasan MAMA ba a wannan lokacin babu tabbas ya ganeta saboda yanda ta koma kamar wata basarakiya..
Fuskarta cike da annuri take kallonsu
Kusa da ASHNA suka zauna cikin rad'a ZUHRA tace
"ASHNA bak'o mukayi ne kuma yau?"
Tana dariya tace
"Ke dillah ABBA ne ya dawofa baki gane shiba ne?"
Ido ta zaro tana fad'in
"ABBA fa kikace....dan Allah da gaske ko wasa?"
Hararar wasa tayi mata sannan ta dad'a sunkuyowa a hankali ta furta
"Banda abunki idan ba ABBA bane to wane zai zauna kusa da MAMA haka wanda ba muharraminta ba...."
"Ehhh to kumafa hakane...."
Bakinta a bud'e ta d'ago
"ABBA barka da dawowa"
Gaba d'aya parlor'n aka sa mata dariya,kallonsu tayi d'aya bayan d'aya tana sunk'e kai jikin KHUBRA dake mata dariya itama
"Sai da kika tambaya sannan kika gane ni kenan"
Dariya tayi bata iya yin maganaba,hannu ya bud'e mata a hankali kuwa ta mik'e ta nufi gurinsa,alama yayiwa KHUBRA da tazo saboda MAMA tayi masa bayaninta tun kafin ya ganta,sai dai kuma ganinta yasa shi jin wani abu game da itan,rungumesu yayi gaba d'aya ko sukayi luf a jikinsa dama ZUHRA ma ba bayaba ce gurin son jiki da ita da KHUBRA shi yasa amintar tasu tazo d'aya..
Nan a parlor suka shiririce ranar idan kaga sun motsa daga gurin to sallah zasuyi sai ko cin abinci abunda ke tashinsu kenan.
Wajejen bayan salla'n Asr motan su KHALEEL ta dad'a kunno kai,dan dama daya kawo su bai shigaba ya koma gida,sai yanzun da ABBA'NSA yasa shi kawosu shi da UMMI...
Anyi gaishe-gaishe UNCLE na shirin yin magana ABBA ya dakatar dashi ta hanyar yi masa inkiya..
Hira sosai ta yaushe rabo ake tsakaninsu duk wanda ya kallesu sai sun bashi sha'awa ganin yadda family biyu suka had'e kamar guda d'aya.
Sai dare suka shirya komawa gida,ZUHRA da KHUBRA na shirin bin UMMI ta daka tar dasu,gefe ta jasu saboda tana son yin magana da su
"Kunga yau ABBA ya dawo ko? to abunda nake so da ku,ku zauna kuyi masa wannan girke-girken naku shima kunji ko?....idan ya so bayan kun gama yi masa barka da dawowa da kaina zan dawo na d'aukeku kunji ko y'an albarka..."
Cike da murna ko dan dama kawai sunyi hakan ne dan kada ace sunyi ba dai-daba,sallama suka mata sannan suka juya..
UNCLE rik'e da hannun ABBA suma suna gefe UNCLE en ya furta
"Bansan dalilin da yasa kak'i yarda ayi maganar abunda ya faru ba.....ko mene ne ma'anar hanawan da kayi?"
"Uhmmm!kasan shi sha'ani irin wannan ba a buk'atar tado shi,sannan ba a buk'atar yaro ya sanshi saboda zai jima yana kallonka a matsayin mai laifi....Bayan hakama bana son yin abunda yarana zasu tsaneni.."
Jinjina kai UNCLE yayi sannan sukayi musabiha tare da sallama da juna suka d'auki hanyan komawa gida suna d'agama juna hannu cike da farin ciki mara misaltuwa...
Tun daga ranar da ABBA ya dawo su KHUBRA ke aikin dafawa da saukewa har tsayin kwanaki bakwai,a ranar ne kuma suke sa ran zuwan UMMI don komawa gida,sosai ABBA ke jinjina musu namijin k'ok'arin da suke,sboda duk girkin da za ayi a gidan idan ya tambaya amsar bata wuce ta kullum wato *KHUBRA da *ZURA* ,idan ko akace ABBA na zaune a parlor haka zasu kewayeshi kowa na bashi labari har rasa na wa zai saurara yake saboda hayaniyansu bata bari yaji labaran nasu,su kuma bazasu bari wani ya bada nashi sannan wanima yayiba,a'a sai dai suce duka zai saurara....
《《》》
A b'angarensu KHALEEL kuwa tun da ABBA'NSA ya dawo bashi da wani abokin hira ko shawara daya wuce ABBA'NSA.
Zuwa yanzun ABBA'N yasan da maganar KHALEEL,yanzun hakama maganar tafiya neman aurenta ake wanda ABBA ya sanar da ABBA'NSU BB zuwansu,da suka gama yanke shawaran zuwa nemo aurenta gurin mahaifinta...
Koda ABBA yasa MAMA ta tambayi KHUBRA yadda zasu samu ganin mahaifinta kuka tasa mata,sai da MAMA tayi aikin lallashi da taimakon ZUHRA da kuma banbaki sannan tayi shiru.
"Ni bansan me zanceba akan haka...."
Abunda ya fito daga bakin KHUBRA kenan fuskarta a had'e
Kallonta kawai ZUHRA tayi
"To banda abunki SISTER sumafa iyaye suna da hakki akanki ko dan sanin inda kike rayuwa da sanin matsayin rayuwarki....yanzun duk son da kikewa ABBA zaki so barinsa?ko kuwa zaki so barinsa cikin mawuyacin hali?
Yanzu baza kiso ganin saba da sanin yana raye ko kuwa akasin haka ba?"
A tsorace ta kalli ZUHRA dake magana,ita kuma ganin yanayinta yasa tace
"Ehhhh!ko kina so ace haka ya faru da ABBA'N?....."
Kaita girgiza da sauri hawaye yana sakkowa kan fuskarta jin ta ambaci mutuwa
"Nooo!bafa kuka za kiyiba....idan har kina son ganinsa to kiyi k'ok'arin bada address na gidanku kinji sister'na"
Cikin sheshshek'ar kuka ta fara magana
"Bazan iya bada kwatance ba....."
Zaro ido ZUHRA tayi MAMA kuma tana gefe tana jinsu tak'i magana
"To sai me kenan?"
"Zan iya gane gidan da kaina amma bazan iya bada kwatance ba"
Sai lokacin suka gane abunda take nufi,aiko cike da jin dad'i ZUHRA ta furata
"MAMA idan zasu tafi nima zan bisu...Kinji?"
Dan tasan abunda ABBA zai ce kenan wato a tafi da KHUBRA..
Nan ko ASHNA ma tace
"Nima haka MAMA....."
FATAHIYYA ta kallesu
"Nima kinji MAMA zani..."
Dariya MAMA tayi
"To shi kenan...kuje ku fad'awa ABBA idan ya amince sai ku bisu......"
Kafin ta rufe baki har FATAHIYYA ta fice dan tambayan ABBA....
*********