← Book details Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 86

Sashe 53

Yar Garuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Shigowarta office en ta tarar da shi yana waya kan dole ta tsaya jiransa har ya gama,sannan ya amshi takardar dake hannunta,zaro farar takardar yayi da take ninke a cikin envelope ya warware,abunda idanunsa suka fara tozali da shi shine yanda gwajin jininta ya koma *POSITIVE* maimakon *NEGATIVE* wannan shi ne abunda ya tabbatar masa da matar na d'auke da cutar da yake hasashe,ajiyan zuciya yayi sannan ya maida takardar ma'adaninta,cikin sanyin murya ya shiga yi mata nasiha kan yarda da *K'ADDARA* da kuma karb'arta ta kowane fuska tazo maka mai kyau ne ko akasin haka,ita dai MA'U ido ne nata babu baki,sam ta kasa gane inda wannan tatsuniya ta likita ke tafiya duk ta kafeshi da idanu
"Likita nifa har yanzun ban gane ma'anar wannan wa'azin nakaba ,kawai idan zaka sanarmin abunda ke faruwa to,idan kuma bazaka fad'a ba to ka sallameni dan na gaji da zaman gurin nan"

Kallonta kawai yayi jin yadda take magana cikin kaushin murya a ransa ya furta
"Lallai wato bata san meke faruwa ba amma takemin irin wannan maganar....aiko zaki san ni kikewa magana haka"
Yayi niyyan sanar da ita cikin ruwan sanyi amma maganarta tasa shi had'e giran sama dana k'asa ya shiga fad'in
"HAJIYA sakamakon gwajin da aka miki ya tabbatar mana da kina d'auke da cuta me karya garkuwa'n jiki wato *HIV* kenan kamar yadda muke kiranta a turance,wanda a hausa kuma muke kiranta da *K'ANJAMAUU*......."

《《》》

Hannunsa d'auke da envelope yana tafiya yana kare fuskarsa saboda zafin rana dake damunsa,ci gaba da kallon hanya yake saboda hangen abun hawa da zai d'auke shi a lokacin,da k'yar ya samu NAPEP ya fad'a masa inda zashi,tafiyar mintuna k'alilan ta kawosu bakin k'aton get en,kud'i ya fiddo ya sallami mai NAPEP en sannan ya tura get en ya shiga.
Tun daga harabar gidan nake kallon gurin kamar na sanshi haka wani lokaci daya gabata,cikin sauri ya shige k'ofar da zata sadashi da babban parlor na k'asa,shigowarsa ya tarar dasu sun baje kayan shaye-shaye wasu da kwalabe wasu kuma sai had'awa sama hazo suke.
"Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un!!"
Abunda ya fara fitowa daga bakinsa kenan,cikin fushi ya isa gurin baiyi wata-wataba ya shiga fashe kwalaben a k'asa cikin fad'a yake fad'in
"Ban fad'a muku kada wanda ya sake yimin shaye-shaye a gida ba?.....ko kuwa so kuke ayimin cunen y'an drugs?
To wallahi yau kam kunyi na k'arshe dan dukanku sai kun barmin gida...gara kusan inda dare yayi muku,nima na samu Hutu da nutsuwar zuciya.."

"SO.....SO...SORRY OGAAA...."
Wani yaronsa daya sha yayi mankas ya fad'a idanunsa na rufewa da bud'ewa
"In...sh...sh...sha....Allahu ba zaka sake kamamu da wannan laifinba.."
Tsaki yayi ya wuce hanyan stairs a ransa yake fad'in
"Ya zama dole akaina ko dai ku chanja hali ko kuma dukanku dole na rabu daku"
Kafin ya k'arasa haurawa saman wayansa dake aljihu ta soma k'ara da sauri ko ya zarota ganin bak'uwar number har zai fasa d'auka wata zuciyar tace
"Ina kai ina k'in d'aukan bak'uwar number,ai kawai ka d'auka wata kila ko cikin guraren da ka kai takardunkane aka dace ka samu aikin da kake nema...."
Bai ka'arasa tunaninba yayi saurin d'auka had'eda karata a kunne,cikin harshen nasara daga gefen da aka kira shi ake fad'in
"Ko kaine SADEEQ MUHAMMAD?"
Cikin hanzari har yana had'awa da girgiza kai BIGGY ya amsa da eh shi ne..

"Muna nemanka ranar monday a ma'aikatar revenue ta nan kano a branch enmu dake bomphai..."

Ai BIGGY kam ji yayi kamar zai gangaro daga saman stairs en saboda dacen da yayi bak'aramin dad'i yajiba,dan dama ranar da UMMI tace ya kai mata takardunsa ya amsane kawai amma a ransa ya k'udurce shifa ba zai koma gidanba har sai bayan ya samu aiki wanda yayi k'ok'arin hakan a k'ashin kansa,wannan shi kad'ai zai sa su ganshi da k'ima..
Godiya yayiwa Allah,sannan ya kuma tabbatarwa da kansa lallai duk wanda yake laifi ya tuba ubangiji yana karb'an tubansa,kansa ya d'aga sama hawayen farin ciki suna sakko masa a hankali ya furta
"Lallai ne ubangiji shi kad'ai yafi cancanta da a bautawa...Allah na gode maka da ka nufeni da tuba tun lokaci bai k'ureminba..."

*~#TEAM KHUBRA.*~

*_#REAL SMASHER._*
💠💠💠💠💠

*Y'AR GARUWA......*
*(ɬɧɛ mơʂɬ ɧɛąrɬ ɬơųcɧıŋɠ ʂɬơrყ).*

🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹

*©®2018*
*22/ʝųlყ,2018*

*ʂɬơrყ ąŋɖ wrıɬɛɛŋ*
*ცყ*
_HAWWA M.U {$мaѕнer}_
🕊🕊🕊🕊🕊
🌹🌹🌹🌹

_BISMILLAHIR-RAHMANIR-RAHEEM..._
*~________________________~*

*DEVOTED TO:*
_BILKISU M.ADAM (Y'AR ABBA)_

*BESTOWED TO:*
_MURJA SALIS (NA'IKKE)._

*AND*

_FATIMA ABUBAKAR (FATEEY AFIRST)._

*4⃣9⃣*

*"A* lak'ar data had'amu da SAFWAN itace auratayya inda na auri k'anwarsa mai suna FALMATA"
A nan ABBA'N KHUBRA ya dakata saboda wani tunanin daya bijiro masa wanda sam baiji dad'in hakanba,sai yanzu yake nadama da dana sanin abunda ya aikata,ciki kuwa harda saurin yanke hukunci,wanda Annabi (S.A.W) ya hanemu da mu yanke hukunci cikin fushi.
LADIYO ya kalla da rinannun idanunsa da babu komai cikinsu face zallar b'acin rai wanda kana kallonsa zaka tabbatar had'e kuma da gano abunda ke k'unshe k'asan zuciyarsa.
Muryarsa a shak'e ya kalli mutanen gurin ya kuma kallon LADIYO data sha jinin jikinta,sai da yayi gyaran murya sannan ya fara da fad'in
"Da farko dai zan fara da yiwa wannan matsiyaciyar matar Allah ya isa,sannan kuma in shaida muku ina son ku zama shaida ni ABUBAKAR SA'ADU (MALAM BUBA) na saki LADIYO saki uku babu ni babu ita,daga yau ina son ta tattara kayanta tabarmun gidana na sallameta......"

Innalillahi wa-inna ilaihi raji'un...
Abunda mutanen gurin keta maimaitawa kenan kamar sa ari baki,ABBA'N KHALEEL ne ya fara magana
"Haba MALAM ya zaka yanke irin wannan hukunci haka,bayan ka sani cewa ubangiji da kansa yana k'yamar saki irin wannan,sam bai dace kayi hukunci irin wannan ba koda kuwa wane irin laifi ta aikata maka,idan ka kyaleta da mahaliccinmu zai hukuntata komai girman laifinta kuwa..."
Bai kai k'arsheba MALAMA BUBA ya dakatar da shi ta hanyar fad'in
"Haba ALHAJI yanzu ita wannan matar da kake magana akanta kasan girman laifukanta kuwa?ko kuwa ni kasan meta aikatamin?kasan tsahon loacin data d'auka tana cutata?to ku saurareni yanzun zaku ji irin cutarwa da azabtarwar da wannan munafukar tayimin ni da iyalina...."

*19 YEAR'S BACK......*
Chapter 53 · 0% Book details